Whimsical graphics

Whimsical graphics Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Whimsical graphics, London.

We create eye-catching:
✅ Flyers & Posters
✅ Wedding & Birthday Invites
✅ Logos & Branding
✅ Business Cards & Social Media Graphics
✅ Brochures & Menus

01/07/2025
Babu Wanda Ya Cancanta Ya maye Gurbin Kakakin Shugaban ƙasa Ajure Ngelale K**ar Comr Adamu Garba IIA jiya ne Kakakin Shu...
08/09/2024

Babu Wanda Ya Cancanta Ya maye Gurbin Kakakin Shugaban ƙasa Ajure Ngelale K**ar Comr Adamu Garba II

A jiya ne Kakakin Shugaban ƙasa Ajure Ngelale yayi murabus daga mukaminsa Wanda tun Jiya Jama'a suke ta kai kawo na wa Yak**ata ya maye Gurbin wannan muƙami da ya ajiye.

Kasancewar Comr Adamu Garba II jajirtaccen ne wanda yake da kaifin basira da iya sarrafa al'umma, Yana da kwarewa Sosai wajen iya Magana da yaruka daban-daban. Wanda ina da tabbacin idan Tinubu ya bashi wannan muƙamin zai samar da tsare-tsare masu mahimmanci da zasu fito da ingantattun manufofin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bayanne, Ga yan Najeriya cikin sauki.

Muƙamin Kakakin Shugaban ƙasa yana buƙatar jajirtaccen Mutum wanda yake da juriya ta hanyar Hakuri da maganganun da mutane zasuyi akan shugaba da kuma fahimtar da al'umma ba Tare Da tsangwama ko cin fuska ba, Adamu Garba II yana daga cikin na Gaba-gaba da yake kare Gwamantin Tinubu duk da yana fuskantar s**a daga yan adawa Amma bai taba janye wa daga goyon bayansa ga Tinubu ba duk rintse duk wuya .

Misalai Guda biyu na farko a lokacin da shugaban Tinubu ya zama Ɗan Takarar Shugaban ƙasa na jam'iyar APC a Zaɓen da ya gabata na 2023. Wanda Comr Adamu Garba II haifaffen jihar Adamawa ne dake yankin Arewa maso Gabas jihar da ɗan Takarar Shugaban ƙasa na Jam'iyyar adawa Atiku Abubakar ya fito. Amma Hakan bai hana Adamu Garba jajircewa Wajen fahimtar da al'umma wanene Tinubu ba babu irin s**a da bai fuskanta ba a lokacin amma sai da muryar sa ta isa ko ina a fadin Arewacin Najeriya. Dangane da al'umma su zaɓe Tinubu shine Yafi kowa dacewa da cancanta.

Misali na biyu a yan kwanakin nan an kirkire Zanga-zanga adawa da Gwamnatin Tinubu Wanda a wannan lokacin Babu wani da yake cikin Gwamantin Tinubu da ya fito ya fahimtar da al'umma rashin alfanun Zanga-Zanga da kuma Irin Alheran da Tinubu ya samar da wanda yake da burin aiwatarwa K**ar Adamu Garba II. Wanda a wannan lokacin ba irin zage da bak'ar Magana da bai fuskanta ba Amma hakan bai sanya ya daina kare Gwamantin Tinubu ba Alhamdulillah Jama'a da dama da s**a Fahimci maganganunsa a lokacin sun janye daga shiga Zanga-Zangar.

Daga karshe Yana da kyau mashawartan Shugaba Tinubu su bashi shawara ta kwarai ɗaukan Adamu Garba II a matsayin Kakakinsa ba ƙaramin kariya bane A Gwamnatinsa duba da yadda a kullum ake ƙoƙarin Ganin an bata Gwamnatinsa a wajen yan Najeriya. Samun jajirtacce Irin Adamu Garba II zai dakile makirce-makirce da s**a dabaibaye Gwamnatinsa ba tare da samun cikas ba

Daga Comr Babangida Adamu
Haifaffen Jihar Bauchi dake arewa Maso Gabashin Najeriya

27/08/2024

Uwargidan Shugaban Najeriya Sen Oluremi Tinubu, wacce Uwargidan Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Haj Laila Barau Jibrin ta wakilta, ta bayar da Tallafin Naira Miliyan 50 ga mata Ƙananan Yan kasuwa kimanin 1,000 a Jihar Kaduna, .

A wani ɓangare na shirin bunƙasa tattalin arziki a karkashin ofishin Uwargidan Shugaban kasa. Shirin Karfafawa wani bangare ne na shirin sabunta bege, Wanda ke mayar da hankali kan inganta Rayuwar kananan ‘yan kasuwa, musamman mata a fadin kasar nan.

Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar sa, Sani Liman Kila shi ma ya yabawa shirin, inda ya bayyana goyon bayan Gwamnatin jihar kan shirye-shiryen.

Daukar Nauyi Babban Mataimaki na Musamman kan Hulda da Jama'a na Gwamnan Jihar Kaduna Mal Uba Sani,M S Ustaz Mesittin

Masu Ruwa da tsaki na kudancin Kaduna Zone 3 Sun Yabawa Gwamna Uba Sani bisa Gudanar da mulki ba tare da nuna kabilanci ...
25/08/2024

Masu Ruwa da tsaki na kudancin Kaduna Zone 3 Sun Yabawa Gwamna Uba Sani bisa Gudanar da mulki ba tare da nuna kabilanci ba.

A Ranar 24 ga Agusta, 2024, Masu Ruwa da tsaki daga kananan hukumomi takwas (LGAs) na yankin Kudancin Kaduna sun hallara a karamar hukumar Jema’a, Kafanchan, Domin tattauna ci gaban al’ummarsu Tattaunawar ta ta'allaka ne kan muhimman fannoni k**ar ilimi, kiwon lafiya, noma, da bunkasa jarin bil'adama.

Babban mataimaki na musamman (SSA) kan hulda da masu ruwa da tsaki na 1 ga Gwamnan Jihar Kaduna, MS Ustaz ne ya kira taron. Taron ya samu halartar wakilan JNI, CAN, Shugabannin jam’iyya, ƙungiyoyin kasuwa, da kungiyoyin tallafawa matasa da mata.

Masu ruwa da tsaki daban-daban sun yi bi-bi-bi-da-bi don tantance manufofi da ayyukan da s**a shafi jama'a da aka fara a karkashin Gwamnatin Sanata Uba Sani a shiyyar. Sun yabawa Gwamnan bisa salon jagorancin sa, Tare da amincewa da wasu ayyuka na musamman na inganta rayuwar al’ummar Kudancin Kaduna.

Taron ya samar da wani dandali na mu’amala da masu ruwa da tsaki domin bayyana damuwarsu a fili game da al’amuran da s**a shafi al’ummarsu. MS Ustaz ya amsa a madadin Gwamnati, yana ba da cikakkun bayanai kan tsare-tsare da ayyukan da mutane ke aiwatarwa.

An kammala ziyarar Kafanchan da Ziyartar mai Martaba Sarkin Jama’a, Alhaji Muhammadu Isa Muhammadu domin neman Tabbarraki.

Za a ci gaba da gudanar da wadannan ayyuka a fadin jihar Kaduna domin tabbatar da ingantaccen tsarin amsa tambayoyi da kuma ci gaba da huldar jama’a a matsayin babban ginshiki a Gwamnatin Sanata Uba Sani.

Dauka Nauyi Babban Mataimaki na Musamman kan Hulda da Jama'a na Gwamnan Jihar Kaduna Mal Uba Sani,M S Ustaz Mesittin

Please like Northern Mirror Hausa

Ina Taya Mai Alfarma Sarkin Musulmi Murna A yayin bikin cikarsa Shekara 68 Masu Albarka Alh Zaharaddeen Aminu Abubakar D...
24/08/2024

Ina Taya Mai Alfarma Sarkin Musulmi Murna A yayin bikin cikarsa Shekara 68 Masu Albarka

Alh Zaharaddeen Aminu Abubakar Dujiman Giade Ya mika sakon murnar ƙarin Shekara Zuwa Ga Mai Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar, CFR,mni

Shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA) da Kungiyar Jama'atul Nasril Islam (JNI), Shine Shugaban Kungiyar hadin kan addinai ta Najeriya. NIREC) Kuma Shugaban majalisar sarakunan gargajiya ta kasa.

Muna godiya ga Allah da ya bamu kai a matsayin jagora, wanda ke tsayawa tsayin daka don kare addinin Musulunci da kuma ciyar da al’umma gaba. Ka kasance ginshiki mai ƙarfi, wanda ya yi tasiri sosai a rayuwar Musulmai a Najeriya. Muna godiya Mara Adadi da sadaukarwa da jajircewarka wajen haɗa kai da fahimtar juna a tsakanin Musulmai da ma sauran al’ummomi.

Ya bayyana cewa "Wannan rana mai cike da farin ciki da shekara mai cike da albarka. Allah Ta'ala Ya karawa Mai Alfarma Shekaru masu yawa Ya cigaba da hidima Ga al'umma ba tare da nuna Gajiyawa ba.

Bugu da ƙari Dujiman Giade Ya bayyana Mai Alfarma Sarkin Musulmi a matsayin Dattijo mai tawali'u da jajircewa Wajen hidima ga al'umma yayi fatan Allah Yakara masa lafiya da nisan Kwana. A ƙoƙarin da yake yi na hada Kawunan dukkan Musulmi baki ɗaya.

Alh Zaharaddeen Aminu Abubakar (Dujiman Giade)

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Tarayya ta dage fara bayar da lamuni na Naira biliyan 150 ga masana’antu Ƙanana da matsakaitan m...
18/08/2024

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Tarayya ta dage fara bayar da lamuni na Naira biliyan 150 ga masana’antu Ƙanana da matsakaitan masana’antu har zuwa watan Satumbar 2024 inda kowanne mutum zai karbi Naira 50,000

Ministan masana'antu, kasuwanci, da zuba jari, Dr Doris Uzoka-Anite, Ta tabbatar da hakan A yau Lahadi

Northern Mirror Hausa

Abin  Da Ya K**ata Ku Sani Kan  Ƙudirin Cire Kudin Harajin  Shigo Da Wasu Kayan Abinci A Najeriya 1. Hukumar Kwastam ta ...
15/08/2024

Abin Da Ya K**ata Ku Sani Kan Ƙudirin Cire Kudin Harajin Shigo Da Wasu Kayan Abinci A Najeriya

1. Hukumar Kwastam ta Najeriya ta yi amfani da umarnin shugaban kasa Bolo Ahmad Tinubu da nufin rage wahalhalun da 'yan Najeriya ke fuskanta sak**akon tsadar kayan masarufi, inda ta ke farin cikin sanar da Mai Girma Shugaban Tarayyar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ta hannun mai girma Ministan Kudi kuma Ministan Tattalin Arziki na Kasa, Olawale Edun wanda ya amince da dokar da ta bada damar cire haraji kan kayan abinci da ake kira Zero Percent Duty Rate (0%) da kuma keɓancewar ƙarin haraji wato VAT akan wasu zaɓaɓɓun kayan abinci.

1. Wannan manufar ta fara aiki daga ranar 15 ga watan Yulin 2024 kuma za ta ci gaba da aiki har zuwa ranar 31st ga Disamba 2024.

2. Wannan matakin na da nufin rage tsadar kayan abinci a kasuwannin Najeriya ta hanyar samar da kayayyakin masarufi mafi sauki ga ‘yan kasa, kuma shirin na zuwa ne a wani bangare na kokarin da gwamnati ke yi na magance kalubalen samar da abinci da kuma tabbatar da cewa kayan abinci na yau da kullun sun isa kuma sun wadaci ɗaukacin ‘yan Najeriya, kuma , yana da mahimmanci a jaddada cewa, duk da cewa wannan matakin na wucin gadi ne, yana da nufin magance matsalolin da ake ciki a halin yanzu, ba kuma zai lalata dabarun da aka dade ana yi don kare manoma na gida da kuma kare masu masana'antuumu na cikin gida.

3. Ya k**ata a lura cewa aiwatar da wannan manufa za ta mayar da hankali ne wajen magance gibin wadata kasa da abinci, ta hanyar shigo da kayan abinci na yau da kullun ba tare da biyan haraji ba, dole ne duk wanda zai amfana da damar ya zamana yana da kamfani Najeriya wanda kuma ya yi aiki na aƙalla shekaru biyar.

Dole ne ya zaman kamfani ne da ya ke bayar da bayanan al'amuransa na shekara-shekara da bayanan kuɗi da biyan haraji da wajibcin biyan albashi na shekara biyar da s**a gabata.

Kamfanonin da ke shigo da buhunan shinkafa, ko hatsi da s**a haɗarda dawa, ko gero suna buƙatar mallakar masana'antar niƙa wacce ke saraffa aƙalla tan 100 a kowace rana, tsawon shekaru huɗu, kuma suna da isasshen filin noma, haka suma masu shigo da masara, alk**a, ko wake dole ne su zama kamfanonin noma da masu mallakar isassun filayen noma ko kuma masana'antar niƙa ko kamfanin sarrafa amfanin gona tare da hanyar sadarwa don amfanin gona.

4. Kayayyakin abinci na yau da kullun da s**a cancanci janye kuɗin harajin sun haɗar da;

ISamfarerar Shinkafa,Dawa, Gero,Masa Masara,Alk**a da wake

5. Ma’aikatar Kudi ta Tarayya za ta ba hukumar Kwatsam jerin sunayen masu shigo da kaya da kuma adadin da aka amince da su don saukaka shigo da wadannan kayan abinci na yau da kullun bisa tsarin wannan manufa. Manufar tana buƙatar a sayar da aƙalla kashi 75% na abubuwan da aka shigo da su ta hanyar musayar kayayyaki da aka sani, tare da rubuta duk ma'amaloli da ajiya.

Kamfanoni dole ne su adana cikakkun bayanan duk ayyukan da ke da alaƙa da hakan, waɗanda gwamnati za ta iya nema don tabbatar da yarda da kuma bibiya, Idan kamfani ya kasa cika wajibcinsa a ƙarƙashin izinin shigo da kaya, zai rasa duk wata dama na cire harajin, kuma dole ne ya biya harajin VAT, da haraji, da kudaden da s**a shafi ayyukan shigo da kaya. Haka kuma wannan hukuncin ya shafi kamfanin da ya fitar da kayan da aka shigo da su ta wannan manufa, ko kuma yayi yunƙurinn sarrafa su a wajen Najeriya.

6. Hukumar Kwastam ta Najeriya karkashin jagorancin Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi MFR, ta jajirce wajen tallafa wa manufofin gwamnati don inganta samar da abinci da inganta tattalin arziki. Hukumar ta bukaci masu ruwa da tsaki da su ba da cikakken hadin kai wajen aiwatar da wannan shirin domin amfanin daukacin ‘yan Najeriya.

Sanarwar daga ABDULLAHI MAIWADA
Babban Sufeto na Kwastam, kana
Jami'in Hulda da Jama'a na ƙasa
Na Kwanturola Janar na Kwastam.

AID Multimedia Hausa

Ana Zargin Wasu 'Yan Sanda Sun Karɓi Kuɗi Ba Bisa Ƙa'aida Wajen Mai Kafar Yaɗa Labarai Ta Mikiya Hamisu Inuwa"Daga zuwa ...
14/08/2024

Ana Zargin Wasu 'Yan Sanda Sun Karɓi Kuɗi Ba Bisa Ƙa'aida Wajen Mai Kafar Yaɗa Labarai Ta Mikiya Hamisu Inuwa

"Daga zuwa beli, 'Yan Sanda sun tursasa Mai Kamfanin Yaɗa Labarai na Mikiya, Hamisu Inuwa bayar da kuɗu Naira dubu ɗari (N100,000.) domin fansan kansa daga 'yan sandan a birnin tarayya a Abuja.

Yanzu haka dai ana zargin wasu 'yan sandan Najeriya naci gaba da amfani da manhajar pos domin karban na goro a ofishin su duk da gargadin da babban Sufeton 'yan sandan Kayode Adeolu Egbetokun, ya sha yi masu, da kuma matakan da rundunar da ke ɗauka akan baragurbin da ta k**a da laifin, amma duk da haka wasu sun ci gaba yayin da s**a yi kunnen uwar shegu.

Hamisu Inuwa na zargin wasu 'yan sandan Najeriya kuma 'yan uwa biyu da karban na goro, lokacin da s**a k**a wani matashi mai suna Abubakar Umar s**a tsare shi a runduna ta 7 dake Abuja.

Abinda yafi bada mamaki shi ne karban kudin goro wajen dan jarida da yan sandan s**ayi bayan sunyi barazanar rikeshi saboda yaje belin dan uwansa, wanda shima an k**ashi ne saboda ana neman dan uwansa mai suna Faruq.

Bayan sun sallami dan Jaridar Hamisu Inuwa ne kuma washe gari s**a saki dan uwan nasa Abubakar bayan da ya tura masu zun zurutun kudi, naira dubu dari biyar (N500,000).

Bayan samun kwafin wannan koke da lauya mai zaman kansa M. D. Abubakar ya rubuta, Editan kafar yaɗa labarai ta Karamchi ya tuntubi wadanda zargin ya shafa inda s**a nemi a tura masu koken, amma bayan tura masu basu kara amsa wayar ba.

Wannan labari yau kwana 8 kenan ana sauraren martanin 'yan sandan amma dai shiru kake ji k**ar an shuka dusa.

Abin jira a gani yanzu shi ne matakin da hukumar 'yan sandan zata dauka kan jami'an nata da ake zargi da karban cin hanci da rashawa tare da cin zarafin ’yan kasa ba bisa ka’ida ba.

Madogara: kafar yaɗa labarai ta Karamci.

Al'ummar garin Gadiya da ke Karamar hukumar gamawa suna bukatar daukin gaggawa saboda yadda ruwan kogi  yake ambaliya a ...
14/08/2024

Al'ummar garin Gadiya da ke Karamar hukumar gamawa suna bukatar daukin gaggawa saboda yadda ruwan kogi yake ambaliya a garin k**ar Yadda wani mazaunin garin mai suna Anas Abdullahi ya shaidawa majiyar mu cewa yanzu haka wasu suna fake acikin masallatai yayin da wasu suke cikin makarantu saboda yadda ruwan ya lalata musu gidajen su, suna neman daukin gwamnati cikin gaggawa
Sannan suna barar addu'ar al'umma akan Allah ya kawo musu mafita

TIRKASHI: Majalisar Wakilai Ta Bukaci Kotu Ta Ɗaure Duk Wanda A K**a Bai Iya Sabon Taken Nigeria Ba Na Tsawon Shekara Go...
14/08/2024

TIRKASHI: Majalisar Wakilai Ta Bukaci Kotu Ta Ɗaure Duk Wanda A K**a Bai Iya Sabon Taken Nigeria Ba Na Tsawon Shekara Goma Tare Da Biyan Kuɗin Tara Naira Miliyan Biyar

Ya kuke ganin wannan batun ?

Har Nasami Gurbin Karatun Medicine A BUK, Amma Na Watsar Na Koma Amurka Nayi Karatu Kuma Na Zama Makamin Firamare A Chai...
13/08/2024

Har Nasami Gurbin Karatun Medicine A BUK, Amma Na Watsar Na Koma Amurka Nayi Karatu Kuma Na Zama Makamin Firamare A Chaina, Dan Bello

Matashin nan ɗan asalin jihar Kano da a yanzu tauraronsa ke haskawa a kafar soshiyal midiya a Najeriya, Dan Bello Galadanci, ya shaida cewa a Najeriya ya taso, kuma har yayi karatun Remedial Sciences A tsohuwar jami'ar Bayero, wato BUK Old Side, har ya kai ga samun gurbin karatu wato admission a fannin medicine domin yayi karatun likita, amma yayi watsi da karatun bayan daga baya ya sami gurbin karatu a kasar Amurka.

Ɗan Bello ya ce akwai bambancin karatu a Amurka idan an kwatanta da Najeriya don haka yayi watsi da gurbin karatun likita da ya tafi Amurka yayi karatu inda daga bisani ya ce Chaina nan ma yayi, har ya kai ga zama Malamin firamare a kasar Chaina.

Me zaku ce game da wannan abu da Ɗan Bello yayi?

Wasu na ce wa A maimakon Ɗan Bello ya ci gaba da karatun likita, ya duba marasa lafiya a Najeriya, ya zabi ya zama malamin Firamare mai koyar da 'ya'yan 'yan Chaina.

Wasu kuma na cewa ai ko da ya zaɓi koyar wa a Chaina bai yi watsi da gida ba, domin yana da kishi, kuma yana yin Comedy inda ya ke wayar da miliyoyin 'yan Najeriya.

Me zaku ce?

YANZU-YANZU: Shugaba Bola Tinubu Ya Umarci Shugaban Riƙo Na Jam'iyyar APC Ganduje Da Ya Gaggauta Shirya Yadda Za'a Gudan...
13/08/2024

YANZU-YANZU: Shugaba Bola Tinubu Ya Umarci Shugaban Riƙo Na Jam'iyyar APC Ganduje Da Ya Gaggauta Shirya Yadda Za'a Gudanar Da Zaɓen Shugabancin Jam'iyyar Na Din-din-din

Me zaku ce?

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Address

London

Telephone

+2347067289098

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Whimsical graphics posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share