10/06/2026
📍 JIHAR NEJA
Rundunar 'Yan Sandan Jihar Neja ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa an kai hari wasu makarantu a yankunan Bosso, Kpakungu, Sabon-Wuse da Lambata.
Mai magana da yawun rundunar, SP Wasiu Abiodun, ya bayyana cewa jami'an tsaro sun kai ziyara zuwa makarantun da aka ambata, kuma babu wata shaida da ke nuna cewa an kai wani hari.
Rundunar ta bukaci jama'a da su yi watsi da wannan jita-jita tare da tabbatar da sahihancin bayanai kafin yadawa domin kauce wa tayar da hankalin iyaye, dalibai da al'umma baki daya.
Haka kuma rundunar ta tabbatar da cewa an kara kaimi wajen tsaron makarantu domin tabbatar da lafiyar dalibai da ma'aikata.
⚠️ Mu rika tantance bayanai kafin yadawa.
💬 Mene ne ra'ayinku kan yadda ake yada labaran karya a kafafen sada zumunta? Ta yaya za mu rage wannan matsala?
Muryar Gaskiya