B-Line Hausa

B-Line Hausa Media/News Company | Labarai, Addini, Al’adu, Nishaɗi da Tattaunawa

Sojojin da s**a yi juyin mulki a Guinea-Bissau Bissau sun naɗa Janar Horta Nta Na Man matsayin shugaban kasaKarin bayani...
27/11/2025

Sojojin da s**a yi juyin mulki a Guinea-Bissau Bissau sun naɗa Janar Horta Nta Na Man matsayin shugaban kasa

Karin bayani :

A ranar Alhamis, rundunar sojin Guinea-Bissau ta sanar da cewa an rantsar da Janar Horta Nta Na Man a matsayin sabon shugaban rikon kwarya, kwana guda bayan da s**a hambarar da gwamnatin kasar. A cewar sanarwar da sojin ƙasar s**a fitar, rantsuwar ta biyo bayan jawabin da hafsoshin rundunar s**a yi...

Sauya shekata zuwa APC daga PDP don amfanin mutanen jihar Taraba ne - Gwamna KefasKarin bayani:
23/11/2025

Sauya shekata zuwa APC daga PDP don amfanin mutanen jihar Taraba ne - Gwamna Kefas

Karin bayani:

Gwamnan Taraba, Agbu Kefas, ya ce shawarar da ya ɗauka na komawa jam’iyyar APC ta samo asali ne daga bukatar kare muradun mutanensa, ya bayyana haka ne a wani biki na raya al’adun kabilar Margi da aka yi a Jimeta, Jihar Adamawa a ranar Asabar. Kefas, wanda ya dage bikin shigarsa APC saboda sace...

Gwamnatin jihar Kaduna ta musanta zargin El-Rufa’i na biyan Naira biliyan 1 ga ’yan bindiga, tana cewa kalaman ba su da ...
23/11/2025

Gwamnatin jihar Kaduna ta musanta zargin El-Rufa’i na biyan Naira biliyan 1 ga ’yan bindiga, tana cewa kalaman ba su da tushe kuma barazana ce ga zaman lafiyar jiha

Karin bayani:

Gwamnatin jihar Kaduna ta musanta zargin da tsohon gwamna jihar, Nasir El-Rufa’i ya yi a Channels TV cewa gwamnatin Uba Sani ta biya ’yan bindiga Naira biliyan 1, tana mai cewa maganar ba ta da tushe b***e makama. Wannan na cikin sanarwar da ma’aikatar tsaro ta cikin gida ta fitar a ranar Laha...

Babu abin da ke tada mun hankali irin matsalolin tsaron da ya addabi Nijeriya - Shugaba TinubuKarin bayani:
23/11/2025

Babu abin da ke tada mun hankali irin matsalolin tsaron da ya addabi Nijeriya - Shugaba Tinubu

Karin bayani:

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ce matsalar tsaro ita ce babbar damuwar Nijeriya, musamman Arewacin ƙasar, yana mai cewa dole a hanzarta dawo da zaman lafiya da haɗin kai. Da yake magana a Kaduna ta bakin Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, a bikin cika shekara 25 na kungiyar tuntuba ta Ar...

21/11/2025

Kana iya danna waya har sa’o’i 4 yau… amma baka danna ko wata ƙofa ta cigaba ba.

👉 Progress doesn’t come by scrolling... it comes by starting.
Think. Act. Move. 🧠
B-Line Media Hub

20/11/2025

Amnesty International ta koka kan halin da jihar Katsina ke ciki kan batun tsaro

Karin bayani: https://is.gd/8frOy4

Wasu tsoffin 'yan majalisar dokokin jihar Kano da kuma masu ci a yanzu sun mara wa Barau Jibrin baya don neman tsayawa t...
19/11/2025

Wasu tsoffin 'yan majalisar dokokin jihar Kano da kuma masu ci a yanzu sun mara wa Barau Jibrin baya don neman tsayawa takarar gwamna a 2027

Karin bayani:

Wasu tsoffin ‘yan majalisar dokokin jihar Kano da kuma masu ci a yanzu sun mara wa mataimakin shugaban majalisar dattawan Nijeriya Barau Jibrin baya don tsayawa takarar gwamna a shekarar 2027.   Daily Trust ta ruwaito cewa kungiyar mutanen da adadinsu ya zarta 200, sun kai wa dan majalisar dattaw...

Majalisar dattawan Nijeriya ta bukaci shugaba Tinubu ya dauki matasa masu jini a jika dubu 100 aiki a rudunonin tsaro do...
18/11/2025

Majalisar dattawan Nijeriya ta bukaci shugaba Tinubu ya dauki matasa masu jini a jika dubu 100 aiki a rudunonin tsaro domin inganta tsaron kasar

Karin bayani:

Majalisar dattawan Nijeriya, ta nuna damuwa kan tabarbarewar tsaro a ƙasar, tana kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya amince da daukar matasa akalla 100,000 cikin rundunonin tsaro domin ƙarfafa tsaron ƙasar da ya yi rauni. Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, wannan matakin ya biyo bayan kudi...

Masu ibadar Umara 42 sun mutu bayan da motarsu ta yi taho-mu-gama da wata tankar mai a kusa da birnin Madina a kasar Sau...
17/11/2025

Masu ibadar Umara 42 sun mutu bayan da motarsu ta yi taho-mu-gama da wata tankar mai a kusa da birnin Madina a kasar Saudiyya.

Ƙarin bayani 👇

Allah Ya yi wa masu ibadar Umara 42 rasuwa bayan motarsu ta yi taho-mu-gama da wata tankar mai a kasar Saudiyya

Atiku da Kwankwaso ba za su taba haduwa a jam'iyya guda don aiki tare ba - Jigo a jam'iyyar APCKarin bayani :
16/11/2025

Atiku da Kwankwaso ba za su taba haduwa a jam'iyya guda don aiki tare ba - Jigo a jam'iyyar APC

Karin bayani :

Mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kudu maso gabashin Nijeriya Ijeoma Arodiogbu, ya ce rade-radin da ake yi cewa Atiku Abubakar da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na shirin yin kawance kafin zaben 2027 ba shi da tushe ballantana makama. Jaridar Punch ta rawaito Arodiogbu na cewa babu wata hanya da t...

Gwamnan Kano ya rattaba hannu kan bukatar samar da kwalejin Polytechnic a GayaKarin bayani :
15/11/2025

Gwamnan Kano ya rattaba hannu kan bukatar samar da kwalejin Polytechnic a Gaya

Karin bayani :

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan dokar kafa kwalejin kimiyya da fasaha “Gaya Polytechnic” a wani mataki na fadada damar samun ilimin gaba da sakandare tare da inganta koyon sana’o’in zamani a fadin jihar. Mai magana da yawun gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya bayyana haka...

Muna biyan ‘yan bindiga Naira miliyan 7 don zama a gidajenmu ko noma gonakinmu - Wasu al’ummomi a Neja
13/11/2025

Muna biyan ‘yan bindiga Naira miliyan 7 don zama a gidajenmu ko noma gonakinmu - Wasu al’ummomi a Neja

Wasu al’ummomi a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja sun bayyana cewa suna biyan haraji ga ‘yan bindiga domin su samu damar zama a garuruwansu ko kuma ci gaba da noma gonakinsu. A cewar shugaban al’ummar, Alhaji Yahaya, wanda ya bayyana haka yayin wata hira da shi a shirin Tsalle Daya na tas...

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when B-Line Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share