30/05/2026
Gobara Ta Hallaka Dalibai 16 a Makarantar Kwana ta jami’ar kenyatta dake nairobi a kasar Kenya
Iyalan daliban da abin ya shafa sun wayi gari cikin alhini da fargaba a gaban makarantar kwana bayan wata mummunar gobara da ta tashi da tsakar dare a ɗakin kwanan dalibai. Gobarar ta yi sanadin mutuwar dalibai 16 tare da jikkata wasu 79.
Mahukunta sun tabbatar da k**a dalibai mata takwas da ake zargi da haddasa gobarar da gangan. Sai dai har zuwa yanzu ba a fara tantance gawarwakin waɗanda s**a rasa rayukansu ba, lamarin da ya ƙara jefa iyalai da dangi cikin damuwa da rashin tabbas.
Yayin da ake ci gaba da bincike kan musabbabin gobarar, iyalan waɗanda abin ya shafa na ci gaba da neman bayani daga hukumomi game da halin da ‘ya’yansu ke ciki da kuma yadda wannan mummunan al’amari ya faru.
Wannan lamari ya girgiza al’umma tare da tayar da tambayoyi kan tsaro da kula da dalibai a makarantun kwana.