Premiere Hausa magazine

Premiere Hausa magazine ilmantarwa/nishadantarwa

LABARAN GIDA NIGERIA | LABARAN WAJE| HARSHEN HAUSA DA TURANCI| MUJALLARMU AL'UMMARMU MALLAKIN ABDULLAHI ASHIRU FUNTUA
PREMIERE HAUSA MAGAZINE
BILINGUAL
GA MASU SON TALLATA HAJARSU 08032210254

Hadakar Kungiyoyin tsaron sa kai na kasa wato (Coalition of Nigerian Youths on Security and Safety Affairs) reshen jihar...
13/08/2025

Hadakar Kungiyoyin tsaron sa kai na kasa wato (Coalition of Nigerian Youths on Security and Safety Affairs) reshen jihar Bauchi ta gudanar da taron wayar da kai wa kungiyoyin tsaro na sa kai tare da bukatar zama jakadu nagari.

Taron ya gudana tare da hadin gwiwar hukumar wayar da kai ta kasa (NOA) da sauran hukumomin tsaro.

Fargaba Bayan Kwashen Sojoji Daga Tashar Bawa a Karamar Hukumar SabuwaDr. Dikko Umaru Radda read more....
11/08/2025

Fargaba Bayan Kwashen Sojoji Daga Tashar Bawa a Karamar Hukumar Sabuwa
Dr. Dikko Umaru Radda read more....

Fargaba Bayan Kwashen Sojoji Daga Tashar Bawa a Karamar Hukumar Sabuwa 11/08/2025 Rahotanni daga Karamar Hukumar Sabuwa, Jihar Katsina, sun tabbatar da cewa an kwashe jami’an tsaro daga Tashar Bawa…

Fargaba Bayan Kwashen Sojoji Daga Tashar Bawa a Karamar Hukumar Rahotanni daga Karamar Hukumar Sabuwa, Jihar Katsina, su...
11/08/2025

Fargaba Bayan Kwashen Sojoji Daga Tashar Bawa a Karamar Hukumar

Rahotanni daga Karamar Hukumar Sabuwa, Jihar Katsina, sun tabbatar da cewa an kwashe jami’an tsaro daga Tashar Bawa, lamarin da ya haifar da firgici tare da sa wasu mazauna yankin fara barin gidajensu domin neman mafaka.

Tashar Bawa, wadda ke iyaka da Jihar Kaduna, na cikin yankunan da s**a dade suna fama da hare-haren ‘yan bindiga, garkuwa da mutane, da kuma rasa rayuka, abin da ya tilasta wa wasu mazauna yin hijira. A baya, bayan kafa sansanin sojoji a yankin, rahotanni sun nuna raguwar hare-haren da kusan kaso 90 cikin ɗari, kamar yadda wasu mazauna s**a shaida wa Katsina Times.

Sai dai a safiyar Asabar, mazauna s**a wayi gari da ganin an kwashe dukan sojojin daga yankin ba tare da sanin dalili ba. Wannan mataki ya tayar da hankulan jama’a, inda wasu s**a fara kwashe kayayyakinsu don komawa wuraren da s**a fi samun tsaro.

Wasu mazauna sun yi kira ga Gwamnatin Jihar Katsina da hukumomin tsaro da su gaggauta dawo da jami’an tsaro a yankin, musamman ganin mafi yawan mazauna manoma ne, kuma a halin yanzu ana tsakiyar damina, lokaci mai muhimmanci ga aikin gona.
Source:katsina city News page
Dr. Dikko Umaru Radda

Rukayyah Fema a 15years Yobe state girl has also put Nigeria 🇳🇬 on prestigious Map of the world.  She won the overall be...
05/08/2025

Rukayyah Fema a 15years Yobe state girl has also put Nigeria 🇳🇬 on prestigious Map of the world. She won the overall best in Debate organised by Teeneagle in London.

She deserves to be honour 🎖

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badegi FMMinistan Yaɗa Labarai da Waya...
04/08/2025

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badegi FM

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci jama'a da su kwantar da hankalin su bayan dakatar da gidan rediyon Badegi FM da ke Minna da Gwamnatin Jihar Neja ta yi.

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, shi ne ya bayar da umarnin rufe tashar , kamar yadda rahotanni s**a nuna, a yayin wani taron faɗaɗa na tsangayar jam'iyyar APC da aka gudanar a Minna a ranar 1 ga Agusta.

Rahotanni sun ce gwamnan ya zargi rediyon da rashin bin ƙa'idar aiki a cikin shirye-shiryen sa da kuma tayar da zaune tsaye kan gwamnati.

Minista Idris ya bayyana damuwa da irin martanin da al’umma da masu ruwa da tsaki a harkar yaɗa labarai s**a nuna dangane da lamarin. Amma ya jaddada cewa hukumar da ke da hurumin dakatar da lasisin gidajen rediyo da talabijin ita ce Hukumar Kula da Gidajen Radiyo da Talabijin ta Ƙasa (NBC), kamar yadda doka ta tanada.

Sanarwar da Gwamnatin Tarayya ta bayar kan lamarin ta ce: “Saboda haka, ministan yana maraba da matakin da Gwamnatin Jihar Neja ta ɗauka na kai koken da ta ke da shi kan zargin rashin ɗabi’a da Badegi FM ta yi a hukumance zuwa ga NBC domin a warware batun.”

Idris ya roƙi dukkan ɓangarori da su kwantar da hankalin su, yana mai tabbatar da cewa NBC tana da tsarin da ya dace na warware irin waɗannan matsaloli cikin gaskiya da adalci.
Copied

Menene ra'ayoyin ku akan kirkiro sabuwar jihar karaɗuwa?Idan jihar ta tabbata za'a samu manyan cibiyoyin tsaro da s**a h...
03/08/2025

Menene ra'ayoyin ku akan kirkiro sabuwar jihar karaɗuwa?

Idan jihar ta tabbata za'a samu manyan cibiyoyin tsaro da s**a haɗa da Sansanin sojoji, Cibiyar yan sanda. Cibiyar DSS. Hukumar Immigration, da jami'an hana fasa kwabri. Cibiyar Civil Defence. Da sansanonin jami'an tsaro daban daban.

Menene ra'ayin ku?

WANNAN  SHINE Dr.  Abdullahi sufi shugaban SIDES.YAKASANCE  MALAMI WANDA YAKOYAR DA DALIBAI DAGA BANGARORI MABANBANTA, N...
03/08/2025

WANNAN SHINE Dr. Abdullahi sufi shugaban SIDES.
YAKASANCE MALAMI WANDA YAKOYAR DA DALIBAI DAGA BANGARORI MABANBANTA, NA HANNUN DAMAR PROF AA.GWARZO SHUGABAN GAMMAYAR JAMI AR MARYAM ABACHA AMERICAN UNIVERSITY.

Governor Uba Sani has officially flagged off the 2025 Fertilizer Distribution Exercise in Kaduna State, distributing 400...
03/08/2025

Governor Uba Sani has officially flagged off the 2025 Fertilizer Distribution Exercise in Kaduna State, distributing 400 trucks of fertilizer to 100,000 smallholder farmers.

The well-attended event, held at Murtala Square in Kaduna, reaffirmed the administration’s unwavering commitment to inclusive development, food security, and rural prosperity through sustained agricultural transformation.

With this latest distribution, Governor Uba Sani has now distributed over 900 trucks of fertilizer to a total of 220,000 smallholder farmers across the state—making Kaduna the only state in Nigeria to consistently provide support of this scale to its farming population.

TABBAS KATSINA STATE  MUNA CIKIN DACE DA KASANTUWAR SAMUN SHUGABANNI DA ALLAH YASA SUNA DA ILMI (Ph.D) SHINE TAKENMU.Sak...
03/08/2025

TABBAS KATSINA STATE MUNA CIKIN DACE DA KASANTUWAR SAMUN SHUGABANNI DA ALLAH YASA SUNA DA ILMI (Ph.D) SHINE TAKENMU.

Sakon *BIYAR NA MUSSAMMAN*
1.TSARO
2.ILMI
3.TATTALIN ARZIKI
4.KIWON LAFIYA
5.AIKINYI

Da Dumi-Dumi: Ana shirin gudanar da zazzafar zanga-zangar nuna goyon baya ga 'yan sanda a Shelkwatar 'yan sanda ta ƙasa....
21/07/2025

Da Dumi-Dumi: Ana shirin gudanar da zazzafar zanga-zangar nuna goyon baya ga 'yan sanda a Shelkwatar 'yan sanda ta ƙasa.

A cewar fitaccen ɗan Jarida, Omoyele Sowore, za'a gudanar da zanga-zangar ne a safiyar ranar Litinin a Shelkwatar 'yan sanda ta ƙasa dake Abuja, don yaƙi da take haƙƙin jami'an 'yan sanda.

Shin zaku shiga cikin zánga-zángár nuna goyon baya ga 'yan sanda a gobe ?

Source IDON MIKIYA

Address

Abuja

Opening Hours

Friday 09:00 - 20:00
Saturday 00:00 - 17:00
Sunday 10:00 - 17:00

Telephone

+2348032210254

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Premiere Hausa magazine posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share