16/07/2025
Buhari ya saki matar sa kafin rasuwar sa, inji Farooq Kperogi
Ga cikakken bayanin daya wallafa a shafin sa na Facebook
Fitaccen marubucin nan dake zaune ƙasar Amurka Farooq Kperogi, cikin wani sako daya wallafa a shafin sa na Facebook, ya bayyana cewa, ana ta yayata wata magana da ake cewa Aisha Buhari ce ta fada, inda akayi ikirarin cewa tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya roƙe ta da ta nemar masa afuwar ’yan Najeriya a madadinsa.
Ba zan iya tabbatar da sahihancin wannan ikirari ba, amma abin da nake da tabbaci akai shi ne, kafin rasuwar Buhari, babu aure a tsakanin sa da Aisha, saboda ya sake ta.
Aisha ma ta dawo amfani da sunanta na asali wato Aisha Halilu.
Idan ka lura da kyau, za ka fahimta cewa Aisha ba ta bi Buhari zuwa Daura ba bayan ya bar ofis. Haka kuma, lokacin da ya ƙaura zuwa Kaduna daga baya, shi kaɗai ya tafi.
A lokacin da ya fara rashin lafiya kuma aka ce Aisha ta je Landan don kula da shi, an ce ta yi jinkiri sosai saboda ba ta ƙara matsayin mata a gare shi. Sai daga baya, kwanaki kafin ya rasu, ta je — bayan matsin lamba sosai daga wasu mutane.
Har yanzu ma, a lokacin wannan juyayin, Aisha na cikin wani hali na rudani da rashin tabbas game da rawar da take takawa.
Don haka, abin tambaya da gaske shi ne, yaushe ne kuma a ina Buhari ya umarce ta da ta roƙi ’yan Najeriya su gafarta masa? Kuma a ina ne ma Aisha ta fadi hakan ?
Fitaccen marubucin nan dake zaune ƙasar Amurka Farooq Kperogi ya bayyana cewa Jama’a na ta yada wata magana da aka danganta ga Aisha Buhari, inda suke cewa Buhari ya nemi ta nemi gafarar ‘yan Najeriya a madadinsa.
Ba zan iya tabbatar da ingancin wannan ikirari ba, amma abin da na sani shi ne kafin rasuwar Buhari, shi da Aisha babu aure.
Sun rabu, Aisha ta koma sunanta Aisha Halilu.
Idan ka lura da kyau za ka ga Aisha ba ta je Daura ba a lokacin da ya yi ritaya zuwa garin bayan ya bar ofis. Shi ma Buhari shi kadai ne daga baya ya koma Kaduna.
Hasali ma lokacin da ya kamu da rashin lafiya aka ce Aisha tj