Mutanen Arewacin Nigeria Mazauna Nijar

Mutanen Arewacin Nigeria Mazauna Nijar Domin Hadin Kai, Jin Labaran Juna Da Kuma Yin Magana Da Murya Daya.

AN YI JANA'IZAR MUTANE 4 DA 'YAN BINDIGA S**A KASHE A ZARIAAnyi Jana'izar Mutum  Hudu Cikin Wanda Masu Garkuwa Da Mutane...
07/10/2023

AN YI JANA'IZAR MUTANE 4 DA 'YAN BINDIGA S**A KASHE A ZARIA

Anyi Jana'izar Mutum Hudu Cikin Wanda Masu Garkuwa Da Mutane S**a Harba A Zariya..

Damisalin karfe 10 na safiyar yau Asabar 7/10/2023 , aka gabatar da sallar jana'izar mutum hudu wanda Mahara (kidnappers) s**a kashe nan take a daren jiya juma'a , a Unguwan Dankali dake yankin Dan magaji a Zariya .

Kamar yadda labari ya tabbata yan ta'addan sun bayyana ne damisalin karfe 11 na dare , inda s**a mamaye gidan Alh Musa ( Dan haki) basu sameshi shi ba , s**a tafi da d'aya daga cikin matan shi , dasuran mata guda uku . sunyi ta barin wuta da bindigogi , sun harbi kusan mutum 9 , inda mutum 4 s**a rasu , mutum 5 kuma na Asibiti.

Dubban al umma ne s**a halartarci jana'izar cikin alhini da da damuwa . limamin Anguwan Malam Musa Tanko shine yajagoranci jana'izar.

Cikin taimakon Allah duka mata hudu da yan ta'adda s**a dauka Allah ya kubutar dasu.

Muna rokon Allah yajikan wanda s**a rasu , yabaiwa masu rauni lafiya sannan yayi mana Maganin wannan musiba 🤲.

✍️Aqil Abdulladir
7/10/2023.

07/10/2023

MURYAR MUTANEN AREWACIN NIGERIA MAZAUNA JAMHURIYAR NIGER

SHIMFIDA:

An samar da wannan 'page' ne domin kara samun hadin kai tsakanin Hausawa, mutanen arewacin Nigeria mazauna jamhuriyar Niger.

DALILIN BUDE WANNAN 'PAGE'

Duk da cewa mun san akwai hadaddiyar kungiyar 'yan Nigeria mazauna jamhuriyar Niger wato 'Association of Nigerian Citizen In Niger' (ANCN) da kuma wasu kungiyoyin na jihohi kamar kungiyar 'yan jihar Sokoto ko Kebbi ko Katsina ko kuma Zamfara da Kaduna da da Kano da sauran su. Duk da hakan sai muka ga dacewar samar da wannan shafi na facebook, wanda ta hanyar sa ne muke sa ran za a rika samun labaran halin da 'yan uwan mu ('yan arewacin Nigeria mazauna jamhuriyar Niger suke ciki). Saboda haka, muna iya cewa samar da wannan 'page' ba yana nufin mun kirkiri wata sabuwar kungiya bace. Sai dai muna fata wannan shafin ya habaka ya zama dalilin kara kawo cigaba a tsakanin al'ummar mu ta yadda ba a yi tsammani ba.

MANUFAR WANNAN AIKI:

Matsalar komabayan tallalin arziki da Nigeria ta samu kanta a ciki, ya sanya musamman mutanen arewacin Nigeria masu sana'o'in hannu daban-daban da kasuwanci iri-iri suke kwararowa zuwa birane da kauyakun jamhuriyar Niger. Bisa wadannan dalilan muka yi tunanin cewa wasu abubuwa na iya faruwa na farin ciki ko akasin haka da mutanen mu, wanda ya kamata a ce ana da wata kafa wacce za a rika jin labarin juna, musamman a wannan yanayi na dambarwar juyin mulki da ake ciki a jamhuriyar ta Niger. Sannan muna da hanyar jin duk wani abu da ya kamata a sanar da mutanenmu daga 'Nigerian Embassy' da ke Niamey, Niger da kuma daga hadaddiyar kungiyar 'yan Nigeria wato (ANCN).

Muna sa ran wannan 'page' zai taimaka sosai wajen karban sakonni da kuma isar da sakonnin kan halin da 'yan uwan namu 'yan arewacin Nigeria mazauna jamhuriyar din Niger suke ciki a wuraren da suke, idan bukatar hakan ta taso.

AYYUKAN DA WANNAN 'PAGES' ZAI RIKA YI:

(1) Kira zuwa ga sanin dokoki da kuma bin dokokin zama a jamhuriyar Niger.

(2) Kira zuwa ga muhimmancin Kyakkyawar mu'amala da abokan hulda.

(3) Kira zuwa ga muhimmancin gaskiya da rukon amana.

(4) Kira zuwa ga muhimmancin hadin kai tsakanin 'yan arewacin Nigeria mazauna jamhuriyar Niger.

(5) Kira zuwa ga magana da murya daya akan abinda ya shafe mu.

(6) Kira zuwa ga muhimmancin zumunci da hadin kai tsakanin 'yan arewacin Nigeria mazauna jamhuriyar Niger.

(7) Za mu rika yin sanarwoyin na aure, suna da kuma mutuwa da sanarwoyin tarukan da 'yan arewacin Nigeria mazauna jamhuriyar Niger din suke shiryawa, idan bukatar hakan ta taso.

(8) Wannan 'page' zai bukaci akalla mutum dai-dai 'yan arewacin Nigeria mazauna jamhuriyar Niger daga kowace jiha cikin jihohi takwas (8) na jamhuriyar Niger din, wadanda za su zama wakilan wannan 'page' kuma wakilai a cikin 'yan arewacin Nigeria da suke zaune tare da su a jihohin da suke, domin su rika samar mana da bayanan da muke bukata lokaci zuwa lokaci.

(9) Cikin 'yan arewacin Nigeria mazauna jamhuriyar Niger din, mai bukata na iya aiko mana hotunan aikin da yike yi ko kayan da yike siyarwa tare da lambar waya da kuma adireshin wajen da yike domin mu tallata masa a wannan 'page', domin ya samu abokan hulda a cikin mutanen arewacin Nigeria mazauna jamhuriyar Niger din da ma wadanda ba 'yan Nigeria din ba.

KA'IDOJIN MU A HALIN YANZU:

(1) A yanzu, ba mu da shirin tambayan kowa ko dala don yin wani aiki.

(2) Ba za mu wallafa wani abu ko wani labarin da ya fita wajen abubuwan da muka tsara tunda farko ba.

(3) Ba za mu yarda wani ya canza mana tsari ba.

Muna fata Allah ya sa mu fara wannan aiki a sa'a kuma da fatan wadanda muka tsara wannan abin domin su, za su bamu cikakkiyar hadin kai.

Mun gode!

Domin Karin Bayani:

Appél±22795862336/±22789134440
WhatsApp: ±2348033718219.

ASABAR/07/102023

https://www.facebook.com/profile.php?id=61552361421165

07/10/2023
'YAN NIGERIA MAZAUNA JAMHURIYAR NIGER SUN GUDANAR DA MAULUDIN MANZON ALLAH (S.A.W.A)Daga: Wakilan MuA ranar lahadi 16 ga...
07/10/2023

'YAN NIGERIA MAZAUNA JAMHURIYAR NIGER SUN GUDANAR DA MAULUDIN MANZON ALLAH (S.A.W.A)

Daga: Wakilan Mu

A ranar lahadi 16 ga watan Rabi'ul-Auwal 1445H dai-daita da 1/10/2023 ne 'yan Nigeria mazauna jamhuriyar Niger s**a shirya Mauludin Manzon Allah Muhammad (S.A.W.A) kamar yadda s**a saba yi a kowace shekara.

Taron ya samu halartar 'yan Nigeria da ke zaune a lungu da sako na garin Niamey da kewaye. Kamar yadda aka saba, bayan bude taro da addu'a da karatun al'kur'ani mai girma sai aka bada abin magana ga wani malami inda ya jima yina yi wa Manzon Allah da Ahlil-baiti (AS) kirari.

Khalifa Sheikh Sharif Muhammad Maky daga Zawiyar marigayi Sheikh Shu'aibu (RA) daga nan Niamey ne ya gabatar da jiwabi a wannan taro. Sheikh Maky, ya yi dogo kuma gamsashshe bayani a wannan wuri, inda a cikin yawabin nasa ya maida hankali kan kisshoshin da ke kara nuna girma da daraja irin na Manzon Allah (S.A.W.A). Ya kuma yi bayani a kan yadda mu'ujizar al''kur'ani da yadda ta zama gagara-badau a tarihin al'ummar Manzon Allah. daga karshe, ya kara da bayanai akan yadda Manzon Allah yake da tausayi ga kowa da kowa.

An fara gudanar da wannan taron ne da misalin karfe 9:00 na dare a layin 'La cruz' a anguwar Balafon da ke Niamey a jamhuriyar Niger. An fara wannan taro lafiya kuma an kammala taron lafiya.

Adresse

Pharmacie Soni, Balafon
Niamey
8003

Téléphone

+22789134440

Site Web

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Mutanen Arewacin Nigeria Mazauna Nijar publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager

Type