Dandalin damagarawa

Dandalin damagarawa Fasahar sadarwar zamani Domin yan'uwana su anfana da wannan DANDALIN DAMAGARAWA DOMIN FADAKARWA DA NISHADANTARWA DA KUMA KARANTARWA

Labari Da Ɗumi Ɗumi:- Na janye ƙudirin kai hari Najeriya —TrumpAlhmdllh Alhmdllh
03/11/2025

Labari Da Ɗumi Ɗumi:- Na janye ƙudirin kai hari Najeriya —Trump

Alhmdllh Alhmdllh

Bayan an rantsar da ita a yau, Shugaba Samia Suluhu ta yi wa taron jama'a da ke cike da farin ciki a filin wasa na ƙasa ...
03/11/2025

Bayan an rantsar da ita a yau, Shugaba Samia Suluhu ta yi wa taron jama'a da ke cike da farin ciki a filin wasa na ƙasa da ke Dodoma godiya ta kuma gode wa 'yan ƙasar Tanzaniya saboda jajircewarsu da goyon bayan da s**a ba ta ga takararta. Zaɓen ya kasance cike da kura-kurai da zarge-zargen magudin zaɓe wanda aka hana babbar 'yar takarar adawa tsayawa takara.

A da ta kasance mace mai kwarin gwiwa a nahiyar Afirka; da kuma duniya, shugabar mata ta farko a ƙasar ta sauya salon shugabanci sosai ta hanyar tursasa 'yan adawa da kuma muryoyin da ke adawa da ita don ci gaba da mulki.

Daga Ibrahim Sani

Donald Trump ya kara jaddada barazanar cewa Amurka za ta iya tura sojoji Najeriya ko kuma ta kai hare-hare ta sama don d...
03/11/2025

Donald Trump ya kara jaddada barazanar cewa Amurka za ta iya tura sojoji Najeriya ko kuma ta kai hare-hare ta sama don dakatar da abin da ya kira kisan kiyashi da ake yi wa Kiristoci.

😭😭😭Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah Bayan shekaru 35 yau munyi sanadiyyar haɗa wannan bawan Allah da yan uwansa...
02/11/2025

😭😭😭

Alhamdulillah
Alhamdulillah
Alhamdulillah

Bayan shekaru 35 yau munyi sanadiyyar haɗa wannan bawan Allah da yan uwansa

Bayan sun cire tsammanin sake haɗuwa dashi 🥲

Allah sarki

Ya Allah kasa wannan aikin yazamo sanadiyyar tsira agaremu a ranar alƙiyama.

Ga yan uwansa nan, ɗansa da yayansa.

Alhamdulillah ansamu damar tattaunawa da wannan dattijonBayan anje gurinsa, da ƙyar aka samu damar tattaunawa dashiWanna...
01/11/2025

Alhamdulillah ansamu damar tattaunawa da wannan dattijon

Bayan anje gurinsa, da ƙyar aka samu damar tattaunawa dashi

Wannan bawan Allah sunansa (Sadisu Aliyu) daga ƙasar Niger 🇳🇪, garin Maraɗi, a unguwar Tasawa.

Ya share sama da shekaru (35) yana rayuwa a wani masallaci dake nan garin Ore, a ƙaramar hukumar mulkin Odigbo, Jahar Ondo, Nigeria.

Saboda haka muke neman yan uwa su yaɗa mana wannan rubutun ko Allah zai sa yan uwansa su samu wannan labarin
--------------------

Ina zargin k**ar anyi masa wani asiri ne da bayason komawa gida

Ko yanzu saida aka sha wahala sosai, da dabara, da ƙarya, daƙyar akasamu yayi bayanin garinsu da sunansa.

Alhassan Mai Lafia

A Jamhuriya Nijar ana fargabar fararan hula sama da 10 sun halaka sannan wasu gwammai sun jikkata a wani hari bisa kusku...
28/10/2025

A Jamhuriya Nijar ana fargabar fararan hula sama da 10 sun halaka sannan wasu gwammai sun jikkata a wani hari bisa kuskure da ake kyautata zaton jirgin sojin Nijar maras matuki ya kai a wani kauye de ke yankin Tillabery.

Sai dai rundunar sojin Nijar ta tabbatar wa da DW cewa ta kai harin amma a kan 'yan ta’adda inda ta ce ta halaka mayaka da dama.

Shugaba Alassane Ouattara wanda ke kan madafun ikon kasar mai arzikin koko tun a shekara 2011, yanzu haka yana da kaso 8...
27/10/2025

Shugaba Alassane Ouattara wanda ke kan madafun ikon kasar mai arzikin koko tun a shekara 2011, yanzu haka yana da kaso 89% na kuri'un da aka kirga.

Tun farko hukumar zaben kasar ta Cote d'Ivoire ta haramta wa manyan 'yan takara biyu shiga zaben.

DA DUMI-DUMI: Yanzu haka matasan kasar Kamaru sun fara zanga-zanga tare da toshe Tituna da kone-kone bayan an sanar da c...
27/10/2025

DA DUMI-DUMI: Yanzu haka matasan kasar Kamaru sun fara zanga-zanga tare da toshe Tituna da kone-kone bayan an sanar da cewa Paul Biya ya lashe zaben shugaban kasar.

DA DUMI-DUMI: Sak**akon zaben kasar Kamaru SOUTH REGION Biya - 90%Tchiroma - 6 % NORTHWEST REGION Biya: 86%Tchiroma: 5%C...
27/10/2025

DA DUMI-DUMI: Sak**akon zaben kasar Kamaru

SOUTH REGION
Biya - 90%
Tchiroma - 6 %

NORTHWEST REGION
Biya: 86%
Tchiroma: 5%

CENTER REGION
Biya gets 70%
Tchiroma get 21%

WEST REGION
Biya: 38.5 %
Tchiroma: 46%

NORTH REGION
Biya: 38%
Tchiroma: 43%

Adamawa Region:
Biya: 34%
Tchiroma: 50%

Jami‘an tsaro na barazanar k**a dan takarar adawa a Kamaru da ya ayyana kansa a matsayin zababben shugaban kasaIssa Tchi...
24/10/2025

Jami‘an tsaro na barazanar k**a dan takarar adawa a Kamaru da ya ayyana kansa a matsayin zababben shugaban kasa

Issa Tchiroma Bakary, dan adawar da ya fafata da shugaban Kamaru Paul Biya ya yi zargin cewa jami‘an tsaron kasar na barazanar k**a sa.

A shafinsa na Facebook, Tchiroma, ya gargadi gwamnatin Kamaru cewa yunkurin k**a shi na kara fusata mutanen Kamaru kuma hakan na kara jefa kasar cikin hatsari a mulkin shekaru 43 da Paul Biya yake yi a kasar, inda yanzu kuma yake neman tazarcen sabon wa‘adin shekaru bakwai.

Shugaban Mulkin Soji na Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traoré, ya ninka Albashin masana kimiyyar kasar zuwa ninki biyar.A...
23/10/2025

Shugaban Mulkin Soji na Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traoré, ya ninka Albashin masana kimiyyar kasar zuwa ninki biyar.

A cewar Traore anyi haka ne don karfafa bincike da fata ga Masana kimiyyar kasar, don gina kasa mai cike da Nasara a nan gaba.

“Ina so in taya dukan masana kimiyya, malamai masu bincike, masu ƙirƙira murna bisa kokarin da s**a riga s**a yi duk da matsalolin da suke fuskanta,” in ji Kyaftin Traoré a farkon jawabin nasa.

Adresse

Zinder

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Dandalin damagarawa publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Contacter L'entreprise

Envoyer un message à Dandalin damagarawa:

Partager