Tambari News

Tambari News Domin Samun labarai masu inganci
(1)

ABUJA: Kotu Ta Tura Faruk Abuja Gidan Yarin Kuje Kan Zargin Cin Zarafin Ministan TsaroAn gurfanar da fitaccen ɗan TikTok...
27/08/2026

ABUJA: Kotu Ta Tura Faruk Abuja Gidan Yarin Kuje Kan Zargin Cin Zarafin Ministan Tsaro

An gurfanar da fitaccen ɗan TikTok kan tuhume-tuhume guda huɗu, yayin da aka ɗage sauraron buƙatar belinsa zuwa 9 ga Satumba

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin tsare fitaccen ɗan TikTok, Faruk Musa Muhammad, wanda aka fi sani da Faruk Abuja, a gidan yarin Kuje bisa zargin cin zarafin Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, ta kafar intanet. An gurfanar da Faruk mai shekaru 35 a gaban Mai Shari’a Obiorah Egwuatu kan tuhume-tuhume guda huɗu.

Ana zargin Faruk da wallafa wasu kalamai da s**a yi ikirarin cewa sojojin Najeriya da ke yaƙi da ta’addanci na rasa rayukansu sakamakon gazawar Ministan Tsaro da shugabannin hukumomin tsaro wajen ɗaukar matakan da s**a dace. Haka kuma, tuhume-tuhumen sun ƙunshi wasu zarge-zarge da s**a shafi Mai Bai wa Ministan Shawara kan Harkokin Shari’a, Aliyu Anas.

Faruk ya musanta dukkan tuhume-tuhumen da ake masa. Lauyansa, Abdulkadir Ahmad, ya kuma sanar da kotun cewa yana da niyyar neman a bayar da belinsa. Sai dai Mai Shari’a Egwuatu ya ɗage sauraron buƙatar belin zuwa 9 ga Satumba, 2026, tare da bayar da umarnin ci gaba da tsare Faruk a gidan yarin Kuje har zuwa lokacin.

26/08/2026

"Fulani sun fi kowacce ƙabila ba da gudummawa wajen samar da kuɗin shiga a jihar Nasarawa amma an barmu a baya"

Nasir Abubakar, Kodinetan Umbagadu Na Fulanin jihar Nasarawa.

Wamba: Hajiya Maryam Wadada Ta Tallafa wa Mata 500 Kowacce daga cikin matan ta samu tallafin ₦50,000 domin ƙarfafa sana’...
25/08/2026

Wamba: Hajiya Maryam Wadada Ta Tallafa wa Mata 500
Kowacce daga cikin matan ta samu tallafin ₦50,000 domin ƙarfafa sana’a da tattalin arzikin iyali a jihar Nasarawa

Ku ajiye mana wata Kalma ko Baiti da za ta faranta mana zuciya a wannan safiyar ta bikin Maulidin Annabi SAWA. BARKAN MU...
25/08/2026

Ku ajiye mana wata Kalma ko Baiti da za ta faranta mana zuciya a wannan safiyar ta bikin Maulidin Annabi SAWA.

BARKAN MU DA MAULIDIN FIYAYYEN HALITTA.

𝐀 𝐓𝐫𝐢𝐮𝐦𝐩𝐡𝐚𝐧𝐭 𝐇𝐨𝐦𝐞𝐜𝐨𝐦𝐢𝐧𝐠 & 𝐀 𝐁𝐢𝐫𝐭𝐡𝐝𝐚𝐲 𝐖𝐨𝐫𝐭𝐡 𝐂𝐞𝐥𝐞𝐛𝐫𝐚𝐭𝐢𝐧𝐠: 𝐖𝐞𝐥𝐜𝐨𝐦𝐞 𝐇𝐨𝐦𝐞, 𝐃𝐫. 𝐅𝐚𝐢𝐬𝐚𝐥 𝐒𝐡𝐮𝐚𝐢𝐛 (DFS)!𝟏𝟒𝐭𝐡 𝐀𝐮𝐠𝐮𝐬𝐭, 𝟐𝟎𝟐𝟔 - 𝐀𝐛𝐮𝐣𝐚,...
25/08/2026

𝐀 𝐓𝐫𝐢𝐮𝐦𝐩𝐡𝐚𝐧𝐭 𝐇𝐨𝐦𝐞𝐜𝐨𝐦𝐢𝐧𝐠 & 𝐀 𝐁𝐢𝐫𝐭𝐡𝐝𝐚𝐲 𝐖𝐨𝐫𝐭𝐡 𝐂𝐞𝐥𝐞𝐛𝐫𝐚𝐭𝐢𝐧𝐠: 𝐖𝐞𝐥𝐜𝐨𝐦𝐞 𝐇𝐨𝐦𝐞, 𝐃𝐫. 𝐅𝐚𝐢𝐬𝐚𝐥 𝐒𝐡𝐮𝐚𝐢𝐛 (DFS)!

𝟏𝟒𝐭𝐡 𝐀𝐮𝐠𝐮𝐬𝐭, 𝟐𝟎𝟐𝟔 - 𝐀𝐛𝐮𝐣𝐚, 𝐍𝐢𝐠𝐞𝐫𝐢𝐚

Glad to have our APC Candidate for Nasarawa West Senatorial District, Dr. Faisal Shuaib, OON, safely back home in Nigeria.

Welcome back, our incoming distinguished Senator in sha Allah, and a very happy birthday to you. May Allah bless you with good health, strength, wisdom, and continued success. Ameen

25/08/2026

Bayani akan WAƘAFI da yadda ake yi bisa Addinin Musulunci tare da Dr. Sabo Ibrahim Sani na jami'ar jihar Nasarawa dake Keffi.

KSMC @ 1: Ƙungiyar Keffi Social Media Connect Ta Ƙarfafa Matasan Keffi Kan Jagoranci, Amfani da Soshiyal Midiya da Dogar...
25/08/2026

KSMC @ 1: Ƙungiyar Keffi Social Media Connect Ta Ƙarfafa Matasan Keffi Kan Jagoranci, Amfani da Soshiyal Midiya da Dogaro da Kai

An gudanar da Tea Hangout na musamman a NSUK, inda masana da shugabanni s**a tattauna kan siyasa, ɗaukar nauyi da sana’o’in dogaro da kai

Ƙungiyar Keffi Social Media Connect (KSMC) ta gudanar da bikin cika shekara guda da kafuwarta, inda aka shirya wani Tea Hangout a Window on America, Nasarawa State University, Keffi. Taron ya mayar da hankali kan ci gaban matasa, jagoranci nagari, ɗaukar nauyin ɗan ƙasa, siyasa, amfani da kafafen sada zumunta yadda ya kamata da kuma ƙarfafa matasa ta hanyar sana’o’i.

Daga cikin muhimman jawaban da aka gabatar akwai na Hon. Dr. Idris Ahmad Damagani, Shugaban Ƙaramar Hukumar Keffi, wanda ya yi magana kan “Responsible Youth Participation in Politics Beyond Thuggery and Dependency”. Ya buƙaci matasa su guji daba, tashin hankali da dogaro da ’yan siyasa, su rungumi siyasa mai ma’ana, jagoranci da hidima ga al’umma. Anas Jafar Ramalan Sarkin Yaki Ne, Shugaban Prestige Unisex Collection, ya tattauna kan yadda matasa za su yi amfani da soshiyal midiya cikin gaskiya da ɗaukar nauyi, yayin da Salihu Abdullahi Umar, Manajan Daraktan SI14 Clothing, ya ƙarfafa matasa su rungumi sana’o’i, koyon fasaha da kasuwanci domin dogaro da kansu. An kuma samu gwanin waƙar baka daga Maryam El Abari.

Taron ya samu saƙonnin fatan alheri daga Salisu Sani Idris, Hadimin Mataimakin Shugaban Ƙasa; Hon. Kasim Talba, SA ga Gwamnan Nasarawa kan Harkokin Siyasa; Hon. Dr. Abdullahi Bashir Idris, ɗan takarar ADC na Keffi/Karu/Kokona; Hon. Nuraini Abdullahi Adamu (Dujiman Keffi), SA ga Gwamnan Nasarawa kan Albarkatun Ruwa; da Obasun Paul, wanda ya kafa Purposeful City Network. KSMC ta sake jaddada aniyarta ta ci gaba da bunƙasa matasa, wayar da kan jama’a, amfani da soshiyal midiya cikin alhaki, kasuwanci, hidimar al’umma da kyakkyawar hulɗa tsakanin matasa. Shekara ɗaya ta haɗin kai, shekara ɗaya ta tasiri — makoma mai cike da dama na nan gaba.

23/08/2026

Comrd. Adamu Sanusi Alguruz ya yi zazzafan Martani ga Abdullahi Dallatu bisa s**ar salon siyasar Dr. Faisal Shuaib OON

HOTUNA: Malaman Musulmi 500 Sun Amince da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara a 2027 — MasariAn ce malaman sun bayyana goyon b...
23/08/2026

HOTUNA: Malaman Musulmi 500 Sun Amince da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara a 2027 — Masari

An ce malaman sun bayyana goyon bayansu ga Tinubu tare da kira ga ’yan Arewa su zaɓi APC

Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Siyasa, Ibrahim Masari, ya ce kusan malaman addinin Musulunci 500 da shugabannin addini daga jihohin Arewa 19 da Abuja sun amince da Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin ya sake neman takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

Masari ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook bayan halartar taron Northern Muslim Intellectual Forum da aka gudanar a Sir Ahmadu Bello Hall, Dutse, Jihar Jigawa, inda malamai s**a tattauna batutuwan tsaro, ci gaba da makomar yankin Arewa. Taron ya samu halartar gwamnonin Jigawa, Kano, Yobe, Sokoto da Kaduna, da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, da Ministan Gidaje, Muttaka Darma.

A cewar Masari, mahalarta taron da s**a haɗa da Shehunnai Limamai, Huffaz da masu wa’azi, sun bayyana gamsuwarsu da yadda gwamnatin Tinubu ke tunkarar matsalolin tsaro da ayyukan raya ƙasa. An ce taron ya fitar da ƙudurin amincewa da Tinubu da kuri’ar goyon baya, tare da kira ga ’yan Arewa da su mara wa APC baya a zaɓen 2027.

2027: Ƙungiyar Matasan Nasarawa Ta Buƙaci Tinubu Ya Sake Duba Wakilcin Jihar a Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen APCƘungiyar ta...
22/08/2026

2027: Ƙungiyar Matasan Nasarawa Ta Buƙaci Tinubu Ya Sake Duba Wakilcin Jihar a Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen APC

Ƙungiyar ta nemi a ƙara wa Gwamna Sule da Hajiya Imaan Suleiman-Ibrahim manyan ayyuka a tsarin kamfen ɗin

Ƙungiyar Coalition of Youth Support Groups for Wadada 2027 ta roƙi Shugaba Asiwaju Bola Ahmed Tinubu , a matsayinsa na Jagoran APC na Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa na jam’iyyar, da ya sake duba tsarin wakilcin Jihar Nasarawa a kwamitin kamfen ɗin da aka fitar kwanan nan. Shugaban ƙungiyar kuma Shugaban NYCN na Jihar Nasarawa, Kwamared Jaafar M. Loko, ne ya bayyana hakan a wata sanarwar manema labarai..

Ƙungiyar ta ce roƙon nata ba ya nufin adawa da mutanen da aka naɗa daga jihar, sai dai tana son a tabbatar da cewa matsayin siyasar Nasarawa da gudummawar da jihar ke bayarwa ga APC sun samu cikakkiyar wakilci. Ta musamman buƙaci a bai wa Gwamna Gov. Abdullahi A. Sule, wanda shi ne Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta Tsakiya, babban matsayi wajen jagorantar kamfen ɗin a yankin North-Central, ko kuma a duba yiwuwar naɗa shi Daraktan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a ko wani babban matsayi da ya dace da gogewarsa.

Haka kuma, ƙungiyar ta buƙaci a sake duba matsayin Hajiya Imaan Suleiman-Ibrahim, Ministar Harkokin Mata, domin ganin an ba ta wani babban matsayi a tsarin yaƙin neman zaɓen, musamman a ɓangaren wayar da kan mata ko wani muhimmin darakta. A cewar Kwamared Loko, hakan zai ƙara wa mata, matasa da sauran magoya bayan APC a Nasarawa kwarin gwiwa, tare da ƙarfafa haɗin kan jam’iyya da inganta tsarin kamfen ɗin APC a Nasarawa da yankin Arewa ta Tsakiya.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tambari News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share