Dandalin damagarawa

Dandalin damagarawa Fasahar sadarwar zamani Domin yan'uwana su anfana da wannan DANDALIN DAMAGARAWA DOMIN FADAKARWA DA NISHADANTARWA DA KUMA KARANTARWA

Dakarun Isra'ila sun kashe Falasdinawa akalla 25 tare da jikkata fiye da 70 a yayin da suke neman agaji a yankin Rafah n...
19/07/2025

Dakarun Isra'ila sun kashe Falasdinawa akalla 25 tare da jikkata fiye da 70 a yayin da suke neman agaji a yankin Rafah na Gaza, a cewar kamfanin dillancin labarai na AA, wanda ya ambato wasu majiyoyi daga yankin Falasdinu

Firaministan Nijar Lamine Zaine ya damƙa wa tawagar ƙollon kafar ƙasar tuttar Nijar dan ƙarfafa ma su gwiwa a wasar CHAN...
18/07/2025

Firaministan Nijar Lamine Zaine ya damƙa wa tawagar ƙollon kafar ƙasar tuttar Nijar dan ƙarfafa ma su gwiwa a wasar CHAN 2024 da za su fafata da sauran takwarorinsu na kasashen Afirka.
Wasar dake a matsayin karo na 8 za'a fafata ne daga ranar 2 zuwa 30 ga watan Agustan 2025 a kenya ,Ouganda,da Tanzaniya in Allah ya so.

SHUGABAN KASAR NIGER YA GABATAR DA ZAMAN MAJALISAR MINISTOCI.Shugaban Ƙasa Janar Abdourahamane Tiani ya jagoranci zaman ...
18/07/2025

SHUGABAN KASAR NIGER YA GABATAR DA ZAMAN MAJALISAR MINISTOCI.

Shugaban Ƙasa Janar Abdourahamane Tiani ya jagoranci zaman Majalisar Ministoci a dakin taro na musamman da aka saba.

Majalisar Ministoci ta gudanar da zaman ta na yau a karkashin jagorancin Shugaban Ƙasa, Janar Abdourahamane Tiani. Taron ya mayar da hankali kan muhimman batutuwa na tsaro, ci gaban tattalin arziki, samar da ababen more rayuwa, da inganta ayyukan gwamnati.

Shugaban Ƙasa ya jaddada bukatar karfafa tsaro da yaki da cin hanci don tabbatar da zaman lafiya da cigaban kasa. Cikakken bayanin zaman zai fito daga fadar gwamnati a nan gaba.

Ƙarya ne mijina bai sakeni ba tabbas mun ɗan samu saɓani da maigida na amma saɓani ne irin na mata da mijina, amma ƙarya...
17/07/2025

Ƙarya ne mijina bai sakeni ba tabbas mun ɗan samu saɓani da maigida na amma saɓani ne irin na mata da mijina, amma ƙarya ake min wlh bai sakeni ba—Aisha Buhari

Uwar gidan marigayi tsohon shugaban Najeriya Muhammad Buhari, Aisha ta bayyana cewar rahotanni da aka shafe yinin yau ana yaɗawa a kafafen sada zumunta na cewa ita bazawa ce mijinta ya daɗe da sakinta ƙarya ne Aisha tace.

"Maƙiya na ne ke yaɗa wannan labarin kuma ƙarya suke kawai dai mun ɗan samu saɓani ne irin na mata da miji kuma tuni muka fahimci juna, saboda haka ni matarsa ce har Allah ya karɓi rayuwar sa, kuma don Allah ina kira ga mutane su barmu muji da abinda ke damun mu na rashin da muka yi" In ji ta kamar yadda ta bayyana a wani taron manema labaran data kira a daren nan.

A yinin yau ne dai wasu rahotanni s**a bayyana cewar Buhari ya sake ta kafin ya rasu kamar yadda fitaccen marubucin nan.

Farfesa Farooq Kperogi, ya bayyana cewa mutane suna yaɗa labaran cewa Buhari ya ba wa matarsa, A’isha wasiyya cewa idan ya mutu ta roƙa masa afuwar ƴan Najeriya a madadinsa, "amma dai, a abin da na sani, babu aure a tsakanin Buhari da A’isha. Sun rabu tun kafin ya rasu, kuma ta koma amfani da asalin sunanta na A’isha Halilu". Cewar Farook, kamar yadda DK-TV ta ruwaito.

Farfesa Kperogi, kuma ya ƙara da cewa duk da cewa bai san inda wancan labari na wasiyya ya samo asali ba, amma in jama’a sun kula ko a lokacin da Buhari ya koma Daura bayan ya bar mulki ba da A’isha ya koma ba. Sannan kuma shi kaɗai ya koma Kaduna daga Daura.

"Magana ta gaskiya, ko lokacin da ya kwanta rashin lafiya a Ingila an nemi ta je ta kula da shi amma ba ta amince ba saboda a lokacin ita ba matarsa ba ce. Duk da haka, ta je ƴan kwanaki kaɗan kafin ya mutu bayan an takura ta". In ji shi.

Faefesa Farook, ya kuma ƙara da cewa, ko a yanzu da ake cikin jimamin mutuwarsa, "za a fahimci ba ta taka wata rawa a matsayin matarsa ba". In ji shi.

Don Allah duk wanda yaga wannan labarin ya taimaka wajen tura shi zuwa sauran groups don a fitar da

Buhari ya saki matar sa kafin rasuwar sa, inji Farooq KperogiGa cikakken bayanin daya wallafa a shafin sa na FacebookFit...
16/07/2025

Buhari ya saki matar sa kafin rasuwar sa, inji Farooq Kperogi

Ga cikakken bayanin daya wallafa a shafin sa na Facebook

Fitaccen marubucin nan dake zaune ƙasar Amurka Farooq Kperogi, cikin wani sako daya wallafa a shafin sa na Facebook, ya bayyana cewa, ana ta yayata wata magana da ake cewa Aisha Buhari ce ta fada, inda akayi ikirarin cewa tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya roƙe ta da ta nemar masa afuwar ’yan Najeriya a madadinsa.

Ba zan iya tabbatar da sahihancin wannan ikirari ba, amma abin da nake da tabbaci akai shi ne, kafin rasuwar Buhari, babu aure a tsakanin sa da Aisha, saboda ya sake ta.

Aisha ma ta dawo amfani da sunanta na asali wato Aisha Halilu.

Idan ka lura da kyau, za ka fahimta cewa Aisha ba ta bi Buhari zuwa Daura ba bayan ya bar ofis. Haka kuma, lokacin da ya ƙaura zuwa Kaduna daga baya, shi kaɗai ya tafi.

A lokacin da ya fara rashin lafiya kuma aka ce Aisha ta je Landan don kula da shi, an ce ta yi jinkiri sosai saboda ba ta ƙara matsayin mata a gare shi. Sai daga baya, kwanaki kafin ya rasu, ta je — bayan matsin lamba sosai daga wasu mutane.

Har yanzu ma, a lokacin wannan juyayin, Aisha na cikin wani hali na rudani da rashin tabbas game da rawar da take takawa.

Don haka, abin tambaya da gaske shi ne, yaushe ne kuma a ina Buhari ya umarce ta da ta roƙi ’yan Najeriya su gafarta masa? Kuma a ina ne ma Aisha ta fadi hakan ?

Fitaccen marubucin nan dake zaune ƙasar Amurka Farooq Kperogi ya bayyana cewa Jama’a na ta yada wata magana da aka danganta ga Aisha Buhari, inda suke cewa Buhari ya nemi ta nemi gafarar ‘yan Najeriya a madadinsa.

Ba zan iya tabbatar da ingancin wannan ikirari ba, amma abin da na sani shi ne kafin rasuwar Buhari, shi da Aisha babu aure.

Sun rabu, Aisha ta koma sunanta Aisha Halilu.

Idan ka lura da kyau za ka ga Aisha ba ta je Daura ba a lokacin da ya yi ritaya zuwa garin bayan ya bar ofis. Shi ma Buhari shi kadai ne daga baya ya koma Kaduna.

Hasali ma lokacin da ya kamu da rashin lafiya aka ce Aisha tj

Ga fassarar maganar AKON daya taɓa yi; "Lokacin da na fara samun dala miliyan ɗaya daga waƙa, na yi matuƙar farin ciki h...
16/07/2025

Ga fassarar maganar AKON daya taɓa yi;

"Lokacin da na fara samun dala miliyan ɗaya daga waƙa, na yi matuƙar farin ciki har na kashe su da sauri. Abu na farko da na siya mai muhimmanci shi ne studio na kiɗa—na kusan dala $250,000 na kayan aiki—saboda na yi tunanin, ko da ba zan ci gaba da yin waka ba, zan iya rubutawa da shirya wa wasu.

Na ba wa mahaifiyata $150,000, mahaifina $150,000, sannan kowanne daga cikin ƴan uwana na ba su $25,000 don su fara kasuwancinsu.

Sai budurwata a wancan lokacin ta tambaye ni $200,000. Na yi dariya, na ba ta $5,000 kawai. Ina da wata ƙa’ida: ba zan taɓa ba wa mace fiye da kashi 2% na kuɗina ba. Dalilin haka yasa ta bar ni, amma ban damu ba—halayenta sun nuna min cewa kuɗina kawai take so, ba ni ba.

Darasi? Idan kana so ka zauna da kuɗi a matsayin namiji, dole ka yi taka-tsantsan—har ma ka zama mai kaucewa kashe wa mata kuɗi."

~Akon

Sakon Ta’aziyya daga Tsohon Shugaban Jamhuriyar Nijar, mahamadou issoufou Afirka ta yi babban rashiNa yi jimamin rasuwar...
16/07/2025

Sakon Ta’aziyya daga Tsohon Shugaban Jamhuriyar Nijar, mahamadou issoufou

Afirka ta yi babban rashi
Na yi jimamin rasuwar tsohon Shugaban Najeriya, Janar Muhammadu Buhari (mai ritaya), wanda ya bar tarihi mai ɗimbin daraja ga ƙasarsa da ma nahiyar Afirka baki ɗaya.

Na san Marigayi Shugaba Buhari tun a shekarar 1983 a Jos, lokacin da nake matsayin Daraktan Ma’adanai a Nijar, shi kuma ya kasance kwamandan soja a yankin. Muka hadu a wani taro na ƙasashen masu hakar ƙarfen tin. A lokacin ban taɓa zaton cewa wannan mutum mai kamun kai da gaskiya zai zama shugaban ƙasa ba. Kuma ban yi tsammanin cewa daga bisani, ni da shi za mu zama shugabanni a lokaci guda, mu kuma yi aiki tare wajen karfafa zumunci da haɗin gwiwa tsakanin Nijar da Najeriya.

Daga shekarar 2015 zuwa 2021, mun yi aiki kafada da kafada don ganin an gina layin dogo daga Kano zuwa Katsina har Maradi, da kuma bututun gas na Transsahara. Duk da matsalolin tsaro da s**a kawo jinkiri, mun dage don ganin an cimma manufofin hadin kai da ci gaba.

Na rasa aboki, Ina mika ta’aziyyata ta musamman ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ga Gwamnatin Najeriya, ga dangin Marigayi Buhari da kuma daukacin 'yan Najeriya.

Allah ya jikansa, ya gafarta masa, ya saka masa da Aljanna Firdausi.

Mahamadou Issoufou
Tsohon Shugaban Jamhuriyar Nijar

Wannan sabon takun saka ya taso ne a lokacin taron Majalisar Ministocin kasashen na UEMOA da ya gudana a birnin Dakar na...
15/07/2025

Wannan sabon takun saka ya taso ne a lokacin taron Majalisar Ministocin kasashen na UEMOA da ya gudana a birnin Dakar na Senegal.

Karin bayani na nan

Bayanai sun ce a Birni-N’Konni kawai an yi hasashen cewar akalla mutane 400 aka yiwa kisan kiyashi a rana guda, yayin da...
15/07/2025

Bayanai sun ce a Birni-N’Konni kawai an yi hasashen cewar akalla mutane 400 aka yiwa kisan kiyashi a rana guda, yayin da aka ƙona wasu kauyukan dake yankunan Tsibiri da Zinder da wasu al’ummomi, tare da rataye gawarwakin su a kofar shiga garuruwan. Wasu daga cikin waɗanda s**a tsira daga harin sun gudu zuwa cikin Najeriya inda s**a samu mafaka, kuma ba su koma kasar su ba.

Lokacin da hukumomin Faransa s**a tura Kanar Jean-Francois Klobb domin maye gurbin Voulet a watan Yuli na wannan shekarar, domin kawo karshen zubar da jinin da aka gani, Voulet ya bai wa sojojin da suke goyan bayan sa umarnin harbe Kanar Klobb.

A ƴan shekarun da s**a gabata, ƙasar Faransa ta fara tattaunawa akan abubuwan tarihin da s**a faru da ita, musaman ganin yadda ƙyamar da ake nuna mata ke ƙaruwa a nahiyar Afirka.

A shekarar 2021, shugaba Emmanuel Macron ya amince da kuskuren da kasarsa ta yi wajen kau da kai lokacin kisan kare dangin da aka yi a ƙasar Rwanda, yayin da shekara guda bayan haka, ƙasar ta kuma amince da kisan kiyashin da aka yiwa dubban fararen hula a Setif dake ƙasar Algeria.

A shekarar 2023, Ƙasar ta gabatar da neman afuwa a kan matakin da ta ɗauka na murkushe boren da aka yi a shekarar 1947 a Malagasy.

Karin Hotunan Yadda Aka Binne Gawar Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari A Gidansa Dake Daura, Jihar Katsina Yau Talata...
15/07/2025

Karin Hotunan Yadda Aka Binne Gawar Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari A Gidansa Dake Daura, Jihar Katsina Yau Talata

Allah Ya Jikansa Da Rahama!

Hotunan yadda aka sauke gawar marigayi, shugaba Muhammadu Buhari da kuma yadda shugaba Tinubu da iyalin marigayin s**a r...
15/07/2025

Hotunan yadda aka sauke gawar marigayi, shugaba Muhammadu Buhari da kuma yadda shugaba Tinubu da iyalin marigayin s**a raka shi zuwa motar da ta ɗauke shi domin kai shi garin Daura, inda za a binne shi a harabar gidan sa kamar yanda aka yanke hukunci 🥹🥹

Rayuwar Duka Kennan Fa Dole bawa yaji tsoron Allah shikenan an tafi fa har Abada Allah yagafarta masa yasa yahuta idan tamu tazo Allah yasa mucika da imani 🥹🥹

Allah kaji kan magabatan mu ya hayyu ya kayyum 🤲🏻🤲🏻🙏🏻🥹🥹

🟢⚪️ Manyan mutane da dama sun isa filin jirgin sama na Katsina (Nigeria), ciki har da tsohon shugaban kasa, Issoufou Mah...
15/07/2025

🟢⚪️ Manyan mutane da dama sun isa filin jirgin sama na Katsina (Nigeria), ciki har da tsohon shugaban kasa, Issoufou Mahamadou, domin raka marigayi shugaban kasar Najeriya.

Adresse

Zinder

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Dandalin damagarawa publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Contacter L'entreprise

Envoyer un message à Dandalin damagarawa:

Partager