Alyusaim Reporters Hausa

Alyusaim Reporters Hausa We make servicess for the peoples interm of business and politics etc.

Labari Da Ɗumi Ɗumi:Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya dakatar da kwamishinan sufurin jihar Hon Namadi, dakatarwar t...
02/08/2025

Labari Da Ɗumi Ɗumi:

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya dakatar da kwamishinan sufurin jihar Hon Namadi, dakatarwar ta fara aiki nan take.

Biyo bayan Hukumar DSS ta Gano Dala dubu Talatin $30,000 aka bawa Kwamishinan Sufurin jihar Kano domin Belin dilan muggan kwayoyi.

A wani rahoto da Jaridar Daily Nigerian ta wallafa na cewa Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, ya karɓi cin hancin dala 30,000 daga hannun dilan muggan kwayoyi -Sulaiman Danwawu domin ya tsaya masa, a cewar wani rahoto da hukumar tsaro ta farin kaya, SSS ta gabatar.

Mista Namadi, wanda ‘yan sanda s**a taba shelanta nemansa da laifin zamba, sannan kuma aka tuhume shi da aikata laifuka a shekarar 2013, Gwamna Abba Yusuf ya nada shi a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jihar Kano.

Majiyoyi a hedikwatar SSS da ke Abuja sun shaida wa wannan jarida cewa hukumar ta yi bincike a asirce kan badakalar karbar belin sannan ta kuma ba da shawarar korar kwamishinan ga gwamnan.

Rahoton ya ce an biya kwamishinan dala 30,000 kafin ya amince ya tsaya a matsayin wanda ya yi kaurin suna wajen safarar miyagun kwayoyi.

Bayan da jama’a s**a yi Allah-wadai da lamarin, gwamnan ya kafa kwamitin bincike don binciki badakalar badakalar da za ta tsaya masa tare da mika rahoto cikin mako guda.

Zargin Kisan tsohon Kwamishina, wata Babbar Kotu ta yanke wa Maigadi, da kuma Mai dafa Abinci Hukuncin Kisa a Jihar Kats...
30/07/2025

Zargin Kisan tsohon Kwamishina, wata Babbar Kotu ta yanke wa Maigadi, da kuma Mai dafa Abinci Hukuncin Kisa a Jihar Katsina.

Babbar Kotun Jihar Katsina ta yanke wa Mutanen biyu Mai Gadi, da kuma Mai Dafa abinci Hukuncin Kisa, akan zargin Kashe tsohon Kwamishinan Kimiyya da Fasaha na Jihar Alhaji Rabe Nasir.

Kamar yadda Jaridar Punch ta raiwaito, alkalin Babbar Kotun ta 9 mai Shari'a Ibrahim Mashi, ya sanar da Hukuncin Kisa ga Maigadin tsohon Kwamishinan, da kuma Mai Dafa masa abinci, akan zargin sanadiyyar Mutuwar Marigayin ta hanyar sanya masa guba.

Kazalika, Kotun ta sake yanke wa ɗaya daga cikin Masu gadin Marigayin Hukuncin zaman Gidan yari na tsawon Shekaru biyar, akan laifin rashin bayyana gaskiya game da kisan tsohon Kwamishinan Alhaji Rabe Nasir.

BA ZAMU YI SHIRU BA.BA ZAMU JANYE BA.ZAMU FADI GASKIYA.✊🏽  ✊🏽  ✊🏽
21/07/2025

BA ZAMU YI SHIRU BA.
BA ZAMU JANYE BA.
ZAMU FADI GASKIYA.

✊🏽
✊🏽
✊🏽

Tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ya samu wani muhimmin matsayi a duniya.Amurka, Faransa, Birtaniya, China, R...
19/07/2025

Tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ya samu wani muhimmin matsayi a duniya.

Amurka, Faransa, Birtaniya, China, Rasha da Majalisar Ɗinkin Duniya sun haɗu inda s**a naɗa Goodluck Jonathan a matsayin Jakadan Majalisar Ɗinkin Duniya a kawo sulhu na Rikice-Rikicen Duniya. Wannan matsayi ne wanda tsohon Firayim Ministan Birtaniya, Tony Blair, ya rike a baya a matsayin jakadan wanzar da zaman lafiya a gabas ta tsakiya na Majalisar Ɗinkin Duniya, Ƙungiyar Tarayyar Turai, Amurka da Rasha.

Goodluck Jonathan zai kafa tarihi a matsayin ɗan Afrika na farko da zai rike irin wannan matsayi a matsayin tsohon shugaban ƙasa da ya zama jakadan wanzar da zaman Lafiya a duniya, wanda ke nuna irin matsayin da ya samu a sahun gaba na shugabannin duniya.

Tarihin sa na cike da ban mamaki, daga malami a jami’a zuwa Kwamishina, daga nan ya zama Mataimakin Gwamna, sannan Gwamna, ya cigaba zuwa Mataimakin Shugaban Ƙasa, ya zama Shugaban Ƙasa na rikon kwarya, daga ƙarshe Shugaban Ƙasa. Yanzu kuma ya shiga sahun manyan shugabannin duniya.

Muna taya Mai Girma Goodluck murna da fatan alheri.

DA DUMI-DUMI: An fara hadawa fadar shugaban kasa Solar a Villa.
19/07/2025

DA DUMI-DUMI: An fara hadawa fadar shugaban kasa Solar a Villa.

Alhamdulillah Lissafin Fa Yana Fita Daidai, Malam Nasir El-Rufai da Hon Muhammad Bashir Saidu Kenan Yau a Kaduna a Shiry...
19/07/2025

Alhamdulillah Lissafin Fa Yana Fita Daidai, Malam Nasir El-Rufai da Hon Muhammad Bashir Saidu Kenan Yau a Kaduna a Shirye shiryen Sabuwar Tafiya dakuma shirin zaben cika gurbi.

Dokar taƙaita zirga-zirgan babura a jihar Gombe na cigaba da fuskantar s**a daga al'umma jihar, duk da nasarorin da jami...
18/07/2025

Dokar taƙaita zirga-zirgan babura a jihar Gombe na cigaba da fuskantar s**a daga al'umma jihar, duk da nasarorin da jami'an tsaro ke cewa sun samu sakamakon sanya ta.

Yayin da dokar ke shiga mako na shida a gobe Asabar, wasu mazauna jihar sun shaida mana cewa ta fara zama jiki, sai dai sun koka kan bazanar matsin tattalin arziƙi da dokar ta haifar.

Wani mazauna jihar, Hassan Isah, ya ce ƙarfin jama'a ya soma ƙarewa, musamman a wannan lokaci na damina da ake yawan samun ruwan sama saosai, da kuma rayuwar hanu baka hanu kwarya.

"Lokacin da zamu fita neman na abinci ruwan sama ya tsare mu a gida. Wannan ba abin da zamuyi Allah ne ya ƙaddara. Wani lokaci Ruwan yakan iya shafe sa'oi shida zuwa bakwai. Kuma ba ma wuce sa'oi shida a wajen neman abinci karfe bakwai ta doso," in ji shi.

Ya kuma yi ƙira ga mahukunta a jihar su duba yiwuwar sassauta wannan doka, domin kaucewa tabarbarewar tattalin arziƙin al'umma.

Masana sun yi gargaɗin cewa, talauci da yunwa na iya haifar da ƙaruwar barazanar taɓarɓarewar al'amuran tsaro, musamman a irin wannan yanayi na ƙunci da Najeriya ke ciki.

Gwamnatin jihar Gombe ta ce, ta yaba da ƙoƙarin jami'an tsaro, bisa irin ɗimbin nasarorin da ta ce sun samu, tun bayan sanya dokar ta taƙaita zirga-zirgan babura a jihar.

DA DUMI-DUMI: Sheikh Sani Yahaya Jingir Ya Janye Kalamansa Tare Da Bada Hakuri Kan Kalaman Da Ya Yi Wa Mataimakin Sa She...
18/07/2025

DA DUMI-DUMI: Sheikh Sani Yahaya Jingir Ya Janye Kalamansa Tare Da Bada Hakuri Kan Kalaman Da Ya Yi Wa Mataimakin Sa Sheikh Yusuf Sambo, Na Ziyarar Da Peter Obi Ya Kawo Mishi.

Daga Muhammad Kwairi Waziri.

Menene ke shirin Faruwq ne An Hangi AA Zahra a gidan gwamnati Harma sunui Sallar Juma'a Are da Gwamana' me kuka Fahimata...
18/07/2025

Menene ke shirin Faruwq ne An Hangi AA Zahra a gidan gwamnati Harma sunui Sallar Juma'a Are da Gwamana' me kuka Fahimata da hakan

Tawagar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ta isa filin jirgin sama na Malam Aminu Kano domin tarbar shugaban kasa Bola Ahma...
18/07/2025

Tawagar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ta isa filin jirgin sama na Malam Aminu Kano domin tarbar shugaban kasa Bola Ahmad Tunibu.

Bayan ziyarar jahar Kano, Katsina gwamnan jahar Bauchi Senator Bala Abdulkadir Mohammed Kauran Bauchi.Ya dawo gida jahar...
18/07/2025

Bayan ziyarar jahar Kano, Katsina gwamnan jahar Bauchi Senator Bala Abdulkadir Mohammed Kauran Bauchi.

Ya dawo gida jahar Bauchi bayan halartan Janazah tsohon shugaban kasar Nigeria Alh Muhammadu Buhari da kuma ziyarar iyalan Alhassan Dantata.

Allah Ya musu rahama 🙏

Za a gudanar da taron addu'o'i ga Buhari a masallacin ƙasa na Abuja.
18/07/2025

Za a gudanar da taron addu'o'i ga Buhari a masallacin ƙasa na Abuja.

Address

Hammadu Kafi Adjacent Izala Mosque
Abuja

Telephone

+2347034565777

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alyusaim Reporters Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Alyusaim Reporters Hausa:

Share