B-Line Hausa

B-Line Hausa Media & Awareness Platform
Muryar Matasa | Ilimi | Gaskiya
📍Arewa | 🌍 Africa
Don Gobe Mai Kyau Ga Matashi

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi, ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar Africa...
31/12/2025

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi, ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Obi ya bayyana hakan ne yayin wani taro da magoya bayansa a birnin Enugu, inda ya ce sabon matakin na daga cikin dabarun da za su ƙarfafa fafutukar samar da sahihin zaɓe a ƙasar.

A cewarsa, shi da magoya bayansa za su yi duk mai yiwuwa wajen hana maguɗi da murɗiyar zaɓe a babban zaɓen shekarar 2027, tare da jaddada aniyarsu ta kare ƙuri’ar jama’a.

Sauya sheƙar ta Peter Obi na zuwa ne a daidai lokacin da siyasar ƙasar ke ƙara ɗaukar zafi, yayin da jam’iyyu ke fara shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027.

Me Kuke Tunanin Gwamna Abba Zai Faɗa a Wannan Rana?
31/12/2025

Me Kuke Tunanin Gwamna Abba Zai Faɗa a Wannan Rana?

Shugaban mulkin soja na ƙasar Guinea, Mamady Doumbouya, ya samu nasara a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar, inda ya la...
31/12/2025

Shugaban mulkin soja na ƙasar Guinea, Mamady Doumbouya, ya samu nasara a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar, inda ya lashe zaɓen da kaso 86.72 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa.

Sakamakon, wanda hukumar zaɓen ƙasar ta sanar, ya nuna cewa Doumbouya ya samu rinjaye mai yawa a dukkanin yankunan ƙasar, lamarin da ya tabbatar da ci gaba da jagorancinsa a matsayin shugaban ƙasa bayan mulkin rikon ƙwarya.

Nasarar tasa ta zo ne bayan mulkin soja da ya fara tun bayan kifar da gwamnatin farar hula, wanda ya janyo muhawara daga cikin gida da ƙasashen waje kan makomar dimokuraɗiyya a Guinea.

Masu bibiyar al’amuran siyasa na ci gaba da sa ido kan matakan da sabon shugaban zai ɗauka, musamman wajen aiwatar da alkawuran sauyin mulki, gyaran tattalin arziki da dawo da cikakken tsarin dimokuraɗiyya a ƙasar.

Idan Har Wannan Abin Ya Tabbata Ina Makomar Sanata Barau Jibrin?
31/12/2025

Idan Har Wannan Abin Ya Tabbata Ina Makomar Sanata Barau Jibrin?

Sabuwar dokar harajin Najeriya da aka jima ana ce-ce-ku-ce a kanta, wadda wasu ke zargin an yi mata cushe, za ta fara ai...
30/12/2025

Sabuwar dokar harajin Najeriya da aka jima ana ce-ce-ku-ce a kanta, wadda wasu ke zargin an yi mata cushe, za ta fara aiki nan da kwana biyu, wato ranar Alhamis, 1 ga watan Janairun Sabuwar Shekarar 2026.

Dokar, wadda ta janyo muhawara mai zafi a tsakanin ’yan siyasa, masana tattalin arziki da ’yan kasuwa, na ɗaya daga cikin manyan gyare-gyaren haraji da gwamnatin tarayya ke shirin aiwatarwa domin sauya tsarin tara kuɗaɗen shiga a ƙasa.

Duk da ƙorafe-ƙorafen da aka yi cewa wasu sassa na dokar ba su bi ƙa’ida ba, gwamnatin tarayya ta dage cewa dokar za ta fara aiki kamar yadda aka tsara, tare da jaddada cewa manufarta ita ce sauƙaƙa wa ’yan ƙasa da ’yan kasuwa, ba wai ƙara musu nauyi ba.

Ana sa ran fara aiwatar da dokar zai ƙara tayar da muhawara, musamman daga ɓangarorin da ke ganin akwai buƙatar sake duba wasu tanade-tanaden ta kafin fara aiki.

Jam’iyyar APC a Jihar Kano ta bayyana shirinta na karɓar Gwamna Abba Kabir Yusuf cikin jam’iyyar, gabanin rade-radin sau...
30/12/2025

Jam’iyyar APC a Jihar Kano ta bayyana shirinta na karɓar Gwamna Abba Kabir Yusuf cikin jam’iyyar, gabanin rade-radin sauya sheƙarsa daga NNPP.

Shugaban APC na jihar, Prince Abdullahi Abbas, ya ce wannan kira na da nufin haɗin kai, sulhu da cigaban Kano, ba wai adawar siyasa ba. Ya tabbatar da cewa idan Abba ya shigo APC, za a karɓe shi da cikakken mutunci, tare da sauran jiga-jigan NNPP.

Ya ƙara da cewa APC ta buɗe ƙofa ga duk masu kishin kyakkyawan shugabanci da cigaba, kuma wannan mataki zai ƙarfafa zaman lafiya, dimokuraɗiyya da nasarar jam’iyyar a zaɓen 2027, tare da ƙara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ƙarfi a Kano.

A ƙarshe, Abbas ya jaddada ƙudirin APC na haɗin kai, tattaunawa da hidimar al’umma.

Masu bincike kan cutar koda a Jihar Yobe sun gano wasu ƙarafa masu nauyi a cikin ruwan sha da al’ummar Gashua ke amfani ...
30/12/2025

Masu bincike kan cutar koda a Jihar Yobe sun gano wasu ƙarafa masu nauyi a cikin ruwan sha da al’ummar Gashua ke amfani da shi, waɗanda ake zargin suna da alaƙa da yawaitar annobar cutar koda a yankin.

Jagoran binciken, Farfesa Mahmoud Maina, Darakta na Cibiyar Bincike da Horaswa ta BioRTC da ke Jami’ar Jihar Yobe, ya bayyana cewa an gano sinadarai irin su cadmium, gubar (lead) da arsenic, waɗanda ke iya haddasa cutar koda, da kuma wasu cututtuka masu tsanani kamar cancer da dementia.

A cewar rahoton binciken, ciwon s**ari da hawan jini na daga cikin manyan dalilan da ke haddasa cutar, inda aka fi samun yawaitar masu fama da ita a tsakanin masunta da ke zaune a yankin kogin Yobe.

Farfesa Maina ya ce masu binciken sun tattara samfurori sama da 3,000 na jini, fitsari, abinci, ƙasar noma, da ruwan kogi da rijiyoyi, tare da haɗin gwiwar masana kimiyya daga Najeriya da ƙasashen waje.

Ya ƙara da cewa ana sa ran fitar da cikakken rahoton binciken a watan Janairu 2026.

Haka kuma, cibiyar ta fara wani bincike na musamman kan cutar dementia domin rigakafi, inda aka tattara bayanai da samfurori daga mutane 1,200 da ke cikin haɗari.

Farfesa Maina ya yaba wa Gwamnatin Jihar Yobe bisa tallafin da take bai wa cibiyar, tare da kira ga gwamnati da masu hannu da shuni da su ƙara zuba jari a bincike da kirkire-kirkire, domin magance manyan matsalolin lafiyar al’umma.

Jam’iyyar NNPP reshen Jihar Kano ta sanar da korar shugabanta na jihar, Hashim Suleman Dungurawa, bisa zargin haddasa fi...
30/12/2025

Jam’iyyar NNPP reshen Jihar Kano ta sanar da korar shugabanta na jihar, Hashim Suleman Dungurawa, bisa zargin haddasa fitina da kuma raba kan ’ya’yan jam’iyyar a faɗin jihar.

Shugaban jam’iyyar NNPP na mazaɓar Gargarir da ke Ƙaramar Hukumar Dawan Tofa, Shu’aibu Hassan, ne ya tabbatar wa BBC Hausa da matakin da jam’iyyar ta ɗauka.

A cewarsa, an yanke shawarar korar Dungurawa ne bayan jerin zarge-zargen da ke nuna cewa ayyukansa sun janyo rikice-rikice da rashin jituwa a tsakanin mambobin jam’iyyar a matakin jiha da ƙananan hukumomi.

Shu’aibu Hassan ya ce jam’iyyar ba za ta lamunci duk wani abu da zai kawo barazana ga haɗin kai, zaman lafiya da tafiyar da jam’iyyar bisa doka da tsarin ta ba.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, Hashim Suleman Dungurawa bai ce komai ba dangane da zargin da aka yi masa ko matakin da jam’iyyar ta ɗauka a kansa.

Idan Har Abba Ya Tafi APC Me Makomar Sarautar Sunusi Lamiɗo Sunusi?
29/12/2025

Idan Har Abba Ya Tafi APC Me Makomar Sarautar Sunusi Lamiɗo Sunusi?

Motar Kungiyar ’Yan Jaridu ta Jihar Gombe (NUJ) ta yi mummunan hatsari a kan babbar hanyar Gombe zuwa Yola, lamarin da y...
29/12/2025

Motar Kungiyar ’Yan Jaridu ta Jihar Gombe (NUJ) ta yi mummunan hatsari a kan babbar hanyar Gombe zuwa Yola, lamarin da ya tayar da hankula tare da janyo fargabar rasa rayukan wasu daga cikin ’yan jaridun da ke cikin motar.

Rahotanni na farko sun nuna cewa hatsarin ya faru ne a yayin tafiya, inda wasu daga cikin fasinjojin motar s**a samu munanan raunuka, yayin da ake fargabar mutuwar wasu.

An garzaya da waɗanda s**a jikkata zuwa asibitoci mafi kusa domin samun kulawar gaggawa, yayin da hukumomi ke ci gaba da tattara bayanai domin gano musabbabin hatsarin da kuma tabbatar da adadin asarar rayuka.

Al’ummar jihar da abokan aikin jarida sun nuna alhini da jimami kan wannan iftila’i, tare da addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya jiƙan waɗanda s**a rasu, Ya kuma bai wa waɗanda s**a jikkata cikakkiyar lafiya.

Allah Ya kiyaye aukuwar irin wannan lamari a nan gaba.

29/12/2025

Matsayar Ƴan Jam'iyyar Nnpp Karamar Hukumar Dala, Kano State.

Shin Wani Irin Fata Kukeyi Gwamna Abba Kabir Yusuf.Ku Bayyana Ra'ayoyin Ku?
29/12/2025

Shin Wani Irin Fata Kukeyi Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Ku Bayyana Ra'ayoyin Ku?

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when B-Line Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share