CNN Hausa Media

CNN Hausa Media Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from CNN Hausa Media, Media/News Company, Murtala Mohd Way, Maitama, Abuja.

Gwamnan jihar Neja Muhammad Umar Bago kenan a jiya Alhamis yayin da ya kai ziyarar ta'aziyya ga Mai Martaba Sarkin Zazza...
05/12/2025

Gwamnan jihar Neja Muhammad Umar Bago kenan a jiya Alhamis yayin da ya kai ziyarar ta'aziyya ga Mai Martaba Sarkin Zazzau Suleja Malam Muhammad Auwal Ibrahim bisa rashin matarsa Hajiya Rahama wadda ta rasu a ƙasar Masar (Egypt) a ƙarshen watan jiya.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Ƙwararren Likita, Dakta Kola Ya Rasu A Kaduna Allah Ya Yi Wa Dr. Kola Na Asibitin Alm...
04/12/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

Ƙwararren Likita, Dakta Kola Ya Rasu A Kaduna

Allah Ya Yi Wa Dr. Kola Na Asibitin Almansur Specialist Hospital Kaduna, Rasuwa Da Yammacin Yau Alhamis.

Za A Gudanar Jana'izarsa Gobe Juma'a, Bayan Kammala Sallar Juma'a A Masallacin Juma'a Dake Ibadan Street Kaduna.

Allah Ya Jikansa Da Rahama!

Daga Jamilu Dabawa

Bayan Shafe Sama Da Shekaru 60 A Legas, An Mayar Da Dattijo Wajen Danginsa A Jihar KanoA makon jiya ne wasu matasa s**a ...
04/12/2025

Bayan Shafe Sama Da Shekaru 60 A Legas, An Mayar Da Dattijo Wajen Danginsa A Jihar Kano

A makon jiya ne wasu matasa s**a mayar da wannan dattijo gida cikin danginsa a ƙauyen Birgi na ƙaramar hukumar Madobi dake jihar Kano, bayan ya shafe sama da shekaru 60 a Legas.

A rahotannin da muka samu dattijon ya bar gida ne tun yana matashi da ƙarfinsa, amma ya wayi gari ya tsufa kuma yana mararin komawa wajen 'yan uwansa.

Yau Shekara Ɗaya Da Rasuwar Shahararren Mawaƙin Siyasa, El-Mu’az Birniwa, A KadunaYau ake cika shekara ɗaya cif da rasuw...
04/12/2025

Yau Shekara Ɗaya Da Rasuwar Shahararren Mawaƙin Siyasa, El-Mu’az Birniwa, A Kaduna

Yau ake cika shekara ɗaya cif da rasuwar fitaccen mawaƙin siyasa, El-Mu’az Birniwa, wanda ya rasu a Kaduna a shekarar 2024.

El-Mu’az ya kasance ɗaya daga cikin fitattun mawakan da s**a yi fice wajen amfani da wakoki don faɗakarwa da tallata manufofin siyasa a Arewacin Najeriya.

Allah Ya jikansa da rahama, ya gafarta masa, ya sa Aljannah Firdaus ta kasance makomarsa.

Nnamdi Kanu ya Bukaci a Dauke shi Daga Sokoto a kaishi Gidan yarin Kuje Kotun Tarayya ta saka ranar 8 ga Disamba domin s...
04/12/2025

Nnamdi Kanu ya Bukaci a Dauke shi Daga Sokoto a kaishi Gidan yarin Kuje

Kotun Tarayya ta saka ranar 8 ga Disamba domin sauraron bukatar Kanu na a mayar da shi Abuja daga gidan gyaran hali na Sokoto

Kotun Tarayya da ke Abuja za ta saurari bukatar Nnamdi Kanu na neman a mayar da shi daga gidan gyaran hali na Sokoto a ranar 8 ga Disamba, domin ya samu damar shirya daukaka ƙarar da yake yi.

‎Dan Amanar Katsina Dr. Haruna Umar Maiwada ya kammala aikin Saka Fitulu masu Amfani da hasken rana (Solar Streetlight) ...
04/12/2025

‎Dan Amanar Katsina Dr. Haruna Umar Maiwada ya kammala aikin Saka Fitulu masu Amfani da hasken rana (Solar Streetlight) a bangaren daliban kwana (boarding schools) na makarantun ATC da WTC dake cikin birnin Katsina.

Ko Shakka babu ‎wannan aikin da Dan Amanar Katsina keyi na daya daga cikin dalilin da yasa ya assasa Gidauniyar Gidan Amana Movement domin cike giɓen ayyukan gwamnatin malam Dikko Umaru Radda na kokarin dayake wajen Samar da ingantaccen ilimi da tsaro ga Al'ummar Katsina.

‎Allah ya kara bashi ikon yin fiye da haka, ‎Allah yabamu lafiya da zaman lafiya a jihar mu ta Katsina dama Nijeriya baki daya.

Saƙon: Masoyan Ɗan Amana

Hotunan Yadda Gwamnan Jihar Zamfara Dakta Dauda Lawal Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin Naira Biliyan 861 Gaban Zauren Majalis...
04/12/2025

Hotunan Yadda Gwamnan Jihar Zamfara Dakta Dauda Lawal Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin Naira Biliyan 861 Gaban Zauren Majalisar Dokokin Jihar Na Shekarar 2026, Yau Alhamis

Cinkoson Ababen Hawa a Hanyar Gwagwalada-Abuja-LokojaAn samu cinkoso mai tsanani a yammacin yau Alhamis a hanyar Gwagwal...
04/12/2025

Cinkoson Ababen Hawa a Hanyar Gwagwalada-Abuja-Lokoja

An samu cinkoso mai tsanani a yammacin yau Alhamis a hanyar Gwagwalada-Abuja-Lokoja, sak**akon rufewar gada ta biyu da wani kamfanin gine-gine ya yi domin fara aikin maye gurbin gadar da sabbin karafan ƙarfe.

Rufewar gadar ta haddasa dogayen layukan motoci da jinkiri ga matafiya da direbobi.

Ana bai wa direbobi shawarar amfani da hanyoyi madadin inda ya dace, domin wannan matsala na iya ɗaukar lokaci kafin a warware ta.

SULHU DA 'YAN BINDIGA YA KARE A NIGERIASabon babban Ministan tsaron Nigeria General Christopher Musa yace batun sulhu da...
04/12/2025

SULHU DA 'YAN BINDIGA YA KARE A NIGERIA

Sabon babban Ministan tsaron Nigeria General Christopher Musa yace batun sulhu da tattaunawa da 'yan bindiga ya kare, haka batun biyan kudin fansa, ba zai sake faruwa ba a karkashin ikonsa

Haka naji Maimagana da yawun Shugaban Kasa Tinubu shima yana cewa Gwamnatin tarayya ta dakatar da duk wani tsari ko shiri na yin sulhu da tattaunawa da 'yan bindiga

Tunda masu iko da tsaron Nigeria sun janye batun sulhu to muma mun janye, muna tare da ra'ayin Gwamnati

Alamu na nuni da cewa za'a yi sukuwan doki akan kungiyoyin ta'addanci da suke cutar da Arewacin Nigeria musamman fulanin daji masu garkuwa da mutane

Ubangiji Allah Ka nuna mana karshen wannan masifa ba don halayen mu ba

RAHOTON TATTALIN ARZIKI A IMO:Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, attajirin Afrika Aliko Dangote, da gwamnonin ji...
04/12/2025

RAHOTON TATTALIN ARZIKI A IMO:
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, attajirin Afrika Aliko Dangote, da gwamnonin jihohin Ondo, Nasarawa, Edo, da tsoffin gwamnonin Zamfara (Sanata Abdulaziz Yari) da Kano (Dr. Abdullahi Ganduje) na daga cikin manyan bakin da s**a halarci taron tattalin arziƙin da jihar Imo ta shirya, wanda ke gudana a birnin Owerri.

Taron na da nufin jawo hannun jari, ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zaman kansu, da kuma gina dabarun farfaɗo da tattalin arzikin jihar da ƙasar baki ɗaya.

DA DUMI-DUMI: Bayan Kammala Aikin Masallacin Juma’a Da Islamiyya Dakta Dauda Kahutu Rarara (Sarkin Waka Kasar Hausa), Ya...
04/12/2025

DA DUMI-DUMI: Bayan Kammala Aikin Masallacin Juma’a Da Islamiyya Dakta Dauda Kahutu Rarara (Sarkin Waka Kasar Hausa), Ya Kaddarar Da Fara Aikin Manyan Tituna Guda Biyu Dake Cikin Mahaifarsa Garin Kahutu Dake Karamar Hukumar Danja Jihar Katsina.

Daga Mubarak Dabai Mataimaki na Musamman Ga Mawaki Dauda Kahutu Rarara

CNN HAUSA MEDIA ✍️✍️✍️✍️✍️✍️✍️

YANZU-YANZU: An Rantsar Da Janar Christopher Musa A Matsayin Sabon Babban Ministan Tsaron Nijeriya.Janar Christopher Mus...
04/12/2025

YANZU-YANZU: An Rantsar Da Janar Christopher Musa A Matsayin Sabon Babban Ministan Tsaron Nijeriya.

Janar Christopher Musa ya sha rantsuwar k**a aiki a matsayin sabon babban Ministan Tsaron Nijeriya a yau Alhamis 4 ga watan December shekarar 2025.

Address

Murtala Mohd Way, Maitama
Abuja
900001

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when CNN Hausa Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to CNN Hausa Media:

Share