19/07/2025
Tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ya samu wani muhimmin matsayi a duniya.
Amurka, Faransa, Birtaniya, China, Rasha da Majalisar Ɗinkin Duniya sun haɗu inda s**a naɗa Goodluck Jonathan a matsayin Jakadan Majalisar Ɗinkin Duniya a kawo sulhu na Rikice-Rikicen Duniya. Wannan matsayi ne wanda tsohon Firayim Ministan Birtaniya, Tony Blair, ya rike a baya a matsayin jakadan wanzar da zaman lafiya a gabas ta tsakiya na Majalisar Ɗinkin Duniya, Ƙungiyar Tarayyar Turai, Amurka da Rasha.
Goodluck Jonathan zai kafa tarihi a matsayin ɗan Afrika na farko da zai rike irin wannan matsayi a matsayin tsohon shugaban ƙasa da ya zama jakadan wanzar da zaman Lafiya a duniya, wanda ke nuna irin matsayin da ya samu a sahun gaba na shugabannin duniya.
Tarihin sa na cike da ban mamaki, daga malami a jami’a zuwa Kwamishina, daga nan ya zama Mataimakin Gwamna, sannan Gwamna, ya cigaba zuwa Mataimakin Shugaban Ƙasa, ya zama Shugaban Ƙasa na rikon kwarya, daga ƙarshe Shugaban Ƙasa. Yanzu kuma ya shiga sahun manyan shugabannin duniya.
Muna taya Mai Girma Goodluck murna da fatan alheri.