Mujallar Ajami/Boko عَجَمِيْ اَلْقَلَمِنْ اَرٖيْوَ نَ فَرْكُوْا

Mujallar Ajami/Boko عَجَمِيْ اَلْقَلَمِنْ اَرٖيْوَ نَ فَرْكُوْا Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Mujallar Ajami/Boko عَجَمِيْ اَلْقَلَمِنْ اَرٖيْوَ نَ فَرْكُوْا, Chittagong Division.

SANARWAR MANEMA LABARAI DAGA 'KUNGIYAR 'YAN JARIDA TA 'KASA RESHEN JIHAR  KATSINA (NUJ) KAN RASUWAR TSOHON SHUGABAN 'KAS...
14/07/2025

SANARWAR MANEMA LABARAI DAGA 'KUNGIYAR 'YAN JARIDA TA 'KASA RESHEN JIHAR KATSINA (NUJ) KAN RASUWAR TSOHON SHUGABAN 'KASA (PMB):
*سَنَروَر مَنٜمَ لَابَرَِي دَاغَ قُنغِیَر
عٖین جَرِيدَ تَا قَسَ رٜشٜن جِهَر كَڟِنَ (يٖن.يُو.جي) كَن رَسُووَر ڟُوهُون شُوغَبَن قَسَ (فِي.مٖيم.بِي):*
Kungiyar ‘yan jarida ta 'Kasa reshenJihar Katsina (NUJ)- ta bayyana alhininta da yadda da cewa, kowane rai zai d'and'ani zuk'in mutuwa da kuma mika wuya ga Allah Ta’ala a lokacin da ta samu labarin rasuwar tsohon shugaban k'asar Nijeriya Muhammadu Buhari GCFR.
قُنغِیَر یٖن جَرِيدَ تَا قَسَ رٜشٜنجِهَر كَڟِنَ (يٖن.يُو.جي)- تَا بَییَنَ اَلهِينِنتَ دَ یَددَ دَ ثٜوَ, كُووَنٜ رَِي زَِي طَنطَنِ زُوقِن مُتُوَ دَ كُمَ مِيكَ وُیَ غَ اَللَّه تَعَالَ دَ تَا سَمُ لَابَرِن رَسُووَر ڟُوهُون شُوغَبَن قَسَر نَجٜرِیَ مُحَمَّدُ بُهَارِي جِي.سِي.عٖيف.أَر.
Mun samu kwafin sanarwar ne a jiya 7 ga watan Yulin 2025, mai d'auke da sa hannun shugaban 'Kungiyar Kwamared Tukur Hassan 'Danali.
مُن سَامُ ݣُوفِن سَنَروَر نٜ اَ جِیَ ٧ غَ وَتَن یُولِن ٢٠٢٥, مَي طَوكٜ دَ سَ هَننُن شُوغَبَن قُنغِیَر ݣُومَرٜد تُكُر حَسَن طَن عَلِي.
Sanarwar ta ce, "duk da zamanmu ’yan jarida, ba za mu iya k'ididdige irin jajircewa da sadaukarwar da tsohon Shugaban k'asa ya yi wajen yi wa k'asarmu (Najeriya) hidima ba musamman tun daga shekarar 1975 lokacin da ya fara zama Gwamnan Soja na Jihar Borno.
سَنَروَر تَا ثٜ, "دُك دَ زَمَنمُ يٖين جَرِيدَ, بَ زَا مُ اِیَ قِدِددِغٜ اِرِن جَاجِرثٜوَ دَ سَدَوكَروَر دَ ڟُوهُون شُوغَبَن قَسَ یَایِ وَجٜن یِي وَ قَسَرمُ (نَجٜرِیَ) هِدِمَ بَ مُسَممَن تُن دَاغَ شٜكَرَر ١٩٧٥ لُوكَثِن دَ یَ فَارَ زَمَ ڠُمنَن سُوجَ نَا جِهَر بَرنُو.

Takardar ta k'ara da cewa, "tun daga wancan lokaci sunan Kanar kuma daga baya Janar Muhammadu Buhari ya ci gaba da fitowa a shafuka daban-daban na Jaridun Najeriya da Kafofin yada labarai mabambanta, kuma a kodayaushe ana alakanta su da d'a'a da kwazo da gaskiya a cikin shugabancinsa.
تَكَردَر تَا قَرَ دَ ثٜوَ, "تُن دَاغَ وَنثَن لُوكَثِن سُونَن كَنَر كُمَ دَاغَ بَایَ جَنَر ﷴ بُهَارِ

SANARWAR MANEMA LABARAI DAGA 'KUNGIYAR 'YAN JARIDA TA 'KASA RESHEN JIHAR  KATSINA (NUJ) KAN RASUWAR TSOHON SHUGABAN 'KAS...
14/07/2025

SANARWAR MANEMA LABARAI DAGA 'KUNGIYAR 'YAN JARIDA TA 'KASA RESHEN JIHAR KATSINA (NUJ) KAN RASUWAR TSOHON SHUGABAN 'KASA (PMB):
*سَنَروَر مَنٜمَ لَابَرَِي دَاغَ قُنغِیَر
عٖین جَرِيدَ تَا قَسَ رٜشٜن جِهَر كَڟِنَ (يٖن.يُو.جي) كَن رَسُووَر ڟُوهُون شُوغَبَن قَسَ (فِي.مٖيم.بِي):*
Kungiyar ‘yan jarida ta 'Kasa reshenJihar Katsina (NUJ)- ta bayyana alhininta da yadda da cewa, kowane rai zai d'and'ani zuk'in mutuwa da kuma mika wuya ga Allah Ta’ala a lokacin da ta samu labarin rasuwar tsohon shugaban k'asar Nijeriya Muhammadu Buhari GCFR.
قُنغِیَر یٖن جَرِيدَ تَا قَسَ رٜشٜنجِهَر كَڟِنَ (يٖن.يُو.جي)- تَا بَییَنَ اَلهِينِنتَ دَ یَددَ دَ ثٜوَ, كُووَنٜ رَِي زَِي طَنطَنِ زُوقِن مُتُوَ دَ كُمَ مِيكَ وُیَ غَ اَللَّه تَعَالَ دَ تَا سَمُ لَابَرِن رَسُووَر ڟُوهُون شُوغَبَن قَسَر نَجٜرِیَ مُحَمَّدُ بُهَارِي جِي.سِي.عٖيف.أَر.
Mun samu kwafin sanarwar ne a jiya 7 ga watan Yulin 2025, mai d'auke da sa hannun shugaban 'Kungiyar Kwamared Tukur Hassan 'Danali.
مُن سَامُ ݣُوفِن سَنَروَر نٜ اَ جِیَ ٧ غَ وَتَن یُولِن ٢٠٢٥, مَي طَوكٜ دَ سَ هَننُن شُوغَبَن قُنغِیَر ݣُومَرٜد تُكُر حَسَن طَن عَلِي.
Sanarwar ta ce, "duk da zamanmu ’yan jarida, ba za mu iya k'ididdige irin jajircewa da sadaukarwar da tsohon Shugaban k'asa ya yi wajen yi wa k'asarmu (Najeriya) hidima ba musamman tun daga shekarar 1975 lokacin da ya fara zama Gwamnan Soja na Jihar Borno.
سَنَروَر تَا ثٜ, "دُك دَ زَمَنمُ يٖين جَرِيدَ, بَ زَا مُ اِیَ قِدِددِغٜ اِرِن جَاجِرثٜوَ دَ سَدَوكَروَر دَ ڟُوهُون شُوغَبَن قَسَ یَایِ وَجٜن یِي وَ قَسَرمُ (نَجٜرِیَ) هِدِمَ بَ مُسَممَن تُن دَاغَ شٜكَرَر ١٩٧٥ لُوكَثِن دَ یَ فَارَ زَمَ ڠُمنَن سُوجَ نَا جِهَر بَرنُو.

Takardar ta k'ara da cewa, "tun daga wancan lokaci sunan Kanar kuma daga baya Janar Muhammadu Buhari ya ci gaba da fitowa a shafuka daban-daban na Jaridun Najeriya da Kafofin yada labarai mabambanta, kuma a kodayaushe ana alakanta su da d'a'a da kwazo da gaskiya a cikin shugabancinsa.
تَكَردَر تَا قَرَ دَ ثٜوَ, "تُن دَاغَ وَنثَن لُوكَثِن سُونَن كَنَر كُمَ دَاغَ بَایَ جَنَر ﷴ بُهَارِ یَاثِ غَبَ دَ فِتُووَ اَ شَافُكَ دَبَن-دَبَن نَا جَرِيدُن نَجٜرِیَ دَ كَفَافٖين یَاطَ لَابَرَي مَبَمبَنتَ, كُمَ اَ كُودَیَوشٜ اَنَ اَلَاقَنتَا سُ دَ طَعَ دَ ݣَوزُو دَ غَسكِیَ اَ ثِكِن شُوغَبَنثِسَ.
Hakazalika, sanarwar ta ce, "lallai tarihi zai gafarta wa marigayi Janar Muhammadu Buhari da ya d'auki matakai daban-daban da nufin ganin an fitar da Nijeriya daga k'angin cin hanci da rashawa da sauran d'abi’u marasa nagarta ga wad'anda basu kishin k'asa suke aiwatarwa, musamman lokacin da ya k'arbi ragamar shugabancin k'asa daga ranar 31 ga Disamba, 1983 zuwa Agusta 1985 da kuma lokacin da aka zabe shi ta hanyar dimokradiyya kuma aka rantsar da shi a matsayin shugaban farar hula kuma kwamandan Askarawan Nijeriya daga 2015 zuwa 2023.
هَكَ زَالِكَ سَنَروَر تَاثٖي,"لَلَّي تَارِيهِ زَي غَافَرتَ وَ مَرِغَايِي جَنَر مُحَمَّدُ بُهَارِ دَ يَا طَوكِ مَتَكَي دَبَن - دَبَن دَ نُفِن غَنِن أَن فِتَر دَ نَجٖيرِيَ دَاغَ قَنغِن ثِنهَنثِ دَ رَشَوَ دَ سَورَن طَبِعُ مَرَسَ نَغَرتَ غَ وطَندَ بَاسُ كِيشِن قَسَ سُكٖي أَيوَتَروَ, مُسَممَن لُوكَثِن دَ يَا أَمشِ رَغَمَر شُوغَبَنثِن قَسَ دَاغَ ٣١ غَ دِسَمبَ, ١٩٨٣ زُووَ أَغُستَ ١٩٨٥ دَ كُمَ لُوكَثِن دَ أَكَ زَبٖي شِ تَا هَنيَر دِمُوكَرَطِيَّ كُمَ أَكَ رَنثَر دَ شِ أَ مَثَيِن شُوغَبَن فَرَر هُولَ كُمَ كُومَندَن أَسكَرَاوَن نَاجٖيرِيَ دَاغَ ٢٠١٥ زُووَ ٢٠٢٣.
'Kungiyar (NUJ) wadda ita ce babbar k'ungiyar 'yan jarida da ke a jihar Katsina, tana mika sak'on ta'aziyya ga iyalan jarumin da ya rasu, da Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Ummaru Radd'a PhD, CON da gwamnatin tarayyar Nijeriya bisa wannan rashi da aka yi, tare da addu'ar Allah Ya saka masa da Aljannar Firdausi. Inji sanarwar
قُنغِيَر(يٖين.يُو.جٖي) وَددَ إِتَاثٖي بَببَر قُنغِيَر يٖنجَرِيدَ دَ كٖي أَيكِ أَ جَهَر كَشِنَه٬ تَا مِيقَ سَاقُون تَعَزِييَ غَ إِيَالَن جَارُمِن دَ يَا رَسُ٬ دَ غُمنَن جَهَر كَشِنَه مَالَم دِككُو عُومَر رَططَ فِي.هٖيث.دِي, سِي.أُو.عٖين دَ غُمنَتِن تَرَييَر نَجٖيريَ بِسَ وَننَن رَشِي دَ أَكَ يِي٬ تَارٖي دَ أَدُّعَر أَاللَّه يَا سَاكَ مَسَ دَ أَلجَنَّر فِردَوسِ. إِنجِي سَنَروَو.
Sannan kuma, kungiyar ta shawarci d'aukacin ‘yan jarida na jihar Katsina da su kasance masu kishin k'asa tare da bin ka’idojin aikin jarida wajen bayar da rahoton duk wani abu da ya shafi jana’iza da sauran lamurra a tsawon kwanaki uku ko sama da haka na zaman makoki a Katsina da Daura.
سَننَن كُمَ٬ قُنغِيَر تَا شَوَرثِي طَوكَثِن يٖين جَرِيدَ نَا جَهَر كَشِنَه دَ سُ كَسَنثٖي مَاسُ كِيشِن قَسَ تَارٖي دَ بِن قَاعِدُوجِن أَيكِن جَرِيدَ وَجَن بَايَر دَ رَهُوتُون دُك وَنِ أَبُ دَ يَا شَافِ جَنَاعِزَ دَ سَورَن لَمُررَ أَ ثَوُون كُونَكِي أُككُ كُو سَمَ دَ هَكَ نَا زَمَن مَكُوكِي أَ كَشِنَه دَ دَورَ.
Daga karshe, kungiyar ta yi fatan Allah Ya jikan sa Ya kuma sa ya huta.
دَاغَ قَرشٖي٬ قُنغِيَر تَايِي فَاتَن أَاللَّه يَا جِقَنسَ يَا كُمَ سَ يَا هُوتَ.

13/07/2025

ME YASA SAI SANATOCIN JIHAR KATSINA KAWAI AKE MAGANA KAN TAZARCEN TINUBU...?
مِي يَسَ سَي سَنَتُوثِن جَهَر كَشِنَه كَوَي أَكٖي مَغَنَ ...؟
Da yake an d'ora tukunyar zab'en 2027 kuma har ta fara tafarfasa, sannan jihohin k'asar nan duk inda ka kasa kunne zaka ji maganar Jam'iyyar had'aka ake domin sun yunk'uro don wantsakalar da takarar da Shugaban k'asa Tinubu keso ya yi tazarce a zab'en 2027 mai zuwa da kuma d'aura d'ammarar tunkarar duk wani gwamna da suke ganin zai taimaka wajen tazarcen Shugaban k'asa Tinubu ; amma a jihar Katsina abin ya bambanta, su sanatocinsu na shiyyoyi uku dake jihar ta Katsina su ake ta tattauna batunsu kan batutuwan wakilcin da s**a tura su a majalisar Dattawa a Abuja.

دَ يَكٖي اَن طُورَ تُكُنیَر زَاٻٜن ٢٠٢٧, كُمَ هَر تَا فَارَ تَفَرفَسَ ۭ سَننَن جِهُوهِن قَسَر نَن دُك اِندَ كَ كَسَ كننٖي زَاكَ جِي مَغَنَر جَمعِييَر هَطَاكَ أَكٖي دُومِن سُن يُونقُرُو دُون وَنثَكَلَر دَ تَكَرَر دَ شُوغَبَن قَسَ تِنُبُ كٖيسُو يَايِي تَزَرثٖي أَ زَابٖين ٢٠٢٧ مَي زُووَ دَ كُمَ طَورَ طَممَرَر تُنكَارَر دُك وَانِي ڠَمنَ دَ سُكٖي غَنِن زَي تَيمَكَ وَجَن تَزَرثٖين شُوغَبَن قَسَ تِنُوبُ ; اَممَا اَ جِهَر كَڟِنَ اَبِن یَا بَمبَنتَ, سُ سَنَتُوثِنسُ نَا شِییُویِي اُككُ دَكٜي جِهَر تَا كَڟِنَ سُكٜي تَا تَتتَونَاوَ كَن بَتُوتُووَن وَكِلثِن دَ سُكَ تُورَ سُ اَ مَجَلِسَر دَتتَاوَ اَ اَبُوجَ.
Wasu naganin wad'annan sanatoci sun yi abin a zo a yaba, musamman kan yadda s**a k'ek'asa k'asa s**a dage da cewa, sai Tinubu ya zarce٬ wasu kuwa cewa suke su ba abin da s**a wakilta su suje majalisar su yi ba kenan.
وَسُ نَاغَنِن وَطَننَن سَنَتُوثِ سُن یِي اَبِن اَ زُو اَ یَبَ, مُسَممَن كَن یَددَ سُكَ قٖيقَسَ قَسَ سُكَ دَاغٜي دَ ثٜيوَ, سَي تِنُوبُ یَا زَرثٜي٬ وَسُ كُوَ ثٜيوَ سُكٜي سُو بَ اَبِن دَ سُكَ وَكِلتَاسُ سُ جٖي أَ مَجَلِسَر سُ يیِ بَ كٖينَن.
Wannan cece-kuce da yake ta yawo a jihar yasa Mujallar Ajami-Booko ta tura wakilanta a shiyyoyin jihar Katsina guda uku, shiyyar Katsina da Daura da kuma ta Funtuwa domin baza komarsu don farauto da jiyo dalilan wannan cece-kuce a kuma bayyana wa masu bibiyar kafarmu ta labarai.
وَننَن ثٜيثٜي-كُثٜي دَ یَكٜ تَا یَاوُو اَ جِهَر یَسَ مُجَللَر عَجَيمِ-بُوكُو تَ تُورَ وَكِيلَنتَ اَ شِییُویِن جَهَر كَڟِنَ غُدَ أُككُ شِييَر كَڟِنَ دَ دَورَ دَ كُمَ تَا فُنتُوَ دُومِن بَزَ كُومَرسُ دُون فَرَوتُو دَ جِیُو دَلِيلَن وَننَن ثٜيثٜي-كُثٜي أَ كُمَ بَییَنَا وَ مَاسُ بِبِیَر كَفَرمُ تَا لَابَرَِي.
Don haka, abiyo mu a sati mai zuwa domin samun cikakken rahoton da wakillanmu s**a ruwaito mana.
دُون هَكَ, اَبِیُو مُ اَ سَاتِ مَي زُووَ دُومِن سَامُن ثِكَككٜين رَهُوتُن دَ وَكِللَنمُ سُكَ رُوَيتُو مَنَ.

ASHA KALLO ! ASHA KALLO !!       ASHA KALLO !!!أَ شَا كَلُّو ! أَ شَا كَلُّو !! أَ شَا كَلُّو !!!Gawurtaccen Mataimaki M...
10/07/2025

ASHA KALLO ! ASHA KALLO !! ASHA KALLO !!!
أَ شَا كَلُّو ! أَ شَا كَلُّو !! أَ شَا كَلُّو !!!
Gawurtaccen Mataimaki Mai Amana.....Mai girma Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Malam Faruq Lawal (Sarkn Fulanin Joben Katsina).

غَاوُرتَثثٖين مَاتَيمَكِي مَي أَمَانَ...مَيغِرمَ مَتَيمَكِن غُمنَن جَهَر كَشِنَه مَالَم فَارُق لَاوَل ( سَركِن فُلَانِن جُوبٖين كَشِنَه).

A wajen k'addamar da Littafi mai suffanta yadda tsohon shugaban k'asa Muhammadu Buhari ya mulki Najeriya mai suna “According To The President”.
أَ وَجَن قَددَمَر دَ لِتَّافِ مَي سُففَنتَ يَدَّ ثُوهُون شُوغَبَن قَسَ ﷴُ بُهَارِي يَ مُلكِ نَجٖيرِيَ مَي سُونَ " أَكُودِنت تُو زٖي فِرٖيزدٖنت".
Wanda tsohon mai baiwa tsohon shugaban k'asa shawara kan lamurran yad'a labarai Malam Garba Shehu ya rubuta.
وَندَ ثُوهُون مَي بَا شُوغَبَن قَسَ شَاوَرَ كَن لَمُررَن يَاطَ لَابَرَي مَالَم غَربَ شٖيهُ يَا رُبُوتَ.
An yi taron k'addamar da Littafin a d'akin taro na "Shehu Musa Yaradua Center" da ke Abuja ranar Laraba, 9 ga watan Yulin 2025.
أَن يِي تَارُون قَدَّمَر دَ لِتتَافِن أَ طَاكِن تَارُو نَ "شٖيهُ مُوسَ يٖير أَدُوَ سَنتَ" دَ كٖي أَبُوجَ٬ أَ رَانَر لَارَبَ ٩ غَ وَتَن يُولِن ٢٠٢٥.

ABIN DA SANI AHMAD ZANGINA YA FA'DA KAN 'YAN JAM'IYYAR HA'DAKA TA ADC GASKIYA NE ?**اَبِن دَ سَانِي اَحمَد زَنغِنَ یَا ف...
10/07/2025

ABIN DA SANI AHMAD ZANGINA YA FA'DA KAN 'YAN JAM'IYYAR HA'DAKA TA ADC GASKIYA NE ?
**اَبِن دَ سَانِي اَحمَد زَنغِنَ یَا فَطَ كَن عٖین جَمعِییَر هَطَاكَ تَ عٖي-دِي-سِي غَسكِیَ نٜي ?*
Sani Ahmad Zangina ya bayyana cewa, " gaba d'ayan ‘Yan'jam’iyyar had'aka ta ADC ‘Yan'wasan Kwaikwayo ne", kuma ya k'ara da cewa ," Nasiru El-rufa’i Shi ne Akta wato tauraron wasan.
سَانِي اَحمَد زَنغِنَ یَا بَییَنَ ثٜوَ, " غَبَا طَیَن ‘یٖنجَم إِییَر هَطَاكَ تَ عٖي-دِي-سَي یٖين وَاسَن ݣَويݣَویُو نٜي ?", كُمَ یَا قَارَ دَ ثٜوَ ," نَاصِرُو اٜل-رُفَلإِي شِي نٜي اَكتَ وَاتُو تَُورَارُن وَاسَن.
Wannan furucin Mujallar Ajami-Booko ta nak'alto shi ne a firar da Zangina ya yi da gidan Talabijin na Farin Wata da Rukunin Gidajen Radio Vision FM Abuja.
وَننَن فُرُثِن مُجَللَر عَجَيمِ-بُوكُو تَا نَقَلتُو شِ نٜي اَ فِيرَر دَ زَنغِنَ یَا یِي دَ غِدَن تَلَبِجِن نَا فَرِن وَتَ دَ رُكُنِن غِدَاجٜن رَادِيُن سِشِن عٖيف-عٖيم اَبُوجَ.
Abin tambaya da a kan wannan kalmomi na Alhaji Sani shi ne, " shin dagaske ne wad'annan manyan 'yan'siyasar da ke k'okarin yin had'aka a jam'iyyar ADC duk ‘Yan wasan kwaikwayo ne aka tara a cikin wannan Jam’iyyar kuma El-Rufa'i shi Jigo ?
اَبِن تَمبَیَ اَ كَن وَننَن كَلمُومِي نَ اَلهَجِ سَانِ شِي نٜي, " شِن دَغَسكٜ نٜي وَطَننَن مَنیَن عٖین سِیَاسَر دَ كٜي قُوقَرِن یِن هَطَاكَ اَ جَمعِییَر عٖي-دَي-سِي دُك ‘یَن وَاسَن ݣَِوݣَوایُو نٜي اَكَ تَارَ اَ ثِكِن وَننَن جَمعِییَر٬ كُمَ عٖيل-رُفَاعِ شِي نٖي جِيغُو ?

Kotun Abuja ta sanya ranar 3 ga Oktoba domin yanke hukunci kan karar da mazabar Kogi ta tsakiya s**a yi a kan dakatar da...
10/07/2025

Kotun Abuja ta sanya ranar 3 ga Oktoba domin yanke hukunci kan karar da mazabar Kogi ta tsakiya s**a yi a kan dakatar da Akpoti-Uduaghan | Sahara Reporters
سَهَارَ رِفُوتَس تَاثٖي| كُوتُن أَبُوجَ تَا سَنيَ رَانَر ٣ غَ أُوكتُوبَ دُومِن يَنكٖي هُكُنثِ كَن قَارَر دَ مَزَابٰر كُوغِ تَ ثَكِيَ سُكَ يِي أَ كَن دَاكَتَر دَ أَكفُوتِ-أُدُوَغَهن.

09/07/2025
GASAR KOFIN GWAMNA RADDA...ZAKUNA BIYU SUN GURJI JUNA... NSCDC da NFP.غَاسَر كُوفِن غُمنَ رَطَّ ... زَاكُنَ بِيُو سُن غُ...
28/06/2025

GASAR KOFIN GWAMNA RADDA...ZAKUNA BIYU SUN GURJI JUNA... NSCDC da NFP.
غَاسَر كُوفِن غُمنَ رَطَّ ... زَاكُنَ بِيُو سُن غُرجِ جُونَ...يٖين.سٖيس.سِي.دِي.سِي دَ يٖين.يٖيف.فِي.
A ci gaba da gudanar da gasar Kofin Mai garma Gwamna Malam Dikko Umar Radda a tsakanin Jam'an tsaron jihar Katsina, a yau Asabar 28 ga watan Yuni, 2025 'Kungiyar Kwallon k'afa ta jami'an 'yan sanda da takwararta ta 'Civil Defence' sun gurji juna.
أَ ثِي غَبَ دَ غُدَانَر دَ غَاسَر كُوفِن مَي غِرمَ غُمنَ مَالَم دِكُّو عُومَر رَطَّ أَ ثَكَانِن جَامِعَن ثَرُون جَهَر كَشِنَه٬ أَ يَو أَسَبَر ٢٨ غَ وَاتَن يُونِي, ٢٠٢٥ 'قُنغِيَر كُولُّون قَفَ تَا جَامِعَن يٖن سَندَ دَ تَكُورَتَّ تَا 'سِيبِل دِفٖينس' سُن غُرجِي جُونَ.
An fara wasan da misalin k'arfe tara na safe, kuma duk wanda ya shedi wasan da farko ba zai iya hasashen k'ungiyar da za ta yi galaba a kan 'yar uwarta ba domin kowace k'ungiyar k'wallon k'afa 'yan wasanta kamar zakuna suke, shiya sa ma a cikin mintuna ashirin da biyar da fara wasan aka ci k'wallaye uku kafin a tafi hutun rabin lokaci.
أَن فَارَ وَاسَن دَ مِسَالِن قَرفٖي تَرَ نَا سَافٖي٬ كُمَ دُك وَندَ يَا شٖيدِ وَاسَن دَ فَركُو بَ زَي إِيَ هَسَاشٖين قُنغِيَر دَ زَاتَ يِي غَلَبَ أَ كَن يٖرعُوَرتَ بَا دُومِن كُووَثٖي قُنغِيَر كُولُّون قَفَ يٖن وَاسَنتَ كَمَر زَاكُنَ سُكٖي٬ شِي يَاسَ مَا أَ ثِكِن مِنتُنَ أَشِرِين دَ بِيَر دَ فَارَ وَاسَن أَكَ ثِي كُولَّايٖي أُكُّ كَافِن أَ تَافِ هُوتُون رَابِن لُوكَثٖي.
'Yan k'wallon 'Civil Defence' da s**a dufafi ragar 'yan k'wallon 'yan sanda a kai ruma-ruma sai d'an wasan 'yan sanda ya jawo ma 'kungiyarsu bugun daga kai sai mai tsaron gida ; inda aka sha su d'aya da nema, wannan nasara da 'yan Civil Defence s**a samu ta jaza kace-nace daga b'angaren magoya bayan 'yan sanda inda akai ta canza yawu...bayan komawa k'wallon sai ga shi 'yan sandan sun farke har sun k'ara guda d'aya...a nan ne suma magoya bayan jami'an tsaron 'yan Civil Defence s**a rik'a bayyana k'orafinsu wajen alk'alin wasan da cewa, " don 'yan sanda sun zare maka ido sai ka k'i hura gaskiya bayan kaga yadda suke tafka laifi ?"
يٰين كُولُّون ٰسِيبِل دِفٖينس' دَ سُكَ دُفَافِي رَاغَر يٖين كُولُّون يٖين سَندَ أَ كَي رُمَ-رُمَ سَي طَن وَاسَن يٖن سَندَ يَا جَاوُو مَ قُنغِيَرسُ بُغُن دَاغَ كَي سَي مَي ثَرُون غِدَ; إِندَ أَكَ شَاسُ طَيَ دَ نٖيمَ٬ وَنَّن نَسَرَ دَ يٖين سِيبِل دِفٖيس سُكَ سَامُ تَا جَازَ كَثٖي-نَثٖي دَاغَ بٰنغَارٖين مَغُويَ بَايَن يٖين سَندَ إِندَ أَ كَي تَا ثَنزَ يَاوُو...بَايَن كُومَاوَ كُولُّون سَي غَاشِ يٖين سَندَن سُن فَركٖي هَر سُن قَارَ غُدَا طَيَ...أَ نَنّٖي سُومَ مَغُويَا بَايَن جَامِعَن ثَرُون يٖين سِيبِل دِفٖينس سُكَ رِقَ بَيَّنَا قُورَفِنسُ وَجَن أَلقَالِن وَاسَن دَ ثٖيوَ٬" دُون يٖين سَندَ زَارٖي مَكَ إِدُو سَي كَقِِي هُورَ غَسكِيَ بَايَن كَاغَ يَدَّ سُكٖي تَفكَ لَيفِي؟".
Daga k'arshe dai wasan ya tashi biyu da d'aya. Sannan bayan tashi daga wasan "Mujallar Ajami-Booko sashen Rediyo sun zanta da Ko'odinatan gasar, Koc Abdullahi Wuro a kan b'angarori daban-daban da s**a shafi gasar kuma ya yi cikakken bayani kai, sai a biyomu a shirinmu na rediyo a gobe Lahadi da misalin k'arfe tara na dare aji me firar ta k'unsa.
دَاغَ قَرشٖي دَي وَاسَن يَا تَاشِ بِيُو دَ طَيَ. سَنَّن بَايَن تَاشِ دَاغَ وَاسَن "مُجَلَّر عَجَمِي-بُوكُو سَاشٖين رٖيدِيُو سُن زَنتَ دَ كُوعُودِنٖيتَن غَسَر٬ كُوث عَبدُاللَّهِ وُرُو أَ كَن بٰنغَرُورِي دَبَن-دَبَن دَ سُكَ شَافِ غَاسَر كُمَ يَايِي ثِكَكّٖين بَيَانِي٬ أَ كَي. سَي أَ بِيُومُ أَ شِرِنمُ نَا رٖيدِيُو أَ غُوبٖي لَهَدِ دَ مِسَالِن قَرفٖي تَرَ نَا دَرٖي... أَجِي مِي فِيرَر تَا قُنسَ.

28/06/2025

ZAMANI RIGA...: MANUFAR MUJALLAR AJAMI-BOOKO A WANNAN ZAMANI ABIN A YABA NE DA SHIGA CIKIN LAMARIN MUJALLAR DOMIN FIDDA 'DAN DUMA DAGA CIKIN KABEWA !!!
زَامَنِي رِيغَ...: مَنُفَر مُجَلَّر عَجَمِي-بُوكُو أَ وَنَّن زَامَنِي أَبِن أَ يَبَ نٖي دَ شِغَ ثِكِن لَمَرِن مُجَلَّر دُومِن فِدَّ طَن دُمَ دَاغَ ثِكِن كَبٖيوَ!!!
Shi dai rubutun ajami, wani nau'in salon rubutu ne da Bahaushe ya samar daga harrufan Larabci. Wannan salon rubutu yana ɗaya daga cikin daɗaɗɗun hanyoyin rubutu da aka yi amfani da ita a Ƙasar Hausa. Zarruƙ, Kafin Hausa, da Al-Hassan (1987), sun ce an haura sama da shekaru ɗari da hamsin ana amfani da wannan hanya ta rubutun ajami a Ƙasar Hausa kafin zuwan rubutun boko. Mashahuran malaman Musulunci na ƙarni na goma sha tara kamar irin su Mujadaddi Shehu Ɗanfodiyo da almajiransa, sun yi amfani da wannan salon rubutu wajen rubuta littattafai da waƙoƙi da isar da sakonni.
شِي دَي رُبُوتُن عَجَمِي٬ وَنِ نَوعِن سَلُون رُبُوتُ نٖي دَ بَهَوشٖي يَا سَمَر دَاغَ هَرُفَّن لَارَبثِي. وَنَّن سَلُون رُبُو نٖي دَ بَهَوشٖي يَا سَمَر دَاغَ هَرُفَّن لَارَبثِي. وَنَّن سَلُون رُبُوتُ يَنَ طَيَ دَاغَ ثِكِن دَطَطُّن هَنيُويِين رُبُوتُ دَ أَكَ يِي أَمفَانِ دَ إِتَ أَ قَسَر هَوسَ. زَرُّق٬ كَفِن هَوسَ٬ دَ أَلحَسَن (١٩٨٧)٬ سُن ثٖي أَن هَورَ سَمَ دَ شٖيكَرُو طَرِي دَ هَمسِن أَنَا أَمفَانِي دَ وَنَّن هَنيَ تَا رُبُوتُن عَجَمِي أَ قَسَر هَوسَ كَافِن زُووَن رُبُوتُن بُوكُو. مَشَهُورَن مَالَمَن مُسُلُنثِي نَا قَرنَي نَا غُومَ شَا تَارَ كَمَر إِرِن سُو مُجَدَّدِي شٖيحُ طَنفُودِيُو دَ أَلمَاجِرَنسَ٬ سُن يِي أَمفَانِي دَ وَنَّن سَلُون رُبُوتُ وَجَن رُبُوتَ لِتَّتَّافَي دَ وَاقُوقِي دَ إِسَر دَ سَقُنِّي.
Farfesa Bunza (2002), ya fassara shi da cewa, “ajami na nufin rubutun harshen Hausa cikin harufan Larabci”.
فَرفٖيسَ عَلِيُّ ﷴُ بُنزَا(٢٠٠٢)٬ يَا فَسَّارَ شِي دَ ثِيوَ٬ عَجَمِي نَا نُوفِن رُبُوتُن هَرشٖين هَوسَ ثِكِن هَرُفَّن لَارَبثِي".
Dangane da yaushe ne kuma a ina aka fara yin rubutun ajami kuwa, masana fannin Hausa sun yi rubuce-rubuce masu yawa kowa da nasa ra’ayin. Farfesa Bunza (2002), yana ganin cewa rubutun ajami ya wanzu a Ƙasar Hausa tun kafin zuwan Musulunci, ta in da ya kafa hujjoji da zuwan Bayajidda, da kuma dangantakar cinikayya da ta sarauta da ta wanzu tsakanin Ƙasar Hausa da kuma Ƙasashen Larabawa.
دَنغَنٖي دَ يَوشٖي نٖي كُمَا أَ إِنَا أَكَ فَارَ يِن رُبُوتُن عَجَمِي كُوَا٬ مَسَنَا فَنِّن هَوسَ سُن يِي رُبُوثٖي-رُبُوثٖي مَاسُ يَوَ كُووَ دَ نَاسَ رَعَيِن. فَرفٖيسَ عَلِيُّ ﷴُ بُنزَا(٢٠٠٢)٬ يَا نَ غَنِنثٖيوَ رُبُوتُن عَجَمِي يَا وَنزُو أَ قَسَر هَوسَ تُن كَافِن زُووَن مُسُلُنثِي٬ تَ إِندَ يَا كَفَ هُجُّوجِي دَ زُووَن بَايَجِدَّ٬ دَ كُمَا دَنغَرتَكَر ثِنِكَيَّ دَاتَا سَرَوتَ دَاتَ وَنزُو ثَكَانِن قَسَر هَوسَ دَ كُمَا قَسَشٖين لَارَبَاوَ.
Shi kuwa Ɗanmasanin Kano, Alhaji (Dr.) Yusuf Maitama Sule, ya bayyana cewa malam Ɗanmasani na Katsina shi ne ya ƙirƙiro rubutun ajami na Hausa. A wannan ra'ayi nasa yau kenan ana lissafa shekarun ajami kusan shekaru ɗari bakwai kenan.
شِي كُوَا طَنمَسَنِن كَانُو٬ أَلهَجِ (دَكتَ) يُوسُف مَيتَامَ سُلٖي٬ يَا بَيَّنَ ثٖيوَ مَالَم طَنمَسَنِي نَا كَشِنَه شِي يَا قِرقِرُو رُبُوتُن عَجَمِي نَا هَوسَ. أَ وَنَّن رَعَيِي نَاسَ يَو كٖينَن أَنَ لِسَّافَ شٖيكَرُون عَجَمِي كُسَن شٖيكَرُو طَرِي بَكُوي كٖينَن.
Sai dai, wani abu da ya fito fili shi ne cewa yaɗuwar addinin Musulunci a Ƙasar Hausa ta taimaka gaya wajen shaharar wannan salo na rubutu. Sannan kuma ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen ci gaban rubutu a cikin harshen Hausa.
سَيدَي٬ وَنِ أَبُو دَ يَا فِتُو فِيلِي شِي نٖي ثٖيوَ يَطُوَر أَدِّينِن مُسُلُنثِي أَ قَسَر هَوسَ يَا تَيمَكَ غَايَ وَجَن شَهَرَر وَنَّن سَلُون رُبُوتُ.
سَنَّن كُمَا يَا بَايَر دَ غَغَرُمَر غُدُمُّوَا وَجَن ثِي غَبَن رُبُوتُ أَ ثِكِن هَرشٖي هَوسَ.
Nazarin wadannan zantuka na masana ya zaburarar da mawallafin 'Mujallar Ajami-Booko', malam Rabi'u Ibrahim wanda aka fi sani da suna 'Go slow' , kuma haifaffen garin Katsina domin kafa wannan kafar labarai don kusanto da cike gibin da ke tsakanin masu ilimin boko da malamanmu na Tsangaya, masana Littafin Allah, ( Hadisai da Littafan Ilimi)da Almajiransu wadanda tun tali-tali suke amfani da haruffan Larabci (Ajami) wajen isar da sakunansu.
نَزَرِين وَطَنَّن زَنتُتُّكَ نَا مَسَنَا يَا زَابُرَر دَ مَوَلّافِن "مُجَلَّر عَجَمِي-بُوكُو" , مَالَم رَابِعُ إِبرَاهِيم وَندَ أَكَ فِ سَنِي دَ سُونَ 'غُوسِلُو' كُمَا هَيفَفّٖين غَرِن كَشِنَه دُومِن كَفَ وَنَّن كَفَر لَابَرَي دُون كُسَنتُو دَ ثِكٖي غِيبٖين دَ كٖي ثَكَانِن مَسُ إِلِمِين بُوكُو دَ مَلَمَمُّو نَا ثَنغَيَ٬ مَسَنَا لِتَّافِن أَللَّه٬(هَدِيسِي دَ لِتَتَّفَن إِلِمِي) دَ أَلمَاجِرَنسُ وَطَندَ تُن تَلِ-تَلِ سُكٖي أَمفَانِي دَ هَرُفَّن لَارَبثِي(عَجَمِي) وَجَن إِسَر دَ سَاقُنَنسُ.
Ganin yadda ake ta samun sabani tsakanin Malamammu na Tsangaya a gefen abin da aka rubuta a matsayin Jarida ko kuma abin da aka watsa a cikin kafar watsa labarai na zamani "social media"ko wadanda aka saba da su na al'ada "conventional" media, shi ne ya sa "Mujallar Ajami-Booko" ta fito don ta yi sulhu tsakani.
غَنِن يَدَّ أَكٖي تَا سَامُن سَبٰنِي ثَكَانِن مَلَمَمُّو نَا ثَنغَيَ أَ غٖيفٖين أَبِن دَ أَكَ رُبُوتَ أَ مَثَيِن جَرِيدَ كُو كُمَا أَبِن دَ أَكَ وَاثَ أَ ثِكِن كَفَر سَادَروَر زَامَنِي "سُوشِيَل مِيدِيَ" كُو وَطَندَ أَكَ سَابَ دَ سُ نَا أَلعَادَ "كُونبٖينشِنَل مِدِيَ", شِي نٖي يَسَ "مُجَلَّر عَجَمِي-بُوكُو" تَا فِتُو دُون تَ يِي سُلهُ ثَكَنِي.
Gano dalilan wannan sabani da Mujallar Ajami-Boko ta yi ta sa ta yunkuro don wallafa labarai da makaloli makamantan irin wadanda ake bugawa a jaridun harshen Turanci da Larabci da Hausar Boko tsantsa, domin wayar da kai da ilimantarwa da fadakarwa da ma nishadantarwa ga al'ummar da ke zaune a kasar Hausa da ma masu sha'awar karatun ajami musamman wadanda ba su iya karanta wani rubutun da ba ajami ba.
غَانُو دَلِيلَن وَنَّن سَافٰانِي دَ مُجَلَّر عَجَمِي-بُوكُُو تَايِي تَاسَ تَا يُنقُرُو دُون وَلَّافَ لَابَرَي دَ مَقَالُولِي مَكَمَنتَن إِرِن وَطَندَ أَكٖي بُغَاوَ أَ جَرِيدُن هَرشٖين تُورَنثِي دَ لَارَبثِي دَ هَوسَر بُوكُو ثَنثَ٬ دُومِن وَايَر دَ كَي دَ إِلِمَنتَروَ دَ فَطَكَروَ دَ مَا نِشَاطَنتَروَ غَ أَلعُمَّر دَ كٖي زَونٖي أَ قَسَر هَوسَ دَ مَا مَاسُ شَعَوَر كَرَاتُن عَجَمِي مُسَمَّن وَطَندَ بَاسُ إِيَ كَرَنتَ وَنِي رُبُوتُن دَ بَا عَجَمِي بَا.
Kuma Mujallar Ajami-Boko ta fahimci cewa, salon labarai da rubutun dan shekara tisi'in ya bambanta da na dan shekara arba'in haka na dan shekara talatin abin da yawo kasa na shi salon daban yake.
Wannan abu ba kome ya kawo shi ba face, kowa na da irin rayuwar da ya tashi cikinta.
كُمَ مُجَلَّر عَجَمِي-بُوكُو تَا فَهِمثِي ثِيوَ٬ سَلُون لَابَرَي دَ رُبُوتُن طَن شٖيكَرَ تِسِعِن يَا بَمبَنتَ دَ نَا طَن شٖيكَرَ أَربَعِن هَكَ نَا طَن شٖيكَرَ تَلَاتِن أَ بِن دَ يَاوُو قَسَ نَاشِ سَلُون دَبَن يَكٖي. وَنّن أَبُو بَا كُومِي يَا كَوُوشِ بَا فَاثٖي٬ كُووَ نَادَ إِرِن رَايُوَر دَ يَا تَاشِ ثِكِنتَ.
Fahimtar wannan danbarwa ta sa Mujallar Ajami da Boko cewa idan ana son daidaito a cikin wannan lamari, to salon rubutun yanzu da zai hade malamanmu na tsangaya da 'yan bokonmu ya kasance gamin gambiza, ya kunshi abin da kowane bangare ya sani. Sannan masana lamuran da ke zuwa suna dawowa sun ce suna da tabbacin cewa, ta hanyar farfado da tsarin karatu da rubutun Ajamin Hausa wanda ake amfani da shi a makarantun addinin Musulunci, wadanda s**a hada da makarantar Tsangaya da Islamiyya da kuma na Allo ; sannan a gauraya shi da da rubutun boko zai daidaita bisa kashin bayan zamani.
فَهِمتَر وَنَّن دَمبَروَ تَاسَ مُجَلَّر عَجَمِي دَ بُوكُو ثِيوَ إِدَن أَنَ سَن دَيدَيتُو أَ ثِكِن وَنَّن لَمَرِي٬ تُو سَلُون رُبُوتُن يَنزُو دَ يَكَمَاتَ دَ زَي هَطٖي نَا مَلَمَمُّو نَا ثَنغَيَ دَ نَا يَن بُوكُومُّومُّ يَا كَسَنثٖي غَمِن-غَمبِيزَ٬ يَا قُنشِ أَ بِندَ كُووَنٖي بٰنغَارٖي يَا سَنِي. سَنَّن مَسَنَا لَمُرَّن دَ كٖي زُووَ سُنَ دَاوُووَ سُن ثٖي٬ سُنَ دَ تَبَّ ثِن ثِيوَ٬ تَا هَنيَر فَرفَاطُو دَ ثَرِن كَرَاتُو دَ رُوبُوتُن عَجَمِين هَوسَ وَندَ أَكٖي أَمفَنِي دَ شِي أَ مَكَرَنتُن أَدِّينِن مُسُلُنثِ٬ وَطَندَ سُكَ هَطَ دَ مَكَرَنتَر ثَنغَيَ دَ إِسلَمِيَّ دَ كُمَا نَا أَلاُّو ; سَنَّن أَ غَورَيَا شِي دَ رُبُوتُن بُوكُن زَي دَيدَيتَ بِسَ قَشِن بَايَن زَامَنِي.
Daga Karshe, cikin murna da farin ciki Mujallar Ajami-Boko wadda ta hada da sashen Rediyo da Talabijin a kafar Sadarwar Zamani (Social Media) kuma take gabatar da wannan aiki nata, saboda ta sani kuma tana alfahari da tunkaho da Musulunci a kasar Hausa kuma dalilin samuwar Musuluncin rubutun ajami ya inganta har ya samu tagomashi a wancan zamani har ya dara wa tsara ; to don haka, ko ba a yaba wa wannan kafa ba a kan wannan aikin, to za a ya ba mata a kan kyakkyawar niyyarta a kan manufar.
دَاغَ قَرشٖي٬ ثِكِن مُرنَ دَ فَرِن ثِكِ مُجَلَّر عَجَمِي-بُوكُو وَدَّ تَا هَطَ دَ سَشٖين رٖيدِيُو دَ تَلَبِجِن أَ كَفَر سَدَروَ تَا زَامَنِي (سُوشِيَل مِيدِيَ) كُمَ تَكٖي غَبَاتَر دَ وَنَّن أَيكِ نَاتَ٬ سَبُودَ تَا سَنِي كُمَ تَنَ أَلفَهَرِي دَ تِنقَاهُو دَ مُسُلُنثِ أَ قَسَر هَوسَ كُمَ دَلِيلِن سَمُوَر مُسُلُنثِن رُبُوتُن عَجَمِي يَا إِنغَنتَ هَر يَا سَمُ تَغُومَشِي أَ وَنثَن زَامَنِي يَا طَرَ وَ ثَارَ ; تُو دُون هَكَ٬ كُو بَعَ يَبَ وَ وَنَّن كَفَ بَ أَ كَن وَنَّن أَيكِن٬ تُو زَاعَ يَبَ مَتَ أَ كَن كٖيككٰاوَر نِيَّرتَ أَ كَن مَنُفَر.
Wannan kafa ta Mujallar Ajami-Boko na taya dukkan musulmin duniya (musamman wadanda ke zaune a kasar Hausa), murnar shigowa sabuwar shekarar Musulunci.
وَنَّن كَفَ تَا مُجَلَّر عَجَمِي-بُوكُو نَا تَيَ دُكَّن مُسُلمِن دُونِيَ (مُسَمَّن وَطَندَ كٖي زَونٖي أَ قَسَر هَوسَ)٬ مُرنَر شِغُووَ سَبُوَر شٖيكَرَر مُسُلُنثِ.

Kungiyar 'Yan jarida ta k'asa za ta yi bikin cika shekaru  70 da kafuwa....قُنغِيَر يَنجَرِيدَ تا قَسَ زَاتَ يِي بِكِن ث...
09/06/2025

Kungiyar 'Yan jarida ta k'asa za ta yi bikin cika shekaru 70 da kafuwa....
قُنغِيَر يَنجَرِيدَ تا قَسَ زَاتَ يِي بِكِن ثِكَ ا شٖيكَرُو ٧٠ دَ كَفُوَ.

Address

Chittagong Division

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mujallar Ajami/Boko عَجَمِيْ اَلْقَلَمِنْ اَرٖيْوَ نَ فَرْكُوْا posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mujallar Ajami/Boko عَجَمِيْ اَلْقَلَمِنْ اَرٖيْوَ نَ فَرْكُوْا:

Share