Gombawa

Gombawa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Gombawa, Media/News Company, Maitama Abuja, Abuja.

Gombawa TV is a digital television platform that broadcasts a wide range of content, including news, entertainment, and cultural programs, with a focus on Northern Nigeria.

Abokin sana’ar shahararren mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara, Murtala Mamsa, ya yi zargin cewa wasu gwamnonin Najeriya ...
07/08/2026

Abokin sana’ar shahararren mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara, Murtala Mamsa, ya yi zargin cewa wasu gwamnonin Najeriya sun tara kuɗaɗe da motoci domin tallafa musu a lokacin mulkin marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, amma ya ce har yanzu ba su samu rabonsu ba.

Murtala Mamsa ya yi wannan zargin ne yayin da yake magana kan batun kuɗaɗen da ake cewa an tara domin taimaka musu, inda ya zargi Rarara da karɓa tare da riƙe waɗannan kadarori.

Ya kuma yi zargin cewa Rarara ya yi amfani da wani ɓangare na kuɗin wajen aurar da ’ya’yan marigayi Isyaku Forest.

“Gwamnoni sun tara mana kuɗaɗe da motoci domin a taimake mu a lokacin marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, amma Rarara ya ɗibe su ya danne. Kuma da kuɗin ne ya aurar da ’ya’yan marigayi Isyaku Forest.

“Yanzu tambayarmu ita ce: mu da muke raye, ba mu mutu ba, sai yaushe zai ba mu haƙƙinmu? Muna ba shi shawara ya sani cewa duk abin da ka tara, idan dai da haƙƙin wani ne, yana hana kwanciyar kabari,” in ji Murtala Mamsa.

Ya zuwa yanzu, ba a samu martanin Rarara kan waɗannan zarge-zargen ba. Wannan batu na iya ci gaba da haifar da muhawara tsakanin masu ruwa da tsaki a harkar waƙoƙin siyasa da magoya bayansu.

Majiya: Dokin Karfe Tv

Shahararren mawakin Najeriya, Davido, ya mayar wa tsohon hadimin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad, martani m...
07/08/2026

Shahararren mawakin Najeriya, Davido, ya mayar wa tsohon hadimin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad, martani mai zafi bayan Bashir ya yi masa tsokaci kan harkokin siyasa da nasarorin da ya samu.

Davido ya tuna wa Bashir Ahmad cewa duk da tsawon shekaru takwas da aka yi yana cikin mulkin Buhari, bai samu abin da ya taka-kai-da-murna da shi ba.

A cewar Davido, abin kunya ne yadda Bashir ya samu ƙuri'u 16 kacal lokacin da ya fito takarar siyasa a garinsu.

Bashir Ahmad, a nasa martanin, ya mayar wa Davido da tambaya kan harkar waƙa, inda ya ce:

“Gasar Grammy guda nawa ka taɓa lashewa a cikin biyar ɗin da aka ba ka damar tsayawa takara?”

Martanin nasu ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, yayin da mutane ke bayyana ra'ayoyi mabambanta kan nasarar da kowannensu ya samu a fannonin siyasa da nishaɗi.

Shugaban Ɗariƙar Tijjaniyya Na Duniya Ya Baiwa Tinubu Kyautar CarbiShugaban Ɗariƙar Tijjaniyya na Duniya ya baiwa Shugab...
07/08/2026

Shugaban Ɗariƙar Tijjaniyya Na Duniya Ya Baiwa Tinubu Kyautar Carbi

Shugaban Ɗariƙar Tijjaniyya na Duniya ya baiwa Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kyautar carbi a yayin wata ziyara da s**a gudanar.

An bayyana cewa kyautar carbin na daga cikin abubuwan da ke nuna girmamawa da ƙauna, musamman a al’adar mabiya Ɗariƙar Tijjaniyya.

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya karɓi rahoton kwamitin da aka kafa domin duba hanyoyin yin garambaw...
07/08/2026

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya karɓi rahoton kwamitin da aka kafa domin duba hanyoyin yin garambawul da farfaɗo da ilimin matakin farko da na fasaha a jihar.

Gwamnan ya bayyana rahoton a matsayin muhimmin tsari da zai taimaka wajen sauya fasalin harkokin ilimi tare da inganta koyo da koyarwa da kuma samar da matasa masu ƙwarewar da za su iya fuskantar buƙatun kasuwar aiki a nan gaba.

Yayin karɓar rahoton, Gwamna Inuwa Yahaya ya ce gwamnatinsa za ta fara nazarin shawarwarin da ke cikin rahoton nan take, tare da ɗaukar matakan aiwatar da su.

Ya ce, “Game da wannan rahoto, ina tabbatar muku cewa ba za mu yi watsi da shi ba. Za mu nazarce shi nan take sannan mu fara aiwatar da shawarwarin da ke cikinsa.”

Gwamnan ya kuma bayyana cewa tuni gwamnatinsa ta fara yin wasu manyan sauye-sauye a tsarin harkokin ilimi, ciki har da haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi zuwa ma’aikata guda.

A cewarsa, wannan mataki zai ƙara inganta haɗin gwiwa tsakanin sassa daban-daban na ilimi, da kuma sauƙaƙa aiwatar da manufofi da samar da ingantaccen aiki a fannin.

Gwamna Inuwa ya ce tun bayan hawansa mulki a shekarar 2019, gwamnatinsa ta fuskanci matsaloli da dama a fannin ilimi, amma ta samu nasarori ta fuskar gine-ginen makarantu, bunƙasa ƙwarewar malamai, ƙara yawan ɗalibai, faɗaɗa damar samun ilimi da kuma sauye-sauyen tsarin gudanarwa.

Ya sake jaddada alkawarin da ya ɗauka na cewa gwamnatinsa za ta bar Jihar Gombe cikin yanayi mafi kyau fiye da yadda ta same ta, musamman a ɓangaren ilimi.

“Mun san irin yanayin da muka tarar da wannan fanni lokacin da muka zo mulki a 2019. Muna godiya ga Allah cewa mun samu nasarori masu yawa. Ina sake jaddada alkawarin da na yi cewa za mu bar Gombe fiye da yadda muka same ta a ɓangaren ilimi,” in ji shi.

Da yake magana a madadin kwamitin, fitaccen masani kan harkokin ilimi kuma tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Tom Mataimaki Maiyashi, ya yabawa Gwamna Inuwa Yahaya bisa kafa kwamitin da kuma nuna kishin kawo sauyi a fannin ilimi.

Maiyashi ya ce rahoton ya kunshi cikakken bayani kan halin da ilimin matakin farko da na fasaha ke ciki a Gombe, tare da shawarwari masu amfani waɗanda za a iya aiwatar da su.

Ya bayyana cewa idan aka aiwatar da shawarwarin rahoton yadda ya kamata, hakan zai taimaka matuka wajen sauya tsarin ilimi na jihar tare da sanya Gombe cikin jihohin da ke kan gaba wajen samar da ingantaccen ilimi.

A nata bayanin, Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Gombe kuma shugabar kwamitin, Assoc. Prof. Aishatu Umar Maigari, ta ce an kafa kwamitin ne a watan Nuwamba 2025 domin yin cikakken nazari kan halin da ilimin matakin farko da na fasaha ke ciki a jihar.

Ta ce kwamitin ya duba batutuwan da s**a shafi ƙalubalen malamai, ƙarancin gine-ginen makarantu, tsarin gudanarwa, jin daɗin ɗalibai, yanayin koyon karatu, tsaro da kuma rawar al’umma wajen tallafawa harkokin makarantu.

A cewarta, sakamakon binciken ya zama tushen samar da shawarwari da aka tsara cikin manyan rukunan gyara guda takwas, waɗanda ke buƙatar kulawar gwamnati cikin gaggawa domin samun ci gaba mai ɗorewa a fannin ilimi.

Kwamishiniyar ta yaba da yadda Gwamna Inuwa Yahaya ya nuna ƙwarin gwiwa da kishin ilimi ta hanyar kafa kwamitin da ya ƙunshi ƙwararru da masana masu dogon tarihi a fannin.

Kwamitin ya ƙunshi manyan masana da masu tsara manufofin ilimi, ciki har da Assoc. Prof. Aishatu Umar Maigari, Dr. Nura A. Yakubu, OON, tsohon Babban Sakataren National Board for Technical Education (NBTE), Dr. Hamid Bobboyi, tsohon Babban Sakataren Universal Basic Education Commission (UBEC), Tom Mataimaki Maiyashi, Dr. Sadiq Gombe, Shugaban Hukumar SUBEB ta Jihar Gombe, da kuma Babban Sakataren dindindin na Special Services and Political, Government House, Gombe.

Rahoton ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin jihar ke ƙara mayar da hankali wajen sake fasalin tsarin ilimi domin inganta ingancin makarantu, malamai da kuma makomar ɗaliban Jihar Gombe.

Shahararren mawakin Najeriya, David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, ya yi gargadin cewa idan aka samu wata matsala...
07/08/2026

Shahararren mawakin Najeriya, David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, ya yi gargadin cewa idan aka samu wata matsala ko aka yi magudi a zaɓen gwamnan Jihar Osun mai zuwa, zai nemi shigar Shugaban Amurka, Donald Trump.

Davido ya bayyana hakan ne yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen zaɓen gwamnan Jihar Osun, inda ya jaddada buƙatar gudanar da zaɓe cikin gaskiya, adalci da kuma ba tare da tsoratarwa ko tashin hankali ba.

Mawakin ya kuma yi kira ga hukumomi da masu ruwa da tsaki da su tabbatar da cewa an gudanar da zaɓen cikin lumana, tare da mutunta ƙuri'ar al'umma.

Me za ku ce kan wannan gargadin na Davido?

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira ga maza masu hali da ikon ɗaukar nauyin iyali da su yi la’akari...
07/08/2026

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira ga maza masu hali da ikon ɗaukar nauyin iyali da su yi la’akari da ƙara aure, matuƙar za su iya yin adalci da sauke nauyin da addinin Musulunci ya ɗora musu.

Sarkin ya bayyana hakan ne a yau Juma’a yayin bikin ɗaura auren wasu zawarawa da ’yan mata da aka gudanar a Masallacin Gidan Sarki da ke Kano, ƙarƙashin shirin Gwamnatin Jihar Kano, inda Sarkin ya kasance Waliyin amaren.

A cewarsa, ƙarin aure ga wanda yake da hali kuma zai iya yin adalci na iya taimakawa wajen rage yawan zawarawa da ’yan matan da s**a kai shekarun aure amma ba su samu mazajen aure ba.

Ya kuma jaddada muhimmancin adalci da cika haƙƙin iyali, yana mai cewa wanda zai ƙara aure dole ne ya kasance yana da ikon ɗaukar nauyin matan da ’ya’yansa tare da kiyaye haƙƙoƙinsu.

Maganar ta sake buɗe muhawara kan matsalar yawaitar zawarawa da ’yan mata marasa aure a Arewacin Najeriya.

Me za ku ce kan wannan shawara ta Sarkin Kano?

Majiya: ATP Hausa

Wata matashiya ’yar asalin Jihar Gombe, Hajara Ibrahim, ta samu gagarumar nasara bayan da ta lashe Gasar Karatun Alƙur’a...
07/08/2026

Wata matashiya ’yar asalin Jihar Gombe, Hajara Ibrahim, ta samu gagarumar nasara bayan da ta lashe Gasar Karatun Alƙur’ani Mai Tsarki ta Ƙasa da Ƙasa da aka gudanar a ƙasar Jordan.

Nasarar Hajara ta ɗaga martabar Najeriya da Jihar Gombe a fagen karatun Alƙur’ani na duniya, lamarin da ya sa Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karrama ta tare da bai wa nasarar da ta samu muhimmanci.

A matsayin wani bangare na karramawar, Gwamnan ya ba ta kyaututtuka da tallafi da s**a haɗa da:

₦5,000,000 a matsayin kyauta.

Kujerar zuwa aikin Hajji.

Cikakken tallafin karatu daga matakin digiri na farko (Undergraduate) har zuwa Digirin Digirgir (PhD).

Wannan mataki na Gwamna Inuwa Yahaya ya jawo yabo daga al’umma, musamman masu sha’awar karatun Alƙur’ani, inda aka bayyana shi a matsayin abin ƙarfafa gwiwa ga matasa da ɗaliban da ke ƙoƙarin ganin sun yi fice a fannonin ilimi da addini.

Nasarar Hajara Ibrahim ta kuma zama wata dama ta nuna irin gudunmawar da matasa ’yan Najeriya ke bayarwa wajen ɗaga darajar ƙasar a gasa ta ƙasa da ƙasa.

Jarumin masana’antar Kannywood, Tahir Fagge, ya bayyana cewa ba zai sake tallata jam’iyyar All Progressives Congress (AP...
07/08/2026

Jarumin masana’antar Kannywood, Tahir Fagge, ya bayyana cewa ba zai sake tallata jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ba, yana mai cewa ba shi da wani abin kirki da zai nuna wa al’umma da gwamnatin jam’iyyar ta yi.

A cewar jarumin, “Ba zan tallata APC ba kuma ba zan ce a zaɓe ta domin ba ni da abin da zan nuna wanda APC ta yi mana.”

Maganar ta zo ne a daidai lokacin da ake ƙara samun ra’ayoyi daban-daban daga ’yan fim, mawaka da sauran fitattun mutane kan harkokin siyasa yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.

Wannan ba shi ne karo na farko da ake danganta Tahir Fagge da s**ar APC ba. A wani bayani da aka wallafa a shafukan sada zumunta, an ruwaito shi yana cewa “APC ta gaza, ta lalata komai, ta ci amanar talaka,” tare da neman afuwar al’ummar da ya taɓa tallata wa jam’iyyar.

Sai dai har yanzu wannan matsaya tasa na iya haifar da muhawara tsakanin magoya bayan jam’iyyar da masu adawa da ita, musamman ganin yadda siyasar 2027 ke ƙara ɗaukar zafi.

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sanar da cewa ta kammala aikin saka sunayen dukkan ‘yan takararta na kujera...
07/08/2026

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sanar da cewa ta kammala aikin saka sunayen dukkan ‘yan takararta na kujerar gwamna da majalisun dokokin jihohi a INEC Candidate Nomination Portal, domin babban zaɓen 2027.

Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Prof. Nentawe Yilwatda, ya taya shugabanni, mambobi da ‘yan takarar jam’iyyar murna bisa kammala aikin.

A cewar Yilwatda, APC ta samu nasarar saka sunayen ‘yan takarar gwamna 28 da mataimakansu, da kuma ‘yan takarar Majalisun Dokokin Jihohi 1,015 a shafin INEC.

Wannan na zuwa ne yayin da jam’iyyun siyasa ke kammala shirye-shiryensu domin zaɓen 2027.

Wani hoto na wani katafaren gida da ake danganta shi da wani matashi mai harkar Crypto a Arewacin Najeriya ya jawo ce-ce...
07/08/2026

Wani hoto na wani katafaren gida da ake danganta shi da wani matashi mai harkar Crypto a Arewacin Najeriya ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta.

Alhassan Mai Lafia Mai sharhi kan abubuwan yau da kullum ya fara tambayar cewa, idan har matashin da ke harkar Crypto zai iya mallakar irin wannan katafaren gida, to wane irin gida ne mutum mai irin ƙwarewar Cybersecurity, Computer Science da Digital Economy kamar Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami zai iya mallaka?

Wasu daga cikin masu sharhin sun yi hasashen cewa irin wannan gida na iya kaiwa 50 zuwa 100 idan aka kwatanta da daraja da girman kadarar.

Farfesa Pantami ya yi fice a fannonin fasahar zamani, musamman Cybersecurity da Digital Economy, sannan ya taɓa rike muƙamin Ministan Sadarwa da Tattalin Arziƙin Zamani na Najeriya.

Sai dai, tambayar da ke ci gaba da yawo a kafafen sada zumunta ita ce:

“Idan ɗan Crypto zai iya mallakar irin wannan gida, to Farfesa Pantami, wanda ya shafe shekaru yana cikin duniyar fasahar zamani da Digital Economy, wane irin gida ne zai iya mallaka?”

Wannan tambayar dai ta haifar da muhawara mai zafi tsakanin masu amfani da kafafen sada zumunta.

Address

Maitama Abuja
Abuja
005

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gombawa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gombawa:

Shortcuts

Share