Bakandamiya TV

Bakandamiya TV Informations de contact, plan et itinéraire, formulaire de contact, heures d'ouverture, services, évaluations, photos, vidéos et annonces de Bakandamiya TV, Chaîne de télévision, Douala.
(2)

Bakandamiya TV tasha daya tilo dake watsa shirye-shiryen ta cikin harshen hausa zalla sannan tana maïda hankali akan al'adu zamantakewar malam bahaushe tare da kawo muku labaru masu inganci domin sanin me duniya take ciki.

Gobara Ta Hallaka Dalibai 16 a Makarantar Kwana ta jami’ar kenyatta dake nairobi a kasar Kenya Iyalan daliban da abin ya...
30/05/2026

Gobara Ta Hallaka Dalibai 16 a Makarantar Kwana ta jami’ar kenyatta dake nairobi a kasar Kenya
Iyalan daliban da abin ya shafa sun wayi gari cikin alhini da fargaba a gaban makarantar kwana bayan wata mummunar gobara da ta tashi da tsakar dare a ɗakin kwanan dalibai. Gobarar ta yi sanadin mutuwar dalibai 16 tare da jikkata wasu 79.

Mahukunta sun tabbatar da k**a dalibai mata takwas da ake zargi da haddasa gobarar da gangan. Sai dai har zuwa yanzu ba a fara tantance gawarwakin waɗanda s**a rasa rayukansu ba, lamarin da ya ƙara jefa iyalai da dangi cikin damuwa da rashin tabbas.

Yayin da ake ci gaba da bincike kan musabbabin gobarar, iyalan waɗanda abin ya shafa na ci gaba da neman bayani daga hukumomi game da halin da ‘ya’yansu ke ciki da kuma yadda wannan mummunan al’amari ya faru.

Wannan lamari ya girgiza al’umma tare da tayar da tambayoyi kan tsaro da kula da dalibai a makarantun kwana.

Amurka ta ce ta bai wa rundunar sojin Nijar gudunmawar kwantena tara ta kayan aikin soja da darajarsu ta kai kusan dala ...
30/05/2026

Amurka ta ce ta bai wa rundunar sojin Nijar gudunmawar kwantena tara ta kayan aikin soja da darajarsu ta kai kusan dala miliyan 2.3 domin tallafa wa ayyukan yaƙi da ƙungiyoyin masu aikata laifuka da na ‘yanta’adda.

A cewar wata sanarwa daga Ofishin Jakadancin Amurka da ke Niamey, an miƙa kayan ne ranar 26 ga Mayu, kuma sun haɗa da kayan sawa na soja, kayan kariya da kuma kayan kiwon lafiya.

Wannan tallafin na nuna ci gaba da haɗin gwiwar tsaro tsakanin Washington da yankin Sahel duk da takun-saƙar da ke tsakaninta da gwamnatocin yankin.

Ƙungiyar Gwamnoni Ta Nemi Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Maida Mafi Ƙarancin Albashi Ya Zama Naira Dubu 100Ƙungiyar Gwamnonin N...
30/05/2026

Ƙungiyar Gwamnoni Ta Nemi Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Maida Mafi Ƙarancin Albashi Ya Zama Naira Dubu 100

Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta bayyana goyon bayanta ga manufofin gyaran tattalin arziƙi na gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, tare da neman a ɗaga mafi ƙarancin albashin ma’aikata zuwa Naira Dubu Ɗari.

Shugaban NGF kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ne ya bayyana hakan inda ya ce sabon albashin zai dace da halin matsin tattalin arziƙi da tsadar rayuwa da ake ciki yanzu,

Ya ce gwamnatocin jihohi na ci gaba da tattaunawa da gwamnatin tarayya da kuma ƙungiyoyin ƙwadago domin cimma matsaya mai ɗorewa kan batun mafi ƙarancin albashi.

Ana sa ran wannan kira na neman albashin Naira 100,000 zai ƙara tasiri a tattaunawar da ake yi tsakanin gwamnati da ƙungiyoyin ƙwadago kan sabon tsarin albashi da sauran matakan rage raɗaɗin tattalin arziki ga ƴan Najeriya.

Majalisar wakilai ta Faransa ta kaɗa kuri'a da gagarumin rinjaye domin soke wasu dokokin daruruwan shekaru da s**a gabat...
29/05/2026

Majalisar wakilai ta Faransa ta kaɗa kuri'a da gagarumin rinjaye domin soke wasu dokokin daruruwan shekaru da s**a gabata wadanda s**a halatta bauta a kasashen da Faransa ta yi wa mulkin mallaka, abin da ya nuna wani mataki da ke nuna alamar damuwa da kuma fuskantar abubuwan da s**a faru a tarihin mulkin mallakar kasar.

Rasha ta yi kira ga Amurka da Iran su guje wa sake komawa fagen daga, a maimakon haka su ci gaba da bin hanyoyin neman s...
29/05/2026

Rasha ta yi kira ga Amurka da Iran su guje wa sake komawa fagen daga, a maimakon haka su ci gaba da bin hanyoyin neman sulhu ta lalata.
Zakharova ta ƙara da cewa a shirye Rasha take ta taimaka wajen karɓar mak**ashin yureniyum (uranium) ɗin da Iran ta inganta, sai dai ta ce Rashar ba za ta yi yunƙurin 'tilasta hakan ba

27/05/2026

SALLAH IDI NA LAYYA A BIRNIN DOUALA KAMARU 2026

Bayan an sauke shi daga kujerar Firaminista kwanaki hudu kacal aka ɗaga shi zuwa shugabancin Majalisar Dokoki ta ƙasa, O...
26/05/2026

Bayan an sauke shi daga kujerar Firaminista kwanaki hudu kacal aka ɗaga shi zuwa shugabancin Majalisar Dokoki ta ƙasa, Ousmane Sonko ya dawo tsakiyar ikon siyasa ta bangaren majalisa.

Ya koma majalisar dokoki tare da hawa matsayi na biyu mafi girma a ƙasar, bayan shugaban ƙasa Bassirou Diomaye Faye.

26/05/2026

BUKIN HAWAN KAHO A YAURI YA ZAMA AL’ADAR GARGAJIYA DA KE JAN HANKALIN JAMA’A DUK SHEKARA

26/05/2026

SM ALH. ADAMOU OUSSAINI LABBO NA 2
SARKIN HAUSAWAN DOUALA

26/05/2026

SM ALH. BAKO ABOUBAKAR
PRESIDENT DU CONSEIL DES CHEFS TRADITIONNELS DU LITTORAL ET DU SUD-OUEST

26/05/2026

LABARUN DUNIYA NA 26 MAYU 2026

Adresse

Douala

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Bakandamiya TV publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager