
16/09/2025
A daren Litinin, 15 ga Satumba, 2025, an sanya tsohon ministan mak**ashi na Nijar, Ibrahim Yacoubou, da wasu tare da shi a gidan yari, bisa zargin da ake musu da hannu a kisan gilla.
Wannan mataki ya biyo bayan k**a Ibrahim Yacoubou a ranar Juma’a da ta gabata, inda aka tsare shi a Ofishin ‘Yan Sanda na Bincike (Police Judiciaire), kafin a gurfanar da shi gaban kotu jiya Litinin da yamma misalin karfe 7 na dare.
Yacoubou, wanda ya rike mukamin Ministan Harkokin Waje da kuma Ministan Mak**ashi a zamanin gwamnatin Ouhoumoudou Mahamadou da aka kifar a 2023, yana daga cikin mutanen da wani boka da ake zargi da kashe mutane fiye da biyar ya ambata a bincike.
Rahotanni na nuna cewa ana zargin wannan boka da aikata kisan kai ta hanyar al’ada (assassinats rituels), lamarin da ke ci gaba da tayar da kura a babban birnin ƙasar, Niamey.
Ana sa ran cigaban bincike da shari’a zai fito da cikakken bayani kan rawar da kowanne daga cikin wadanda ake zargi ya taka.