News Daily Press

News Daily Press Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from News Daily Press, Media/News Company, Abuja, Abuja.

Kebbi fisherman wins Argungu festival with 59kg fish catch A 59 kilogram fish has emerged as the biggest catch at the 61...
15/02/2026

Kebbi fisherman wins Argungu festival with 59kg fish catch

A 59 kilogram fish has emerged as the biggest catch at the 61st edition of the Argungu International Fishing Festival, held in Argungu, Kebbi state.

Sunday Dare, special adviser on media and publicity to the president, announced the development in a tweet on Saturday.

The record catch was made by Abubakar Usman from Maiyama LGA during the main fishing competition at the Matan Fada River on Saturday.

More details in comment section.

SANARWAR DAURIN AURE:  Amadadin Iyalan Marigayi Malam Idris Maikayan Miya Kankara  Na Farin Cikin Gayyatar Al'umma Zuwa ...
27/07/2024

SANARWAR DAURIN AURE:
Amadadin Iyalan Marigayi Malam Idris Maikayan Miya Kankara Na Farin Cikin Gayyatar Al'umma Zuwa Daurin Auren Shugaban Jaridar Rana24 Wanda Za'ayi Kamar Haka 👇

RANA:9th, August -2024
LOKACI:2:30 Na Rana
WURI:Kofar Fada Kahutu Karamar Hukumar Danja Jihar Katsina

Dan-majilisar Dattawa Sen. Muntari Mohammed Dandutse Ya Gwagwaje Al'ummar Karamar Hukumar Kankara Da Kudade.Daga: Mannir...
21/03/2024

Dan-majilisar Dattawa Sen. Muntari Mohammed Dandutse Ya Gwagwaje Al'ummar Karamar Hukumar Kankara Da Kudade.

Daga: Mannir Idris Kankara

A yau Laraba Dan-majalisar Dattawa yankin Katsina ta kudu Sen. Muntari Mohammed Dandutse ya rabawa mutane 400 N10,000 a karamar hukumar kankara.

Hon. Abubakar Nuhu wanda shine jagoran wakilan da s**a gudanar da rabon kudaden wadanda s**a zo daga garin Funtua ya fara da bayyanawa Mutanen das**a amfana da sakon godiya daga Danmsjilisar ga Al'immar karamar hukumar ta kankara bisa nuna kauna da goyon bayan da suke nuna mashii.

Sannnan ya kuma tabbatar da akwai wasu ayyukan alheri dake tafe zuwa garin na kankara Wanda Sanatan yasamo daga tarayya daga bisani ya lissafawa al'umma yadda tsarin rabon kudin yake zuwa kaso 4.

Kason farko akwai Malamai 100, 50,50 daga Darika da Izala, Mata 100,Dattawa 100 sainkuma matasa 100 Wanda jimillar s**a kai 400 Inda kowa yasamu kunshin N10, 000 hannu da hannu.

Malam Hamisu Donawa na daya daga cikin kwamitin rabon ya bayyana sun kasa rabon shiyyoyi 11 na mazabun da karamar hukumar ta kunsa, wanda Hakan yasa mutanen wajen gari sun amfana matuka.

Daya daga cikin Malaman da s**a amfana Malam Abdulrashid ya yaba sosai da wannan tsari domin zai ragewa mutane radadin halin da ake ciki, shima Malam Isah ya godewa Danmajilisar gamida yin addu'a ta Kara samun cigaba.

Mata da Maza dama ne s**a kasance cikin farin ciki.

Nazir Isiya wanda shine mai taimakawa wajen biyan Malamai Addini ya yaba da halin dattakon da aka nuna.

Haka zalika shima Aliyu shehu dake bangaren biyan mata ya nuna godiya da yadda matan s**a nuna yayin tantacewa.

Sauran Yan kwamitin tafiyar da rabon kudin sun hada da Bature Omo, Shamsuddeen Magaji, Abdulbasir Maihoto, Danjuma Direba da Kuma Sadiq Pauwa.

Anyi rabon batare da samun Wani tarnakiba.

Gidauniyar Home Of Hospitality Development Initiatives(HOHDI) Takaiwa  'Yan Gudun Hijirar  'Yargoje Da Burdugau A Karama...
13/03/2024

Gidauniyar Home Of Hospitality Development Initiatives(HOHDI) Takaiwa 'Yan Gudun Hijirar 'Yargoje Da Burdugau A Karamar Hukumar Kankara Jihar Katsina.

✍️Mannir Idris Kankara

A ranar 13/3/2024 gidauniyar Home Of Hospitality Development Initiatives takaiwa al'ummar dake gudun hijira dake yankunan Yargoje da Burdugau tallafi.

Gidauniyar Home Of Hospitality Development Initiatives (HOHDI) gidauniya ce Mai zaman kanta wadda aka kafa domin tallafawa al'umma. dake bukatar tallafi ta bangarori daban daban k**ar samar da zaman lafiya,bangaren koyawa al'umma sana'o'i, domin dogaro dakai, samar da ilmi ga sl'umma da sauran al'amuran cigaban kasa.

Awannan karon Gidauniyar HOHDI ta tallafawa masu gudun hijiarar da Yan ta'adda s**a rabo da gidajensu ta hanyar harbi da kone mazuani hadi da yin garkuwa mazauna kauyukan yanki.

Malama Aisha Abdulrashid Kankara wadda itace , shuagabar (Team Leader) gidauniyar ta karamar hukumar kankara ta jagoranci mika wadannan kaya ga masu hijira ayau.

Yayin mika tallafin Malama Aisha Ta bayyana gidauniyar ta Samar da kayan abincin ne ga mutane 200 wadanda s**a kunshi Maza da mata inda aka dauki mutane 100 Ako wane yanki daGarin Kwaki Rabin kwano da Garin kuli kwata da kakke.

Shugabar ta bayyana gidauniyar tayi hakan ne saboda ganin irin halin da jama'a ke ciki na rashin cikkakken matsugunni.

Wasu daga cikin wadanda s**a amfana sun nuna godiyar su ga gidauniyar ga bisa talfafamasu da wannan kayan abinci .

Al'ummar sun kuma gode da hanyar da aka bi wurin raba masu a kai tsaye hannu zuwa hannu.

Cikin wadanda s**a gudanar da aikin rabon tallafin sun hada da Abdul Male,Hajiya Rayya Male, Malama Aisha Musa Shehu hadi da taimakon jami'an tsaron Katsina State Community Watch Corps domin bada tsaro.

Gidauniyar na sanar da al'umma kofa abude take ga masu dama da niyyar taimakawa ga Account Number 👇
1461211077
Access Bank

13/03/2024
Abin Da Ya Hana Ni Amsa Gayyatar EFCC — Sadiya FarouqTsohuwar ministar jin ƙai, Sadiya Umar Farouq ta bayar da uzurin ra...
05/01/2024

Abin Da Ya Hana Ni Amsa Gayyatar EFCC

— Sadiya Farouq

Tsohuwar ministar jin ƙai, Sadiya Umar Farouq ta bayar da uzurin rashin lafiya a matsayin dalilin da ya hana ta amsa gayyatar Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC).

Bayanai sun ce tsohuwar ministar, ta nemi EFCC ƙara mata lokaci kan gayyatar titsiye da za a yi mata bisa zargin ta da hannu a badaƙalar halasta kuɗin haram har naira biliyan 37.1.

Aminiya ta ruwaito cewa, Hukumar EFCC na zargin tsohuwar ministar da almundahanar kuɗin da s**a haura naira biliyan 37 tare da wani dan kwangila, James Okwete.

Sai dai kakakin hukumar ta EFCC, Dele Oyewale ya shaida wa Jaridar The Punch cewa, tsohuwar ministar ta aiko musu da lauyanta a matsayin wakili tare da neman karin lokaci domin amsa wannan gayyata, tana mai ba da uzuri na rashin lafiya da take damunta a yanzu.

Jami’an hukumar ta EFCC a jiya Laraba sun yi ta dakon tsohuwar ministar ta zamanin Shugaba Muhammadu Buhari a ofishinsu da ke Abuja, amma s**a shafe sa’o’i ba tare da ganin keyarta ba.

A farkon makon jiya ne, Sadiya Umar Farouq ta fitar da wata sanarwa, wadda a ciki ta musanta hannu a badaƙalar da ake zargi.

Ta kuma yi iƙirarin cewa kwata-kwata ma ba ta san ɗan kwangilar da rahotanni ke cewa hukumar EFCC ta k**a a binciken da take yi dangane da batun ba.

Aminiya ta ruwaito cewa a makon jiya ne hukumar ta aika wa tsohuwar ministar goron gayyata sak**akon wani bincike da ta ƙaddamar a kan aikace-aikacen ma’aikatarta lokacin da take riƙe da muƙamin tsawon shekara shida.

A makon nan ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Shugabar Hukumar Kula da Zuba Jari ta Kasa (NSIPA), Halima Shehu kan zargin almundahana.

Tinubu ya dakatar da ita ne a ranar Talata kan zargin aikata zamba a hukumar, inda ya maye gurbinta da Mista Akindele Egbuwalo a matsayin mukaddashi har zuwa lokacin da za a kammala bincike.

Tsaro:  An zargi 'Yan Banga da Karkatar da Shanun fulani a Mazoji, jahar Katsina. Zaharaddeen Ishaq Abubakar, @ Katsina ...
05/01/2024

Tsaro: An zargi 'Yan Banga da Karkatar da Shanun fulani a Mazoji, jahar Katsina.

Zaharaddeen Ishaq Abubakar, @ Katsina Times

Yayin da gwamnatin Katsina ke kokarin bambance fulanin kirki da kuma miyagu domin samar da zaman lafiya ingantacce. Ayyukan wasu yan banga a yankin mazoji karamar hukumar Matazu na kokarin mayar da hannun agogo baya a yankin.

Wasu fulani da jaridun Katsina times ta samu labarin su sunyi zargin wasu yan banga sun kore masu shanu a rafi wajen shan ruwa sun karkatar da wasu.

Fulanin da s**a tabbatar da gaskiyar su, s**a nufi wajen jami an tsaro domin su bayyana kansu ayi bincike na gaskiya a basu shanun su.
Fulanin sun bayyana cewa bayan jami an tsaro sun tabbatar da cewa lallai shanun su na gaskiya ne, sai s**a ce suje cikin shanun da aka tara su dauki nasu.

Daya daga cikin fulanin ya fada mana cewa, shanun shi talatin da uku aka kora amma shanun sa guda Goma sha shidda kawai ya gani a wajen sojoji, kuma an zabe masu koshin da lafiya, ba an gansu ba a wajen sojoji.

Wanda ya shaida ma jaridun Katsina Times yace sojoji sun tabbatar masa iya shanun da aka kawo masu kenan.

Karamar hukumar Matazu na Êaya daga cikin Øananan Hukumomi da ke Fama da Matsalar rashin tsaro a jihar Katsina. Sai dai 'wasu fulani na Matazu sun koka akan yanda wasu 'Yan banga suke keta musu haddi ba tare da tabbatar da kuma banbance masu laifi da marasa laifi ba.

Koken da Katsina Times ta samu da wasu gungun fulani a Mazoji a Karamar hukumar ta Matazu, sun zargi, 'Yan Banga da Kore masu shanu babu gaira babu Dalili.

Kamar yanda wani da ya bukaci mu sakaya sunansa ya bayyana mana, cewa 'Yan Banga sun zo har inda yake kiwon shanunsa sun kore masa shanu guda talatin da uku 33, da Tunkiya 27, yace "abin ya faru da yamma, a washe gari na biyo sawu daga mazoji zuwa Matazu, sai na tarar da shanu 16 a maimakon 33, babu guda 17, na iske shanun a wajen sojoji, saboda da s**a kora su daga nan can wajen sojoji s**a isa dasu, kuma ba namu kadai s**a kore ba hadda na 'yan

02/12/2023
 Sheikh Imrana Abdullahi Kankara (KADIMUL ISLAM) Ya Zama Sabon Limamin Madallacin Juma'a (JIBWIS) Na Garin Tashar Maje K...
02/12/2023


Sheikh Imrana Abdullahi Kankara (KADIMUL ISLAM) Ya Zama Sabon Limamin Madallacin Juma'a (JIBWIS) Na Garin Tashar Maje Kankara.

Daga : Mannir Idris Kankara

A jiya Juma'a ne 1/12/2023 aka bude sabon Masallacin Juma'ar garin Tashar Maje Dake Karamar Hukumar Kankara Jihar Katsina.

Kamar yadda majiyar Rana24 ta ruwaito wani bawan Allah ne Alhaji Mustapha Salisu Imam (KAIGAMAN SARKIN PAUWAN KATSINA) Ya dauki nauyin gina Masallacin agarin na tashar majen wanda keda nisan kimanin kilo mita 4 daga cikin garin Kankara.


Da ya ke Nasiha kafin ƙaddamar da sabbon Masallacin Malam Bishir Sh*tu yayi kira ga al'umma da mukasance masu kyyautaya niyya aduk Lokacin da zamu gudanar da wani aikin Ibada tsakanin da Allah, domin gujewa aikata aikin riya.

Bayan Kammala wannan hane, Limamin sabon Masallacin Sheik Imrana Abdullahi Kankara ta ta cigaba hudubar Juma'a, kuma yayi nasiha ga Musulmi da akoda yaushe mukasance musu yin amfani da damarmakin da muke samu wajen yin aiki nagari.

Sheikh Imrana ya Kuma kara da yiwa wanda ya gina Masallacin da 'yan kwamintin da s**a tsaya domin ganin tabbatuwar gina Masallacin yadda ya dace.

Bayan Kammala Sallah ne Ciroman Tudu Alhaji Sada Yakubu wanda shine Maigarin Tudu yayi jawabi amatsayin shi na mai gari, inda ya godewa Allah duba da yadda ake samun cigaban Addinin Musulunci cikin shekaru 10 da hawan bisa karagar sarautar Ciroman Tudu.

Kanwan Katsina Hakimin Ketare Alhaji Usman Bello Kankara mni wanda yasamu wakilcin Maigarin Hurya Malam Abubakar Idris Yusuf ya bayyana sakon farin cikin dacsa Alheri daga Kanwan Katsina,wanda yaso zuwa da kanshi amma wasu lamurra s**a sha kanshi.

Alhaji Kabir Sule daya daga Cikin jigajigan Kungiyar Jama'atul Izalatul Bidi'a Wa'inatul Sunna (JIBWIS) ayankin Karamar hukumar Kankara Yayi kira ga al'umma Wannan shiyya dasu kula da tsaftar wannan Masallaci yadda yak**ata.

Daya daga cikin 'yan uwan wanda yagina wannan Masallacin kuma Limamin sauran sallolin yauda kullum ya bayyana Alhaji Mustapha Salis

Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Malam Faruk Lawal Jobe Ya Halarci Hedikwatar Hukumar UNDP Ta Majalisar Dinkin Duniya Da...
17/11/2023

Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Malam Faruk Lawal Jobe Ya Halarci Hedikwatar Hukumar UNDP Ta Majalisar Dinkin Duniya Da ke Abuja.



Jaridar Rana24 ta ruwaito makasudun taron an yi shi ne kan Yanayi, Zaman Lafiya da Tsarin samar Tsaro don Rigakafin Rikici.

Shidai wannan muhimminTaron ana yinshine shekara-shekara domin nufin tuntuɓar masu ruwa da tsaki masu mahimmanci.

Dafatan abubuwan da Mataimakin Gwamnan Jahar Katsina s**a Tattaunawa ayayin taron zasu zamo mana masu amfanie ta Fannin inganta zaman lafiya tsaro a Jahar mu ta hanyoyin zamani don rigakafin rikice-rikice.

Ba Muda Niyyar Janye Jam’ianmu Daga Wasu Manyan Mutane A Nijeriya-IGPRundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce mukaddashin Suf...
10/11/2023

Ba Muda Niyyar Janye Jam’ianmu Daga Wasu Manyan Mutane A Nijeriya

-IGP

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce mukaddashin Sufeto Janar na ‘yan sandan kasar, Kayode Egbetokun, bai taba janye ‘yan sandan da ke da alaka da wasu muhimman mutane a kasar ba.

IGP Olukayode Egbotokun
Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Muyiwa Adejobi, ya fitar ta bayyana cewa IGP din ya janye jami’an rundunar ‘yan sanda na Monpol (PMF) ne kawai daga wasu muhimman mutane.

A cewar Adejobi, matakin janye ma’aikatan PMF daga aikin rakiya da gadi ya tsaya tsayin daka, kuma ba za a ja da baya kan wannan muhimmin sauyin aikin ba ba.

Koyaya, an sami wasu rashin fahimta game da umarnin IGP game da janye membobin PMF Unit daga VIPs.

Da farko dai, bari mu fayyace ko kadan rundunar ba ta yi niyyar janye jami’an ‘yan sanda daga tsarom manyan mutane a Nijeriya ba.

Yin haka, in ji shi, ba shi da aminci kuma ba shida wata faida.

Madadin haka, rundunar ta ci gaba da cewa manufar ita ce ta sake sanya ma’aikatan PMF da aka janye zuwa ga ƙungiyar ta musamman da aka kafa kwanan nan (SIS).

Address

Abuja
Abuja

Telephone

+2347032340606

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when News Daily Press posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to News Daily Press:

Share