Makarantar Alkauthar Abuja Nigeria

Makarantar Alkauthar Abuja Nigeria ~Ba'a Shi'a da Jahilci~

Kar ka ga taƙallubin kafirai da wadaƙansu a doron ƙasa ya ruɗeka, ainihin ana musu Shifta ne don su ƙara laifi, domin za...
28/09/2024

Kar ka ga taƙallubin kafirai da wadaƙansu a doron ƙasa ya ruɗeka, ainihin ana musu Shifta ne don su ƙara laifi, domin za su koma mahalaka, za su koma ga azaban da ba ya da iyaka.

Inji Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky Hafizahullah.

✍️ Kauthar Sunusi
Makarantar Alkauthar

IN IMAM (MAHADI ALAIHISSALAM) YA BAYYANA ZA'A SHA MAMAKI!.Za'a ga cewa akwai wasu ilmummukan da sam da can ba'a gansu ba...
24/09/2024

IN IMAM (MAHADI ALAIHISSALAM) YA BAYYANA ZA'A SHA MAMAKI!.

Za'a ga cewa akwai wasu ilmummukan da sam da can ba'a gansu ba (ba'a sansu ba), wanda komi zai zama ƙarara ga mutane. Alal misali: duk abubuwan nan da s**a faru a da (shekarun baya) to yanzu za'a je a zuƙosu ne!, Kamar yaƙin Badar; da Uhud; da Handaƙ; da Jamal; da Siffin; da Karbala, to Ɗan-Adam zai gano zai matsa wani na'ura ne sai ya gansu!, Dama ashe Iska na recoding ya na ajewa!, Ashe Ƙasa ma ta na recoding ta na ajewa!, Komi da ka ke gani ashe (Iska da Ƙasa) ya na ajewa, yanzu Ɗan-Adam zai gano tsotso wannan daga Ƙasa ko ya ɗiba daga Iska sai ya fito da shi!.

To in yai wannan ba ya na nufin wai shi (Ɗan-Adam) ya ƙaƙaro Ilimi ba ne, a'a ya gano ne. Duk Ilmummuka da kuke gan ganowa ne ake yi, don dama akwaishi. Kamar yanda Ilimi Allah ya rabashi kashi Ashirin da Bakwai ne (27), tun daga Adam har yazuwa Bayyanar Imam Mahadi (a.s) an saukar da uku ne kawai! In Imam Mahadi ya bayyana (Af) Allah zai saukar da sauran guda ashirin da Huɗu ɗin! Ta yanda Sahihin Mumini zai iya yin mi'iraji (zuwa) saman bakwai ya dawo.

Lokacin zai zama Ilimi ya wadata ne, ya zama ɗan Adam fahimtarsa ya kai a nuna masa wannan. Ana nan (Ɗan-Adam) in ya kai wani miƙdari na lalacewa to sai a cire Taklifi, magana ya ƙare an rufe ƙofan tuba. An gama, koma mutum ya yi imani ba anfani, ko ya yi Ibada ma ba amfani, domin an zo ƙarshe. Saboda an riga an gama gwada Mutum, an bashi hankali na sanar da shi abubuwa an nuna masa komi, ya rage ya bi. To wannan bai zo ba, amma za mu ga an k**a hanya.

Inji Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky Hafizahullah.

✍️Alkauthar Sunusi
Alkauthar

Abinda ya k**ata Ku sani game da Malam Haruna Abbas.Malam Haruna Abbas Almajirin Sayyid Zakzaky (H) ne, an k**a shi a fi...
18/09/2024

Abinda ya k**ata Ku sani game da Malam Haruna Abbas.

Malam Haruna Abbas Almajirin Sayyid Zakzaky (H) ne, an k**a shi a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano a lokacin da ya dawo daga ƙasar Lebanon, yau kimanin Shekaru Goma Sha Biyu ake tsare da shi ba tare da ya aikata laifin komai ba.

Malam Haruna Abbas ya yi shekara uku a hannun DSS da ke Abuja cikin azabtarwa dare da rana, daga bayan matsin lamba daga lauyoyinsa sai aka maida shi a gidan yarin Kuje. A nan ma s**a cigaba da azabtar dashi babu tausayi. Aka ɗaure wuyansa, hannunsa da ƙafarsa da sarƙoƙi masu hakwara!. Sannan a kowace rana ana bashi abinci sau biyu a tafin hannunsa.

Duk wata buƙatar da ta sameshi to a inda yake anan zai gabatar, babu shamaki ko bambanci a tsakanin muhallin zamansa da Ban-Ɗaki (toilet), duk da cewa ya na da ciwon suga; Asma da hawan-jini, su a wurinsu ko ma me zai sameshi basu damu ba.

Shin me ya sa aka k**ashi kuma ake masa irin wannan azabtarwa tsawon shekaru?

Saboda ya ƙi amincewa ya sanya hannu a kan wata takarda mai ɗauke da cewa Allamah Sayyid Zakzaky Hafizahullah ne ya tura shi ƙasar Iran dan ya koyo Ta'addanci!. Yaƙi amincewa da hakan, ya ce ba zai ɗorawa Sayyid Ibraheem Zakzaky Hafizahullah laifin da bai yi ba, ba zai cutar da bawan Allah ba. Domin ƙarya ne da Sharri dan a samu damar cutar da Jagora Sayyid Zakzaky Hafizahullah. Dan haka ko za'a kasheshi ba zai saka hannu ba. Akan haka ne su ke cigaba da azabtar da shi har izuwa yanzu.

Su waye ke da Alhakin wannan zalunci ga Malam Haruna Abbas tsawon shekaru goma sha biyu?

1. Jami'an CIA na America
2. Jami'an Mos*sad na Is*rael
2. Jami'an DSS na Nigeria
Su suke da Alhakin wannan Zaluncin ga wannan bawan Allah Malam Haruna Abbas na tsareshi tsawon shekaru goma sha biyu (12) ba tare da ya aikata laifin komai ba.

✍️Nusaiba Muhammad
14/Rabi'ul-Auwal/1446
18/September/2024





Kaɗan daga Zaluncin Gwamnatin Zalunci ta Najeriya.An jima ana Zaluntar Almajiran Sayyid Zakzaky Hafizahullah, tare da yi...
18/09/2024

Kaɗan daga Zaluncin Gwamnatin Zalunci ta Najeriya.

An jima ana Zaluntar Almajiran Sayyid Zakzaky Hafizahullah, tare da yi musu ƙazafi da sharri.

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN Naso In Magana ...
28/05/2024

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN
INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN
INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN

Naso In Magana Ne Dangane Da Wannan Musiba Da Ta Same Mu A Daidai Wannan Lokaci, Na Rashin Wadannan Bayin Allah, Shugaban
Kasar Jamhuriyar Musulunci Ta Iran, Ayatullah Sayyid Ibraheem Ra’isi, Da Wazirin Sa Na Harkokin Waje, Husain Amir Abdullahian, Da
Limamin Tabriz Kuma Wakilin Sayyid Qa’id A Lardin Gabashin Azerbaijan, Da Gwamnan Tabriz, Da Wadansu Wanda Suke Tare Da Su.

A Abinda Zamu Iya Ce Mishi Wani Hadisa (Wani Abinda Ya Faru) Mummuna Da Ya Auku A Helikoftan Da Suke Tafe Wanda Aka Rasa
Su Gaba Dayan Su. Wannan Ya Auku A Daidai Lokacin Da Muke Cikin Bikin Tunawa Da Ranar Haihuwar Imam Ridha (A.S), Ranar 11
Ga Watan Zulqa’ada.

Muna Cikin Wannan Biki Sai Kawai Labari Ya Zo Mana Cewa Ainihin Ga Halin Da Ake Ciki, Ba’a Ga Jirgin Shugaban
Kasa1 Ba (Na Iran)!, To Wannan Sai Yasa Ainihin Wannan Zama Namu Na Biki Ya Koma Jaje, Aka Fara Kuma Ana Addu’o’i, Wanda Mu
Anan Hakannan Aka Yi Ta Addu’o’i, Muka Yi Ta Bin Abubuwan Da Ke Faruwa Dakika Bayan Dakika, Ainihin Idanun Mu Basu Iya Bacci
Ba A Wannan Dare.

Haka Zalika Kuma Dukkan Sassa Na Duniya, Ainihin Musamman Anan Haramin Imam Ridha (A.S) Wanda Shima Taron Mutane Masu Dinbin Yawan Gaske S**a Koma Addu’o’i, Na Bidan Fatan Mafita Garesu. Haka Ma Ainihin Yan’Uwan Da S**a Tafi
Hajji Suma S**a Yi Dafifi A Haramin Makka Da Madina Duk Suna Ta Addu’o’i, To Hakanan Muka Kwana Bamu Yi Bacci Ba!, Muna
Taraqqubin (Jiran) Me Zamu Ji?,

Saboda A Lokacin Ana Cewa Hadari Da Iska Da Ruwan Sama Ya Hana Ainihin Masu Kokarin Isa Wurin
Don Ceto Su, Ainihin Basu Iya Isa Wurin Ba, Har Saida Wayewan Gari!, Sannan Kuma Daga Karshe Aka Isa, Ainihin Labari Mara Dadi
Ya Iso Mana, Cewa Ainihin Ba’a Samu Ko Dayan Su Da Rai Ba. Wannan Ya Kada Mu Sosai, Ya Girgiza Mu Sosai, Ya Samu Cikin
Matsanancin Bakin-Ciki Da Dimuwa!, Mun Girgiza Sosai, Kuma Kalmomi Ba Zasu Iya Bayyana Irin Kaduwar Mu Da Alhinin (Jaje) Mu
Da Bakin-Cikinmu A Wannan Rana Ba.

_Jagora Sayyid Zakzaky Hafizahullah

أَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ أَنْ تُصَلِّيَ عَلَىٰ مُحَمَّدٍ وآلِ مُحَمَّدٍ وَأَنْ تَأْتِيَ قَائِدَنَا إِبْرَاهِيمَ زَكْزَكِي بِفَرَجٍ مِنْ عِنْدِكَ يُشْبِهُ حُسْنَ ظَنِّهِ بِكَ يَا أَرْحَمَ الرَّاحِمِين.

27/05/2024

Albishirin Ku Azzalumai 💥

Makarantar Alkauthar reshen Abuja ta ware kwanaki Arba'in Dan karanta Ziyarar Ashura Da Addu'ar Alƙama Da niyyar Allah y...
26/05/2024

Makarantar Alkauthar reshen Abuja ta ware kwanaki Arba'in Dan karanta Ziyarar Ashura Da Addu'ar Alƙama Da niyyar Allah ya kai Lada Ga Ruhin jaruman Shahidan Jamhuriyyar Musulunci ta Iran.

أَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ أَنْ تُصَلِّيَ عَلَىٰ مُحَمَّدٍ وآلِ مُحَمَّدٍ وَأَنْ تَأْتِيَ قَائِدَنَا إِبْرَاهِيمَ زَكْزَكِي بِفَرَجٍ مِنْ عِنْدِكَ يُشْبِهُ حُسْنَ ظَنِّهِ بِكَ يَا أَرْحَمَ الرَّاحِمِين.

Hadisai goman farko Daga cikin Littafin ƊAREEƘUL JANNAH Mallakin Makarantar Alkauthar Na Mal. Muhammad Sunusi Usman Birn...
24/05/2024

Hadisai goman farko Daga cikin Littafin ƊAREEƘUL JANNAH Mallakin Makarantar Alkauthar Na Mal. Muhammad Sunusi Usman Birnin Kebbi, Dake bayani Akan Ilimi Da Malami Da Ɗalibi.

Ku shigo Makarantar Alkauthar Domin samun Ilimin Ahlul Bait Alaihissalam cikin Sauƙi.

Marhaba Da Zuwan Imami Na Takwas a Jerin khalifofin Manzon Allah (S) Imam Ali Arridha Alaihissalam 🎉Mu aje Salatin Annab...
19/05/2024

Marhaba Da Zuwan Imami Na Takwas a Jerin khalifofin Manzon Allah (S) Imam Ali Arridha Alaihissalam 🎉

Mu aje Salatin Annabi Hidima zuwa ga Ruhin Jikan sa Sayyid Zakzaky Hafizahullah ✨

اللهم صل على محمد وال محمد وعجل فرجهم 🌹

أَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ أَنْ تُصَلِّيَ عَلَىٰ مُحَمَّدٍ وآلِ مُحَمَّدٍ وَأَنْ تَأْتِيَ قَائِدَنَا إِبْرَاهِيمَ زَكْزَكِي بِفَرَجٍ مِنْ عِنْدِكَ يُشْبِهُ حُسْنَ ظَنِّهِ بِكَ يَا أَرْحَمَ الرَّاحِمِين.

Da yawa mutum kan ɓata ayyukansa ba tare da ya san sun ɓaci ba! Ta hanyar jin cewa ai nine nake yi, ko kuma Sanyi ne dan...
01/02/2024

Da yawa mutum kan ɓata ayyukansa ba tare da ya san sun ɓaci ba! Ta hanyar jin cewa ai nine nake yi, ko kuma Sanyi ne dan a san zan samu wani abu.
Allah ne yake amfani dakai ya aiwatar da aikin sa, kai naka godiya ne da yayi amfani da kai, ba jin cewa kai kayi ba.

🤲أَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ أَنْ تُصَلِّيَ عَلَىٰ مُحَمَّدٍ وآلِ مُحَمَّدٍ وَأَنْ تَأْتِيَ قَائِدَنَا إِبْرَاهِيمَ زَكْزَكِي بِفَرَجٍ مِنْ عِنْدِكَ يُشْبِهُ حُسْنَ ظَنِّهِ بِكَ يَا أَرْحَمَ الرَّاحِمِين.

قال رسول الله صلى الله عليه وآله وسلم:هَذَا عَلِيُّ أَنْصَرُكُمْ لِي، وَأَحَقُكُمْ بِي، وَأَقْرَبُكُمْ إِلَيَّ، وَأَعَزّ...
30/01/2024

قال رسول الله صلى الله عليه وآله وسلم:

هَذَا عَلِيُّ أَنْصَرُكُمْ لِي، وَأَحَقُكُمْ بِي، وَأَقْرَبُكُمْ إِلَيَّ، وَأَعَزُّكُمْ عَلَيَّ، وَاللَّهُ عَزَّ وَجَلَّ وَأَنَا عَنْهُ رَاضِيَانِ...

Manzon Allah (S) Yace: Wannan Aliyu Ya Fiku Taimakona, Ya Fiku Cancanta ta, Ya Fiku Kusanci Gareni, Ya Fiku Girma A Wurina, Allah Mai Girma Da Daukaka Da Ni Mun Yarda Da Shi...

HudubarGhadir

Ta'aliƙi:
Imam yafi kowa cancantar Khalifancin Annabi Muhammad (s) duba da wannan Hadisin.
Yafi kowa matsayi da daraja a gun Allah bayan Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama.

🤲أَللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ أَنْ تُصَلِّيَ عَلَىٰ مُحَمَّدٍ وآلِ مُحَمَّدٍ وَأَنْ تَأْتِيَ قَائِدَنَا إِبْرَاهِيمَ زَكْزَكِي بِفَرَجٍ مِنْ عِنْدِكَ يُشْبِهُ حُسْنَ ظَنِّهِ بِكَ يَا أَرْحَمَ الرَّاحِمِين.

Address

Maraba Abuja
Abuja

Telephone

+2349047986390

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Makarantar Alkauthar Abuja Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Makarantar Alkauthar Abuja Nigeria:

Share