Mi Ke Labari Tv

Mi Ke Labari Tv BARKA DA ZUWA WANAN TASHA �

KUNA JIN DADIN � SHIRYE - SHIRYEN MU ? KU DANA MUNA MABALI BULA DOMIN BIBIYAR MU. MUN GODE 💛.

A daren Litinin, 15 ga Satumba, 2025, an sanya tsohon ministan mak**ashi na Nijar, Ibrahim Yacoubou, da wasu tare da shi...
16/09/2025

A daren Litinin, 15 ga Satumba, 2025, an sanya tsohon ministan mak**ashi na Nijar, Ibrahim Yacoubou, da wasu tare da shi a gidan yari, bisa zargin da ake musu da hannu a kisan gilla.

Wannan mataki ya biyo bayan k**a Ibrahim Yacoubou a ranar Juma’a da ta gabata, inda aka tsare shi a Ofishin ‘Yan Sanda na Bincike (Police Judiciaire), kafin a gurfanar da shi gaban kotu jiya Litinin da yamma misalin karfe 7 na dare.

Yacoubou, wanda ya rike mukamin Ministan Harkokin Waje da kuma Ministan Mak**ashi a zamanin gwamnatin Ouhoumoudou Mahamadou da aka kifar a 2023, yana daga cikin mutanen da wani boka da ake zargi da kashe mutane fiye da biyar ya ambata a bincike.

Rahotanni na nuna cewa ana zargin wannan boka da aikata kisan kai ta hanyar al’ada (assassinats rituels), lamarin da ke ci gaba da tayar da kura a babban birnin ƙasar, Niamey.

Ana sa ran cigaban bincike da shari’a zai fito da cikakken bayani kan rawar da kowanne daga cikin wadanda ake zargi ya taka.

Shugaban ƙasar Chadi, Mahamat Idriss Déby, ya bayyana cewa cimma tsaron kai tsaye yanzu shi ne babban fifiko ga ƙasar, b...
12/09/2025

Shugaban ƙasar Chadi, Mahamat Idriss Déby, ya bayyana cewa cimma tsaron kai tsaye yanzu shi ne babban fifiko ga ƙasar, bayan da sojojin Faransa s**a kammala janyewa gaba ɗaya daga ƙasar.

A jiya Alhamis ne Faransa ta kawo ƙarshen kasancewarta ta soja a Chadi, inda ta fitar da sojoji dubu ɗaya (1,000) tare da kayan aikinsu daga babban birnin N’Djamena, kwana guda kafin wa’adin da gwamnati ta saka.

A yayin bikin bankwana da aka gudanar, Shugaba Déby ya bayyana cewa: “Wannan sabon alfijir ne ga Chadi mai cikakken mulkin kai, da ya ƙuduri aniyar ɗaukar nauyin makomarsa da kansa.”

Ya bayyana cewa Chadi ba ta katse dangantaka da Faransa gaba ɗaya ba, sai dai ta dakatar da bangaren soja na haɗin gwiwar kasashen biyu kawai.

Wannan mataki ya biyo bayan raguwar ƙarfin sojojin Faransa a nahiyar Afirka. A cikin ’yan shekarun nan, aka kore su daga Mali, Burkina Faso da Nijar, yayin da Senegal da Ivory Coast suma s**a sanar da shirin fitar da su. Sai dai sojojin Faransa na nan a Djibouti da Gabon.

Shugaba Déby ya jaddada muhimmancin gina sojoji masu ƙarfi da dogaro da kai, waɗanda za su kare ƙasar ba tare da dogaro da waje ba.

Jarumin Kannywood Malam Nata'ala ya fara sabuwar shiga mai dauke da kalar tutar Nijar, bayan ya samu tallafin Naira Mili...
12/09/2025

Jarumin Kannywood Malam Nata'ala ya fara sabuwar shiga mai dauke da kalar tutar Nijar, bayan ya samu tallafin Naira Miliyan 27 daga Shugaban Nijar Abdurraham Tchani, domin kula da lafiyarsa.

NIGER 🇳🇪: Ma’aikatan RTN Za Su Fara Yajin Aiki na Awa 48Ma’aikatan gidan radiyo na Radiodiffusion Télévision du Niger (R...
11/09/2025

NIGER 🇳🇪: Ma’aikatan RTN Za Su Fara Yajin Aiki na Awa 48

Ma’aikatan gidan radiyo na Radiodiffusion Télévision du Niger (RTN) a Jamhuriyar Nijar sun sanar da cewa za su shiga yajin aikin awanni 48 daga ranar Talata, 16 ga Satumba 2025.

Sun bayyana cewa wannan mataki na zuwa ne sak**akon gazawar gwamnati wajen aiwatar da sabon tsarin albashi, da kuma jinkiri wajen biyan albashi akan lokaci, wanda ya jefa su cikin mawuyacin hali na rayuwa.

Kungiyar ma’aikatan ta ce an yi ƙoƙarin tattaunawa da hukumomi, amma rashin daukar mataki ya tilasta su daukar wannan matsaya. Sun kuma bukaci gwamnati da ta gaggauta daukar mataki domin kaucewa dagula harkokin kafar yada labarai ta kasa.

Ana sa ran yajin aikin zai shafi aikace-aikacen gidan radiyo da talabijin a faɗin kasar.

10/09/2025

NIGER 🇳🇪 : KUNGIYOYIN FARAR HULA SUNA BUKATAR A SAKO BAZOUM MOUHAMED❗️

MURNAR ZAGAYOWAR HAIHUWA 🎂Yar Directan tashar Wangari Tv wato Anwar Abdoulaye tana murnar zagayowar haihuwar ta inda aka...
07/09/2025

MURNAR ZAGAYOWAR HAIHUWA 🎂

Yar Directan tashar Wangari Tv wato Anwar Abdoulaye tana murnar zagayowar haihuwar ta inda aka shirya mata liyafa a birnin Niamey 🇳🇪.

« A jiye cikin murna ne muka yi liyafa 2 : ta yarinya ta mai shekara 3 gimbiya ta Aleena Habiba , de na matata. Nayi matukar farincikin wanan rana mai Albarka … » Anwar Abdoulaye ✅

NIGER 🇳🇪 Agadez: Matan Sojoji da Gwamnatin Gundumar Birnin Agadez Sun Kaddamar da Aikin Tsaftace MuhalliA ranar Asabar, ...
06/09/2025

NIGER 🇳🇪 Agadez: Matan Sojoji da Gwamnatin Gundumar Birnin Agadez Sun Kaddamar da Aikin Tsaftace Muhalli

A ranar Asabar, 6 ga Satumba, 2025, Gundumar Birnin Agadez ta kaddamar da wani aikin tsaftace muhalli, wanda matan aure da gwaɓar sojoji (FDS) s**a ɗauki nauyinsa, ƙarƙashin jagorancin matar Gwamnan Agadez, tare da haɗin gwiwar Gundumar Birnin Agadez.

An fara aikin ne daga Asibitin Yankin (CHR) na Agadez, inda matan s**a shara harabar asibitin da kuma tsaftace dakin ajiyar gawa. Daga nan kuma s**a wuce Cibiyar Uwa da Ɗa, inda s**a shara haraba da kuma *tsabtace dakin kula da yara (pédiatrie).

Mai Gudanar da Gundumar Birnin Agadez (Administrateur Délégué) ya nuna godiya ga waɗannan mata bisa jajircewarsu, duk da nauyin da ke kansu, wajen kyautata yanayin lafiya da jin daɗin marasa lafiya da ma'aikatan lafiya.

Ya kuma yabawa matar Gwamna bisa namijin kokarinta da jagoranci, da kuma yadda ta ƙarfafa mata su fito su taka rawar gani a al’umma.

Wakilar matan FDS ta nuna godiyarta ga gundumar bisa goyon baya da tallafin da aka bayar wajen samun nasarar wannan aiki. Ta jaddada cewa sun zabi cibiyoyin lafiya ne saboda su ne wuraren da ke da matuƙar buƙatar tsafta don samar da ingantaccen muhalli ga masu jinya da ma’aikatan lafiya.

Shugabannin cibiyoyin lafiya da aka tsabtace su ma sun bayyana jin daɗinsu da godiya bisa wannan ƙoƙari na haɗin gwiwa, wanda ya inganta lafiyar muhalli a fa'idar jama'a.

~ Mi Ke Labari TV

NIGER 🇳🇪: Majalisar Ministocin Nijar Ta Amince da Kafa Kamfanin "Niger Air International" Don Sauƙaƙa Zirga-Zirga Cikin ...
06/09/2025

NIGER 🇳🇪: Majalisar Ministocin Nijar Ta Amince da Kafa Kamfanin "Niger Air International" Don Sauƙaƙa Zirga-Zirga Cikin Gida da Wajen Ƙasa.

A zaman ta na kwanan nan, Majalisar Ministocin Jamhuriyar Nijar ta amince da kafa sabon kamfanin jiragen sama mai suna "Niger Air International", domin inganta harkar sufuri na cikin gida da kuma ƙetare, da nufin bunƙasa tattalin arzikin ƙasa da sauƙaƙa sadarwa tsakanin jihohi da ƙasashen duniya.

Wannan mataki ya biyo bayan buƙatar da ake da ita na samun kamfani mai zaman kansa amma na ƙasa, wanda zai cike gibin da rashin kamfanin jirgin saman ƙasa ya haifar na tsawon shekaru.

A cewar sanarwar da fadar gwamnati ta fitar:

"Kafa Niger Air International wani muhimmin mataki ne da zai taimaka wajen farfaɗo da harkar sufurin sama, ƙarfafa kasuwanci, yawon buɗe ido da kuma kyautata huldar Nijar da sauran ƙasashen duniya."

Abubuwan da sabon kamfanin zai ƙunsa sun haɗa da:
- Zirga-zirga tsakanin manyan biranen Nijar da jihohin ƙasa.
- Tashi daga Nijar zuwa manyan biranen Afirka da wasu ƙasashen Turai.
- Samar da guraben aikin yi ga matasa da kwararru.
- Ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kan al’umma ta hanyar sauƙaƙe haɗin kai.

Wata majiya daga Ma’aikatar Sufuri ta bayyana cewa an riga an kammala tsare-tsaren kafa hukumar gudanarwa, da shirin sayen jirage, tare da buɗe tattaunawa da wasu kamfanoni daga ƙasashen waje don haɗin gwiwa.

Masana tattalin arziki sun yaba da wannan mataki, suna ganin zai tallafa wajen rage dogaro da kamfanonin waje da kuma farfaɗo da matsayi na Nijar a harkar sufurin sama a yammacin Afirka.

– Rahoton: Mi Ke Labari TV

NIGER 🇳🇪: Kungiyar G25-Niger Ta Nemi A Saki Tsohon Shugaban Ƙasa Mohamed Bazoum, Da Mayar da Mulki Hannun Farar HulaA wa...
06/09/2025

NIGER 🇳🇪: Kungiyar G25-Niger Ta Nemi A Saki Tsohon Shugaban Ƙasa Mohamed Bazoum, Da Mayar da Mulki Hannun Farar Hula

A wani mataki na neman warware rikicin siyasa da ke addabar Jamhuriyar Nijar tun bayan kifar da gwamnati a watan Yuli 2023, Kungiyar G25-Niger ta fito fili da kira ga hukumar mulkin soja da ta saki tsohon shugaban ƙasa Mohamed Bazoum, tare da duk wadanda aka tsare bayan juyin mulkin.

Kungiyar ta bayyana wannan kira a matsayin wani muhimmin mataki na komawa ga zaman lafiya, adalci da daidaito, inda ta yi nuni da cewa, kawo karshen tsare-tsaren siyasa zai buɗe hanyar sulhu da dawowar mulki ga farar hula cikin girmamawa da shari’a.

A cewar sanarwar kungiyar:

“Barin Bazoum da duk wasu da ke tsare ya zama alamar ƙarfin shugabanci, ba rauni ba. Wannan ne zai bai wa duniya damar ganin cewa Nijar na cikin tafarkin warware rikici da gina ƙasa mai ɗorewar demokradiyya.”

Kungiyar G25-Niger wadda ta ƙunshi tsofaffin jami’an gwamnati, ‘yan kasuwa, malaman jami’a da shugabannin al’umma ta ce babban burinta shi ne ganin Nijar ta fita daga halin kunci da rashin tabbas, musamman ta fuskar siyasa, tsaro da tattalin arziki.

~ Mi Ke Labari TV

Adadin kuɗin da Shugaban Nijar ya bani shine CFA Miliyan 10, kwatankwacin Naira miliyan 28,.Na kasa ɓoye alkairin da yai...
05/09/2025

Adadin kuɗin da Shugaban Nijar ya bani shine CFA Miliyan 10, kwatankwacin Naira miliyan 28,.

Na kasa ɓoye alkairin da yai min ni ɗan halak ne dole na fadawa al'umma gaskiyar abinda aka bani.

Wallahi shugaba Tchiani ya karramani ya nuna min ni ɗa ne, Allah ya saka masa da alkair

~ Inji Malam Nata'ala

Daga Salisu Editor,

AC Milan Ta Taya Musulmai Murnar Zagayowar Ranar Haihuwar Annabi Muhammad (SAW)Fitacciyar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Itali...
04/09/2025

AC Milan Ta Taya Musulmai Murnar Zagayowar Ranar Haihuwar Annabi Muhammad (SAW)

Fitacciyar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Italiya, AC Milan, ta taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar 12 ga Rabi’ul-Awwal, wacce ke da matuƙar muhimmanci wajen tunawa da haihuwar fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (SAW).

A cikin saƙon da ƙungiyar ta wallafa a shafinta na sada zumunta (Twitter/X da Instagram), AC Milan ta ce:

"Daga dangin Rossoneri zuwa ga al’ummar Musulmi ♥️🖤
Wishing you all the best on the occasion of 🌙"

Wannan saƙo ya bayyana cikin salo na girmamawa da jinjina ga Musulmai a duniya, yana nuni da yadda ƙungiyar ke ƙara nuna rashin bayyana bambancin addinai da al’adu a tsakanin masoyanta.

Ba wannan ne karo na farko da AC Milan ke taya Musulmai murna a lokutan addini ba. A lokutan Ramadan, Eid-el-Fitr, da Eid-el-Kabir, ƙungiyar kan wallafa saƙonnin taya murna ga Musulmai a duniya baki ɗaya. Wannan mataki na daga cikin hanyoyin da ke ƙarfafa haɗin kai da fahimtar juna a tsakanin al’ummomi daban-daban a duniyar wasanni.

ABIN A YABA: Jarumar Fina Finan Hausa, Asmee Wakili Tayi Sanadiyar Fitowar Wasu Matasa 5 A Gidan Yari, Bayan Ta Biya Mus...
04/09/2025

ABIN A YABA: Jarumar Fina Finan Hausa, Asmee Wakili Tayi Sanadiyar Fitowar Wasu Matasa 5 A Gidan Yari, Bayan Ta Biya Musu Bashin Kudin Da Yayi Sanadiyar Zuwan Su Kurkuku Na Tsawon Lokaci

Ta dauke nauyin yin hakan ne a matsayin ranar murnar bukin zagayowar haihuwarta maimakon kàshe kudin wajen hada taron yañka (cake)

Me zaku ce?

Adres

Brussels

Meldingen

Wees de eerste die het weet en laat ons u een e-mail sturen wanneer Mi Ke Labari Tv nieuws en promoties plaatst. Uw e-mailadres wordt niet voor andere doeleinden gebruikt en u kunt zich op elk gewenst moment afmelden.

Contact

Stuur een bericht naar Mi Ke Labari Tv:

Delen