Fursanul faidha Tv

Fursanul faidha Tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Fursanul faidha Tv, TV Network, Sultan Road, Abuja.
(1)

05/12/2025

Khudbar Juma'ah Kai Tsaye Daga Al'Irfan Juma'at Mosque II Dake Ibrahim Baqo Buhari Quaters, Tare Da Imam Junaidu Abubakar Bauchi 05/12/2025

Imam Junaidu Abubakar Bauchi
Aliyu Abubakar Baban Karatu
Al-Irfan Foundation For Islamic Da'awa

30/11/2025
Kabarin Mahaifiyar Annabi Muhammad (SAW), Sayyada Aminah bint Wahb dake a Al-Abwā’Masana tarihin Musulunci sun tabbatar ...
23/11/2025

Kabarin Mahaifiyar Annabi Muhammad (SAW), Sayyada Aminah bint Wahb dake a Al-Abwā’

Masana tarihin Musulunci sun tabbatar da cewa a wannan wuri mai albarka—Al-Abwā’—aka binne Sayyada Aminah bint Wahb, mahaifiyar Annabi Muhammad (SAW). Wurin yana tsakanin Makkah da Madinah, kuma yana daga cikin muhimman wuraren tarihi da s**a shafi rayuwar Annabi (SAW).

An rawaito cewa Annabi (SAW) ya ziyarci kabarin mahaifiyarsa fiye da sau ɗaya. Wasu ruwayoyi sun nuna cewa ya ziyarta a lokacin sulhun Hudaybiyyah, wasu kuma sun ce lokacin Fathu Makkah. Har ma wasu masana tarihin suna ƙiyasta cewa Annabi (SAW) ya kai ziyara zuwa Al-Abwā’ har sau takwas a rayuwarsa.

A wasu sahihan hadisai, an tabbatar da cewa Annabi (SAW) ya nemi izinin Ubangijinsa domin ya ziyarci kabarin mahaifiyarsa. Lokacin da ya isa wurin, ya tsaya a bakin kabarin, ya yi kuka, hakan ya sa sahabbai ma s**a yi kuka sosai saboda taushin zuciyar da s**a gani a gare shi.

Dr. Samir Barqah, masanin tarihi kuma mai bincike sananne a fannin alamu na tarihi da na Annabi (SAW) a Makkah da Madinah, ya tabbatar da cewa wannan wurin shine kabarin Sayyada Aminah bint Wahb, bisa bincike da hujjojin tarihi.

Allah Madaukaki ya sanya mu cikin Aljannatul Firdausi tare da Sayyada Aminah da Annabi Muhammad (SAW), ya kuma ba mu ikon kai ziyara ga wannan wuri mai albarka. Ameen.

Daga: Fityanu Islamic Centre
Rana: November 17, 2025

03/10/2025
03/10/2025

SALATUL FATIHI BA TA FI QUR'ANI BA A WAJEN 'YAN 'DARIQAR TIJJANIYYA

Falalar da ake fada ta Salatul Fatihi, ita ma tana cikin abinda yake sanya wasu hassada da kiyayyar wannan Salati. Falalar kuwa ita ce kamar haka:

A) Wanda ya karanta ta qafa daya, yana da ladan wanda ya yi wa Annabi Salati Dubu Shida (6,000).

B) Wanda ya karanta ta sau daya, yana da ladan wanda ya karanta Qur'ani sau 6, ga wanda ba ya tsayawa ga Umurnin Qur'ani.

C) Qafa 'daya nata ya yi daidai da tasbihin halittu.

D) Shehu Tijjani (R.A) ya ce, "Wanda Ya karanta ta sau daya, Allah Zai haramta jikinsa ga Wuta".

E) Shehu Tijjani (R.A) ya ce, "Wanda ya karanta ta sau daya, zai shiga Aljanna".

اللهم صل على سيدنا محمد الفاتح لما أغلق والخاتم لما سبق ناصر الحق بالحق والهادي إلى صراطك المستقيم وعلى آله حق قدره ومقداره العظيم

Mun sha jin wasu suna cewa, "Wannan Salati ya yi kyau da kuma tsari, amma falalarsa ce ba mu yarda da ita ba!"

Abin lura shi ne, akwai Izini na Musamman wanda sai da shi ne ake samun wannan falala da aka ambata, Allah kuma Mai ninka falala ne ga abinda Ya so! Allah Madaukaki Yana cewa:

مثل الذين ينفقون أموالهم في سبيل الله كمثل حبة أنبتت سبع سنابل في كل سنبلة مائة حبة والله يضاعف لمن يشآء والله واسع عليم

"MISALIN WADANDA SUKE CIYAR DA DUKIYOYINSU SABODA ALLAH, KAMAR MISALIN KWAYAR HATSI CE GUDA DAYA (DA AKA SHUKA) TA FITAR DA ZANGANNIYA BAKWAI, A CIKIN KOWACCE ZANGANNIYA AKWAI 'KWAYA 'DARI! KUMA ALLAH YANA NINNINKAWA GA WANDA YA SO, KUMA ALLAH MAYALWACI NE, MASANI!" (Suratul Baqarah: 261)

Annabi (SAW) Yana cewa:

إن الحسنات بعشر أمثالها إلى سبع مائة ضعف إلى أضعاف كثيرة

"KYAWAWAN AIKI, 'DAYA ALLAH YANA BADA GOMA MISALINTA, IZUWA NINKI 'DARI BAKWAI, ZUWA NINKIN-BA-NINKIN (DA YAWA)"

Kuma Annabi (SAW) Yana cewa:

إن لله عبادا ليسوا بأنبياء ولا شهداء، يغبطهم الأنبياء والشهداء لمكانهم من الله عز وجل

"ALLAH YANA DA WASU BAYI, SU BA ANNABAWA BA, KUMA BA SHAHIDAI BA, AMMA ANNABAWA DA SHAHIDAI SUNA BURIN INA MA SU NE SU, DON DARAJARSU A WAJEN ALLAH MADAUKAKI!"

Ka ga wadannan mutane da ba a fade su ba, ba su fi Annabawa da Shahidai ba, daraja ce kawai da Allah Ya ba su. Wannan shi ne abinda ake kira "Maziyya" da "Afdhaliyya". Watau kamar ruwa da turare, za ka iya sayen gwangwani ko kwalbar turare naira dubu, amma da wuya ka iya sayen gwangwanin ruwa a haka! Amma idan aka ce a yi alwala ba za ka yi da turare ba, da ruwa za ka yi. Ka ga ashe turaren bai fi ruwa daraja ba, watau Maziyya ba ta fi Afdhaliyya ba. Don haka Salatul Fatihi ba ta fi Qur'ani ba, falala ce da Allah Yake bayarwa ga abinda Ya so da wanda Ya so.

Shehu Tijjani (R.A) da muridansa gaba daya ba su da abinda ya fi Qur'ani, Salatul Fatihi kuma ba ta fi Qur'ani a wajensu ba. In dã ta fi shi, dã sai mu daina karatun Fatiha da Sura a cikin Sallah mu rinka karanta ta. Wannan kawai mummunar fahimta ce da aka yi wa 'yan Tijjaniyya.

Shehu Tijjani (R.A) ya haddace Qur'ani kyakkyawar haddacewa tun yana da shekara Bakwai da haihuwa, 'ya'yansa ma sun haddace, haka ma almajiransa. Shehu Ibrahim Inyass (R.A) shi da 'ya'yansa sama da Arba'in babu wanda bai haddace Qur'ani ba. Sannan a yau babu wata Dariqa ko Kungiya ta Musulunci da take da yawan mahaddatan Qur'ani sama da Tijjaniyya. Haba 'dan uwana! Dã 'yan Tijjaniyya suna da abinda ya fi Qur'ani ai dã Allah bai wanzar da haske da budi haka a cikinta ba. Falala ce kawai da Allah Yake bai wa abinda Ya so. Allah Madaukaki Yana cewa:

ذالك فضل الله يؤتيه من يشآء والله ذو الفضل العظيم

"WANNAN FALALAR ALLAH CE, YANA BADA ITA GA WANDA YA SO, KUMA UBANGIJI MAI FALALA NE MAI GIRMA!" (Suratul Jumu'ah: 4)

Malam Muhammadu Kani Gusau, Almajirin Marigayi Shehu Mai Hula, a cikin wani yabo da ya yi wa Shehu Tijjani (R.A) yana cewa:

Kash Munkiri nã Qarya..Kan Shehu Tijjani!

Cewa Salatul Fatihi.....Wai tã wuce Qur'ani

Qaryarku ce kuka shirya.....Ya munkiran Tijjani!

Don Shehu ya wuce wasa.....A cikin sanin Qur'ani

Wallahi duk ya fi ku.....Sirrin sanin Qur'ani!

Kuma sai ku nemi dalili.....A Hadisi ko Qur'ani

Uhhmm! Allah Ka bar mu a tafarkin su Shehu Ahmad Tijjani da Khalifansa Shehu Ibrahim Inyass da Almajiransu.

lamarin Shugaba Da Girma yake J@hili Shine Wanda Bai girman Shugaba baWanda Idan aka ambaci Shugaba Gani yake wani mutum...
30/09/2025

lamarin Shugaba Da Girma yake

J@hili Shine Wanda Bai girman Shugaba ba
Wanda Idan aka ambaci Shugaba Gani yake wani mutum ne Mai siffa Irin tasa
wannan cikakken J*hili kenan
Wanda Bai san matsayin Shugaba ba,

a cikin wani Littafin حقائق الأولياء Shafi na 37
ya kawo Bayanin IBN JAFARUL HIDDAD
(Wanda aka haifeshi Hijira tana 264 ta Rasu Hijira tana 345 kenan yayi Shekaru 81 a Duniya)
Daga Haihuwar wannan malamin Zuwa yau shekaru 1183 da s**a wuce

Ibn JAFARUL HIDDAD yace
wata Rana Naje Madina Sai da nayi kwana Goma Sha biyar (15 days) Ban samu abinci ba,

sai naje Inda Shugaba yake (wato Inda kabarinsa yake) Na zauna nayita salati
Bayan nayi salati sai nace Ya RASULULLAH Ka kosar da Bakon ka Domin Yunwa ta Raunana shi daga yima Allah Hidima (Yunwa tasa baya iya bauta ma Allah yadda yake so) Yace sai Bacci ya Rinjayeni

yace sai naga Manzon Allah a mafarki ya bani Buredi/Gurasa Na ci Sai na farka Daga bacci Na jini a koshe(wato na koshi saboda Abunda Annabi ya bani a mafarki na ci) Kuma ga Rabin Gurasar/Buredin a Hannuna.

Wannan Shine fa shine Shugaba
Wanda Idan Aka Jingina da shi
Allah Yana Biyan kowace Bukata

mutum ne yayi kwana 15 Bai samu abinci ba Amma da ya Jingina da Shugaba shikenan aka ciyar da shi a mafarki Kuma ya farka yaga Rabin abunda yaci a Hannunasa
Saboda Albarkacin Annabin Rahama

Ya Allah ka Kara masa Tsira da Aminci
Ya Allah ka sanya mu Cikin Masoyansa
SaLLaLLahu ALaihi Wassalam.

19/06/2025

Address

Sultan Road
Abuja
INYASS

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fursanul faidha Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fursanul faidha Tv:

Share

Category