Maiki Hausa Media

Maiki Hausa Media Muna tura muku ingantaccin labaran kasarmu ta najeriya Labaru da dumi dumin su

GODIYA TA MUSAMMAN GA MAI GIRMA SARKIN KOKO, KUNGIYAR CIGABAN YANKIN KOKO (KODA), DA CIYAMAN NA KOKO/BESSE AKAN DAWOWAR ...
07/11/2025

GODIYA TA MUSAMMAN GA MAI GIRMA SARKIN KOKO, KUNGIYAR CIGABAN YANKIN KOKO (KODA), DA CIYAMAN NA KOKO/BESSE AKAN DAWOWAR WUTAR LANTARKI (NEPA) A GARIN KOKO

Alhamdulillah! Bayan dogon lokaci da Garin Koko ke fama da matsalar rashin wutar lantarki (NEPA), cikin ikon Allah, wannan matsalar tazo karshe. A halin yanzu wutar lantarki ta dawo a wasu sassa na Garin Koko, yayin da ake ci gaba da gyare-gyare a sauran yankuna.

Wannan ci gaban mai matuƙar muhimmanci ya samu ne sakamakon jajircewa, kulawa, da sadaukarwa daga Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, tare da haɗin gwiwar Kungiyar Cigaban Garin Koko (KODA) da Shugaban Karamar Hukumar Koko/Besse, Hon. Sirajo Usman Koko.

Mai Girma Sarkin Koko, tare da shugabannin KODA da kuma Ciyaman na Karamar Hukumar, sun nuna kishin al’umma ta hanyar ba da goyon baya da tallafi wajen tabbatar da dawowar hasken wuta a Koko. Allah (SWT) Ya saka musu da alkhairi, Ya ƙara musu lafiya, nisan kwana, da nasarori masu albarka – Amin.

Wannan Nasarar ta Samu ne tun a ranar 14/10/2025, Mai Girma Sarkin Koko ya zauna da Kwamitin NEPA na Garin Koko domin tattauna matsalolin da s**a haifar da rashin wutar lantarki a yankin. Kwamitin ya bayyana cewa adadin kudin da ake buƙata domin gyaran wutar ya kai Naira Miliyan 2.5 (₦2,500,000).

Ba tare da ɓata lokaci ba, Mai Girma Sarkin Koko ya amince da bayar da cikakkiyar gudunmawar wannan adadi ta hannun Gidauniyar Sarkin Koko – Malam Musa Foundation. Wannan taimako mai dimbin albarka ya zama ginshiƙi wajen tabbatar da dawowar wutar lantarki ga daukacin al’ummar Masarautar Koko. Alhamdulillah, yanzu an samu dawowar hasken wuta a yankin Koko.

Wannan ba shi ne karo na farko da Mai Girma Sarkin Koko ke bayar da irin wannan gudunmawa ba. Tun a baya yana taka muhimmiyar rawa wajen gyaran da kuma kula da harkokin wutar NEPA a Garin Koko. Wannan ya nuna irin kishin sa, tausayi, da kulawarsa ga ci gaban al’ummar sa baki ɗaya.

Hakika, samun Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, a matsayin jagora babbar ni’ima ce daga Allah ga al’ummar Koko da kewaye. Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya saka masa da alkhairi, Ya ƙara masa lafiya, da kuma nasarori masu ɗorewa a dukkan al’amuransa.

Godiya ga Shuwagabannin KODA

Haka kuma, muna mika godiya ta musamman ga Kungiyar Cigaban Garin Koko (KODA) bisa jajircewa da haɗin kai wajen tabbatar da wannan ci gaba. Allah Ya saka musu da alkhairi, Ya ƙara musu jagoranci, fahimta, da haɗin kai a dukkan ayyukansu na alheri.

Daga:
Ciroman Koko Media Team
07/11/2025

30/10/2025

CIKA ALKAWALI: ANA GAB DA KAMMALA AIKIN MASALLACIN GARIN DAN DASHE CIKIN IKON ALLAH DAGA MAI GIRMA SARKIN KOKO.

Akwai wata babbar nasara da ta samu al'ummar Garin Dan Dashe, dake yankin Masarautar Koko, sakamakon cikar alkawalin Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II. Wannan nasara ita ce ta kammala aikin ginin Babban Masallacin garin, wanda al'ummar s**a fara gina shi.

Wannan gagarumin aiki ya samo asali ne daga wata ziyarar ban girma da Hakimin Garin Dan Dashe tare da Al'ummar garin s**a kaiwa Mai Girma Sarkin Koko, Alh. Mohammed Bello Koko II, a fadar sa mai daraja.

Babban makasudin ziyarar shine, g*i suwar bangirma da isar da korafin neman taimako ga Mai Girma Sarki don ya sanya hannu a kammala musu aikin wannan Masallacin da s**a fara gudanar da gininsa.

Mai Girma Sarkin Koko, Alh. Mohammed Bello Koko II, ya karɓi baƙuncin nasu cikin girmamawa da fara'a. Ba tare da ɓata lokaci ba, ya yi musu alkawalin cika burin su na kammala aikin ginin wannan Sabon Masallaci, wanda al'ummar Garin Dan Dashe s**a yi fatan a kammala musu shi.

✅Cikin ikon Allah (SWT) da kuma gagarumin ƙoƙari na Sarki, Mai Girma Sarkin Koko ya cika alkawalin da ya ɗaukarwa al'ummar Garin Dan Dashe. A halin yanzu, ana gab da kammala aikin ginin wannan babban Masallaci karkashin kulawar Gidauniyar Sarkin Koko Malam Musa Foundation. Wannan Masallaci zai zama wuri mai tsarki don bautar Allah da haɗa kan al'ummar garin Dan Dashe.

Hakika, samun Mai Girma Sarkin Koko, Alh. Mohammed Bello Koko II, a matsayin Sarkin Koko, wata babbar nasara ce da Allah (SWT) ya yiwa yankin Masarautar Koko baki ɗaya. Muna roƙon Allah (SWT) ya ƙara masa jagora, da kuma taimakon sa a dukkan al'amuransa. Amin.

Muna kuma roƙon Allah (SWT) ya ƙara taimakon Mai Girma Gwamnan Jahar Kebbi, Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu, bisa ga jajircewar sa wajen kawo manyan ci gaba a faɗin Jahar Kebbi. Amin.

Ciroman Koko Media Team
30/10/2025

ZIYARAR MAIGIRMA MINISTA, SEN. ABUBAKAR ATIKU BAGUDU, A GARIN KARZANNA, KARAMAR HUKUMAR BUNZAA yau, Maigirma Tsohon Gwam...
29/10/2025

ZIYARAR MAIGIRMA MINISTA, SEN. ABUBAKAR ATIKU BAGUDU, A GARIN KARZANNA, KARAMAR HUKUMAR BUNZA

A yau, Maigirma Tsohon Gwamnan Jihar Kebbi kuma Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arzikin Ƙasa, Sen. Abubakar Atiku Bagudu (Matawallen Gwandu), tare da Tsohon Gwamnan Jihar Kebbi Alhaji Sa’idu Usman Dakin Gari, da kuma wasu manyan jami’an gwamnatin jihar, sun kai ziyara zuwa Garin Karzanna, da ke cikin Karamar Hukumar Bunza.

Ziyarar ta kasance ne domin yin jajantawa ga al’ummar garin, a madadin Gwamnatin Jihar Kebbi, sakamakon rikicin da ya barke tsakanin manoma da makiyaya a yankin.

A yayin ziyarar, Maigirma Ministan da tawagarsa sun yi addu’a ga waɗanda s**a rasa rayukansu, tare da roƙon Allah ya jikansu da rahama, da kuma ya ba iyalansu hakuri da juriya.

Haka kuma, Maigirma Ministan ya bayyana jajircewar Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kebbi wajen kawo ƙarshen irin wannan rikice-rikice, tare da tabbatar da zaman lafiya, hadin kai, da ci gaban al’umma a duk faɗin jihar.

Allah ya kara taimakon Mai girma gwamnan jahar kebbi DR NASIR IDRIS KAURAN GWANDU da Mai girma Mininstan Kasafi Da Tsare Tsaren Tattalin Arziki Sen Abubakar Atiku Bagudu Amin, Allah ya kara yimusu jagora Amin.

Ciroman Koko Media Team
🗓️ 29/10/2025

22/10/2025

Kai Ne Zabin Kebbi, Kai Ne Alkiblar Kebbi!

🖐️ Hudu Sau Biyu Gwamnan Kebbi, Yatsa Biyu — Gwamnan Kebbi!
Kai ne dai Zabin Kebbi, kai ne Alkiblar Kebbi!

Mun yarda da kai Mai Mai Ta,
Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi,
Comrade Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu).

Allah Ya ƙara taimaka maka,
Ya ƙara maka nasara da jagoranci na gari.
Amin, Allah ya kara taimakon mai girma Ciroman Koko Alh Shehu Mohammed Bello Koko Amin, Allah ya kara yimai jagora Amin.

✍️ Ciroman Koko Media Team
📅 22/10/2025

Gwamna Nasir Idris (Kauran Gwandu) Ya Halarci Taron Northern Traditional Rulers Council (NTRC) General Assembly 2025Birn...
21/10/2025

Gwamna Nasir Idris (Kauran Gwandu) Ya Halarci Taron Northern Traditional Rulers Council (NTRC) General Assembly 2025

Birnin Kebbi, 2025, Kebbi State

Mai Girma Comrade Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), Gwamnan Jihar Kebbi, ya halarci taron Northern Traditional Rulers Council (NTRC) General Assembly 2025, wanda aka gudanar a dakin taro na musamman da ke Presidential Lodge, Birnin Kebbi.

Taron ya tattaro manyan shugabannin gargajiya daga jihohin Arewa, tare da jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki, domin tattauna muhimman matsaloli da kalubale da ke fuskantar yankin Arewa, tare da neman hanyoyin da za su kawo ci gaba mai ɗorewa da zaman lafiya.

A yayin taron, Gwamna Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu) ya nuna cikakken kudirinsa na yin aiki tare da majalisun gargajiya wajen inganta al’amuran tsaro, habaka ci gaba, da kuma ƙarfafa haɗin kai tsakanin gwamnati da al’umma.

Ya jaddada cewa, shugabannin gargajiya su ne tushen zaman lafiya da ci gaban al’umma, don haka gwamnatin sa za ta ci gaba da kula da su, girmama su, da haɗa kai da su wajen aiwatar da manufofin da za su amfanar da jama’ar Jihar Kebbi da ma Najeriya baki ɗaya.

Halartar Gwamna a wannan babban taro ya sake tabbatar da cewa Jihar Kebbi na tsakiyar tafiyar ci gaban Arewa, tare da rawar gani da Gwamna Idris ke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya, adalci da ci gaba mai ɗorewa.

Ciroman Koko Media Team
21/10/2025

KEBBI TA KAURA CE, KO BA KOSISI, KEBBI TA KAURA CE MUN MIKE YATSU BIYU.Gwamnatin Kauran Gwandu, Gwamnati ce wadda ta tab...
21/10/2025

KEBBI TA KAURA CE, KO BA KOSISI, KEBBI TA KAURA CE MUN MIKE YATSU BIYU.

Gwamnatin Kauran Gwandu, Gwamnati ce wadda ta tabbatar da kulawa da jama’a ta fannoni daban-daban kamar ilimi, lafiya, noma, da raya ƙauyuka, wanda hakan ke kawo ci gaba da sauƙin rayuwa ga al’umma.

Saboda haka, Mai girma Ciroman Koko Alh Shehu Mohammed Bello Koko Yana kara kira ga maza da mata na Jihar Kebbi su ci gaba da nuna goyon baya da haɗin kai ga wannan gwamnati mai albarka, domin a samu damar ci gaba da ayyukan alkhairi da walwalar jama’a.

A cikin wannan sako, Mai girma Ciroman Koko ya jaddada bukatar al’umma su kafa tubali na goyon baya ga Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu) a shekarar 2027, domin ya ci gaba da jagorantar jiharmu zuwa sabon matakin ci gaba da ingantacciyar rayuwa.

Mu tsaya tare da gaskiya, mu tsaya tare da ci gaba. Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu shi ne jagoran da ya cancanta da goyon bayanmu a karo na biyu.

Allah Ya kara masa ikon gudanar da mulki cikin adalci da nasara,
Allah Ya kara wa Mai Girma Ciroman Koko, Alh. Shehu Mohammed Bello Koko, jagoranci na gaskiya da albarka. Amin.

Ciroman Koko Media Team
21/10/2025

GODIYA TA MUSAMMAN GA MAI GIRMA SARKIN KOKO, AKAN WUTAR LANTARKI (NEPA) TA GARIN KOKO.Alhamdulillah! Bayan dogon lokaci ...
21/10/2025

GODIYA TA MUSAMMAN GA MAI GIRMA SARKIN KOKO, AKAN WUTAR LANTARKI (NEPA) TA GARIN KOKO.

Alhamdulillah! Bayan dogon lokaci da Garin Koko ke fama da matsalar rashin wutar lantarki (NEPA), yanzu an samu sauyi mai matukar kyau. Wannan babban ci gaba ya samu ne sakamakon kulawa da jajircewar Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, da hadin kan kungiyar cigaban Garin Koko (KOADA), da kuma Ciyaman na Karamar hukumar mulkin Koko/Besse.

Aikin gyaran ya yi nisa sosai, kuma kowane lokaci ana sa ran dawowar wutar lantarki a Garin Koko, duba da babbar gudummuwar da Mai Girma Sarki ya bayar ta naira miliyan 2,500,000 domin kammala aikin gyaran.

A ranar 14/10/2025, Mai Girma Sarkin Koko ya zauna da Kwamitin NEPA na Garin Koko domin tattauna matsalolin rashin wutar da ke addabar al’umma. Kwamitin ya bayyana cewa adadin kudin da ake bukata domin gyaran wutar ya kai Naira Miliyan 2,500,000.

Nan take, ba tare da bata lokaci ba, Mai Girma Sarkin Koko ya amince da bayar da cikakkiyar gudummuwar Naira Miliyan 2,500,000 ta hannun Gidauniyar Sarkin Koko – Malam Musa Foundation. Wannan tallafi mai dimbin yawa an bayar da shi ne domin tabbatar da dawowar wutar lantarki ga daukacin al’ummar yankin Masarautar Koko.

Wannan ba shi ne karon farko da Mai Girma Sarkin Koko yake bada irin wannan gudummuwa ba. Tun kafin wannan lokaci, ya sha taimakawa wajen gyaran wutar NEPA a Garin Koko. Wannan karamci da kuma gudummuwa sun nuna irin kishin sa, tausayin sa, da kuma kulawar sa ga ci gaban al’ummar sa baki daya.

Hakika, samun Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, a matsayin Sarkin Koko, babbar ni’imar Allah ce ga al’ummar Koko da kewaye. Muna rokon Allah Madaukakin Sarki Ya saka masa da alkhairi, Ya kara masa lafiya, nisan kwana, da nasarori masu albarka a dukkan al'amuransa.

Haka kuma, godiya ta musamman ga Kungiyar Cigaban Garin Koko (KOADA) bisa jajircewarsu da hadin kai wajen ganin cigaban garin Koko. Allah Ya saka musu da alkhairi, Ya kara musu jagoranci, da kuma hadin kai.

Daga
Ciroman Koko Media Team
21/10/2025

19/10/2025

SAKO DAGA MAI GIRMA CIROMAN KOKO, ALH. SHEHU MOHAMMED BELLO KOKO, ZUWA GA ƊUKKAN AL’UMMAR JIHAR KEBBI

Mai girma Ciroman Koko, Alhaji Shehu Mohammed Bello Koko, yana mika sakon godiya ga gwamnatin Jihar Kebbi bisa irin ayyukan alkhairi da take gudanarwa karkashin jagorancin Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi, Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu).

Ciroman Koko ya bayyana cewa, gwamnatin Kauran Gwandu ta tabbatar da kulawa da jama’a ta fannoni daban-daban kamar ilimi, lafiya, noma, da raya ƙauyuka, wanda hakan ke kawo ci gaba da sauƙin rayuwa ga al’umma.

Saboda haka, Ciroman Koko yana kira ga maza da mata na Jihar Kebbi su ci gaba da nuna goyon baya da haɗin kai ga wannan gwamnati mai albarka, domin a samu damar ci gaba da ayyukan alkhairi da walwalar jama’a.

A cikin wannan sako, Mai girma Ciroman Koko ya jaddada bukatar al’umma su kafa tubali na goyon baya ga Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu) a shekarar 2027, domin ya ci gaba da jagorantar jiharmu zuwa sabon matakin ci gaba da ingantacciyar rayuwa.

Mu tsaya tare da gaskiya, mu tsaya tare da ci gaba. Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu shi ne jagoran da ya cancanta da goyon bayanmu a karo na biyu.

Allah Ya kara masa ikon gudanar da mulki cikin adalci da nasara,
Allah Ya kara wa Mai Girma Ciroman Koko, Alh. Shehu Mohammed Bello Koko, jagoranci na gaskiya da albarka. Amin.

Ciroman Koko Media Team
18/10/2025

13/10/2025

Ziyarar Bangirma da Godiya, Chairman Na Matasan Koko, Alh. Bashar Idris Koko (Malam Bashar), Ya Kai Wa Mai girma Sarkin Koko Ziyara.

A wata ziyara ta musamman cike da girmamawa da godiya, Chairman na Matasan Koko, Alh. Bashar Idris Koko (wanda aka fi sani da Malam Bashar), tare da tawagarsa sun kai ziyarar bangirma ga Mai girma Sarkin Koko, Alh. Mohammed Bello Koko II.

Manufar wannan ziyara ita ce nuna godiya ta musamman da kuma jinjina ga Masarautar Koko bisa irin gagarumin kokarin da take yi wajen inganta rayuwar Al’ummar yankin Koko. Tawagar ta zayyana tare da yaba wa Mai girma Sarki kan dimbin ayyukan alheri da ci gaba da yake kawo wa Al’ummar Masarautar.

Jawabin Godiya Daga Bakin Alh. Ibrahim Mai Arewa Koko, Da yake gabatar da jawabin godiya a madadin Chairman na Matasan Koko, Alh. Bashar Idris Koko, ya isar da sakon taya murna da kuma godiya ga Mai girma Sarki kan jajircewarsa wajen tallafawa da kuma kawo ci gaba ga jama’a, Kamar yadda zakuji akan video.

Anashi jawabi Mai girma Sarkin Koko
Cikin fara’a da annashuwa, Mai girma Sarkin Koko, Alh. Mohammed Bello Koko II, ya nuna farin cikinsa da wannan ziyara ta Matasan Koko. Ya gode musu tare da yaba musu bisa wannan karramawa. Daga nan sai Mai girma Sarki ya yi jawabi mai muhimmanci da kuma jan kunne ga Matasan, kamar yadda za’a iya ji cikakke a faifan bidiyon da ke kunshe da wannan rahoto.

Tawagar Chairman na Matasan Koko ta Haɗa da:-
1. Alh Umaru Gona Koko
2. Alh Tukur Dan Lagos
3. Alh Yusuf Mai Wake
4. Alh Auwal Wankau
5. Alh Bashar Dan London
6. Alh Mustapha Koko
7. Alh Abu Garkuwan Arawa
8. Alh Abun Abu
9. Alh Mustapha Dan Sokoto
10. Alh Shehun Gona
11. Alh Labbo Mai Adda
12. Alh Bala Dan Fashi
13. Alh Bello Garkuwan Mahauta
14. Alh Habila
15. Alh Ibrahim Dakora
16. Alh Salisu Mai Kanti
17. Alh Buhari Mai Katifa
18. Alh Muktar Mai Kaza
19. Alh Hayatu Magayaki
20. Alh Muktar Shehu
21. Alh Abu Dan Bagudo
22. Alh Nasiru Adamu
23. Alh Abu Chairman Union
24. Alh Aliyu Gona
25. Alh Ibrahim Mai Arewa
26. Alh Bello Dangari
27. Alh Nasiru Ona
28. Alh Sule Bakason Mai Laudi
29. Alh Usman Labbaika
30. Alh Bello Dandare. Da dai Sauran Manyan Matasa.

Muna Addu'ar Allah (S.W.T) Ya kara taimakon Mai girma Sarkin Koko, Ya ba shi tsawon rai, lafiya da kuma basira wajen jagorantar Masarautar. Ameen.

Daga:
Masarautar Sarkin Koko
13/10/2025

Address

Abuja

Telephone

+2348027746672

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Maiki Hausa Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Maiki Hausa Media:

Share