Fitila Hausa News

Fitila Hausa News Fitila Hausa gidan Sahihan Labarai da Nishadi.
(1)

Ministan Tsaro Ya Kai Ziyarar Ban Kwana Ga Shugaba Tinubu a Addis AbabaMinistan Tsaro na Najeriya, Mai Girma Mohammed Ba...
18/02/2025

Ministan Tsaro Ya Kai Ziyarar Ban Kwana Ga Shugaba Tinubu a Addis Ababa

Ministan Tsaro na Najeriya, Mai Girma Mohammed Badaru Abubakar CON mni, a ranar Litinin 17/02/2025, ya kai ziyarar ban kwana ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu CGFR a birnin Addis Ababa na ƙasar Habasha, jim kaɗan kafin shugaban ya baro ƙasar zuwa Najeriya.

Shugaba Tinubu yana Habasha ne domin halartar taron koli na Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) karo na 38, wanda aka gudanar a Addis Ababa.

18/02/2025

Yadda NABURASKA yayi yabon Sanatan Gabashin Sokoto Sen. Ibrahim Lamido.

Ƴansanda na neman mawaki Portable bisa kai wa ma'aikatan gwamnatin Ogun hariRundunar ƴanandan jihar Ogun ta bayyana cewa...
18/02/2025

Ƴansanda na neman mawaki Portable bisa kai wa ma'aikatan gwamnatin Ogun hari

Rundunar ƴanandan jihar Ogun ta bayyana cewa tana neman mawakin nan mai suna Habeeb Olalomi, wanda aka fi sani da Portable ruwa a jallo bisa zarginsa da jagorantar wani hari akan jami’an gwamnati da ke gudanar da ayyukansu a jihar.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan, Omolola Odutola ya fitar a jiya Litinin, ya ce lamarin ya faru ne a ranar 5 ga Fabrairu, 2025, da misalin karfe 10:00 na safe lokacin da jami’ai uku daga ma’aikatar tsare-tsare da raya birane ta jihar Ogun, Onabanjo Abidemi, Raymond Lateef -Ridwan a Oke-Osa, Tigbo Ilu Ota.

A yayin aikin, sai jami’an su ka je wajen wani dattijo, wanda daga baya aka bayyana shi a matsayin mahaifin Portable, a mashaya a Odogwu, inda aka ce wajen na mawakin ne

Bayan gabatar da kansu kuma s**a nemi a basu takardun ginin su gani, sai mahaifin Portable din ya sanar da su cewa ba sa hannun sa kuma ɗan nasa baya nan.

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa duk da haka, bayan ɗan lokaci,bsai Portable, ya jagoranci matasa su tara dauke da muggan mak**ai, su ka kai hari kan jami'an.

An ce jami’an sun samu raunuka daban-daban amma sun yi nasarar tserewa inda s**a kai rahoton harin ga ofishin ‘yansandan yankin Ita.

Yayin da aka k**a mutane tara daga cikin yaran na Portable, mawakin ya gudu daga wurin kuma tun a lokacin ya buya.

Daily Nigerian Hausa

Watanni 3 ba a ji ɗuriyar mataimakin gwamnan jihar Taraba ba tun da ya kwanta rashin lafiya Ana ci gaba da nuna damuwa k...
18/02/2025

Watanni 3 ba a ji ɗuriyar mataimakin gwamnan jihar Taraba ba tun da ya kwanta rashin lafiya

Ana ci gaba da nuna damuwa kan halin da mataimakin gwamnan jihar Taraba, Aminu Alkali ke ciki, duba da rashin lafiya da ke damun sa.

Daily Trust ta rawaito cewa mataimakin gwamnan dai ya fice daga jihar tun a watan Nuwamban 2024 saboda kalubalen lafiya, sai kuma gwamnatin jihar ta yi gum da bakinta kan halin da ya ke ciki.

Daily Trust ta rawaito cewa da fari, Alkali na kwance a asibitin kasa da ke Abuja saboda rashin lafiya da ba a bayyana ba.

Sai dai wasu majiyoyi da ba a tabbatar da sahihancin su ba sun yi nuni da cewa an fitar da shi daga kasar zuwa kasar Masar domin kula da lafiyarsa sosai.

Rashin fitar da wata sanarwa daga gwamnatin jihar kan halin da mataimakin gwamnan ya ke ciki ya kara haifar da fargaba a tsakanin al’ummar jihar musamman ‘yan siyasa.

Daily Nigerian Hausa

Cikin Masu Siyen Kayan Abinci Suna Boyewa Idan Ya Yi Tsada Su Fito Da Shi Suna Siyarwa, Ya Duri Ruwa, Inda Wani Da Ya Sa...
17/02/2025

Cikin Masu Siyen Kayan Abinci Suna Boyewa Idan Ya Yi Tsada Su Fito Da Shi Suna Siyarwa, Ya Duri Ruwa, Inda Wani Da Ya Sayi Buhunun Masara Akan Naira Dunu 75 Ya Fito Zai Siyar Aka Ki Saye A Naira Dubu Hamsin

Me za ku ce?

Gwamnatin Katsina ta rabawa mata awaki 40,000 a matsayin jari domin kiwo da samar da nama da madara.📷 KTSG
17/02/2025

Gwamnatin Katsina ta rabawa mata awaki 40,000 a matsayin jari domin kiwo da samar da nama da madara.

📷 KTSG

Babu dalilin da farashin suga zai riƙa hawa a Nijeriya, Ƴan kasuwa sun ƙalubalanci Dangote da BUA - Ƴan kasuwaƘungiyar Ƴ...
17/02/2025

Babu dalilin da farashin suga zai riƙa hawa a Nijeriya, Ƴan kasuwa sun ƙalubalanci Dangote da BUA - Ƴan kasuwa

Ƙungiyar Ƴan kasuwa ta Kasuwar Singer, SIMDA, a jihar Kano son yi kira ga kamfanonin Dangote da BUA da su sauko da farashin suga.

Da ya ke sanyawa da manema labarai, wadanda su ka je ofishin sa domin jin bahasin farashin kayaiyakin masarufi a Kano, shugaban SIMDA, Barista Junaidu Muhammad Zakari, ya ce babu wani dalili da zai sanya farashin suga ya ci gaba da hauhawa bayan cewa a gida Nijeriya a ke yin sa.

A cewar Zakari, idan ma an yi maganar tashin farashin kuɗaɗen waje, ai farashin dala akan Naira ya sauko, "saboda haka bai k**ata farashin kayan ya ci gaba da tashi ba."

"Abun damuwa ne. Farashin sauran kayaiyakin masarufi na sauka, amma na suga ya ki sauka ko kuma ya sauka da ɗan kadan.

"Shi fa sugan nan a gida ake yin sa ba a kasar waje ba. Yayin da wasu kayan da ake yi a kasar waje ke sauka, me zai hana farashin suga da ake yi a gida sauka?

"Sabo da haka mu na kira ga kamfanonin Dangote da BUA da su daure su rage farashin suga domin al'umma su samu sauki, musamman ma da watan azumin Ramadan ke ƙaratowa," in ji Zakari.

Kujerar shugabar Majalisar Dokokin Legas na tangal-tangal bayan da jami'an DSS su ka kulle ofishin taAna hasashen cewa s...
17/02/2025

Kujerar shugabar Majalisar Dokokin Legas na tangal-tangal bayan da jami'an DSS su ka kulle ofishin ta

Ana hasashen cewa shugabar Majalisar Dokokin Jihar Legas, Mojisola Meranda, na iya yin murabus a yau, a cewar majiyoyi.

Hakan na faruwa ne jim kadan bayan jami’an Hukumar Tsaro ta farin Kaya (DSS) sun kai mamaye ofishinta tare da kulle shi.

Daily Trust ta rawaito cewa majiyoyi sun bayyana cewa jami’an tsaro sun mamaye harabar majalisar da ke Alausa, Ikeja, da kewaye.

Wannan na zuwa ne makonni kadan bayan tsige tsohon kakakin majalisar, Mudashiru Obasa, wanda tsigewarsa ta haifar da rikici a majalisar, inda Obasa ya ki amincewa da hakan.

Ana hasashen cewa Obasa na iya komawa matsayin kakakin majalisar sak**akon shiga tsakani da Shugaba Bola Tinubu ya yi.

Ɓatan yara a Borno na karuwa yayin da ake zargin Boko Haram da daukar sabbin mayaka Batun ɓatan yara a Jihar Borno ya fa...
17/02/2025

Ɓatan yara a Borno na karuwa yayin da ake zargin Boko Haram da daukar sabbin mayaka

Batun ɓatan yara a Jihar Borno ya fara tayar da hankalin jama’a, bayan wani bidiyo ya fito ya na nuna wani yaro na furta cewa ana ba shi horo na soja a cikin daji tare da wasu yara da dama.

Wasu mazauna yankin da su ka zanta da The PUNCH a jiya Lahadi sun bayyana damuwarsu game da damuwa da su ke fuskanta na rashin sanin inda ‘yan uwansu su ke, tare da fargabar cewa karuwar yawan ɓatan yara a jihar na iya alaka da yunkurin mayar da su ‘yan ta’adda.

Wani faifen bidiyo na wani yaro mai kimanin shekara 10 da haihuwa da ya bayyana yana karbar horo kan amfani da mak**ai tare da wasu yara kusan 30 a cikin dajin Ajiri da ke karamar hukumar Mafa a Jihar Borno, ya karade kafafen sada zumunta a karshen mako.

Bidiyon, wanda wani mai suna Zagazola Mak**a ya wallafa a shafin X kuma aka ce an dauke shi a ranar 22 ga Janairu, 2025, ya nuna yaron yana kokarin nuna yadda ake sarrafa bindiga.

Ya bayyana cewa shi da sauran yara ana ba su horo a cikin daji mai zurfi.

Wasu mazauna yankin sun bayyana damuwarsu kan yadda ake fama da yawaitar batan yara a jihar, lamarin da suke tunanin yana da nasaba da bidiyon da ya karade intanet.

Aisha Ali, wata mazauniya Mafa, wadda ke kusa da dajin da ake zargin ana bautar da yaran, ta tabbatar da cewa danta mai shekara shida ya ɓace tsawon shekaru uku ba tare da an same shi ba.

Da Punch ta tuntubi rundunar ‘yan sanda ta jihar Borno, kakakin rundunar, Nahum Daso, ya ce ana samun rahoton batan yara akalla sau daya a kowane mako.

Sai dai a kan bidiyon, Daso ya ce ana iya amfani da tsofaffin bidiyo domin tayar da hankali.

Daily Nigerian Hausa

Wasu alƙaluma sun nuna an fara samun sauƙin kayan masarufi a wasu jihohin Nijeriya, sai dai da dama daga cikin masu saye...
17/02/2025

Wasu alƙaluma sun nuna an fara samun sauƙin kayan masarufi a wasu jihohin Nijeriya, sai dai da dama daga cikin masu sayen kayan masarufi na yau da kullum na korafi ragin ya kasa karasowa garesu sak**akon rashin saukaka farashi daga shagunan cikin unguwanni.

Ya abin yake a inda kuke ragin ya karaso muku?

Jam'iyyar APC Ta Lashe Kafatanin Zaɓen Shugabannin Kananan Hukumomin 34 Da Kansiloli 361 A Zaɓen Da Aka Gudanar A Jiya A...
16/02/2025

Jam'iyyar APC Ta Lashe Kafatanin Zaɓen Shugabannin Kananan Hukumomin 34 Da Kansiloli 361 A Zaɓen Da Aka Gudanar A Jiya Asabar

Daga Jamilu Dabawa, Katsina

Yanzu Yanzu:~ Babban Mawakin Hausa Naziru Sarkin Waka Tare Da Tawagarsa Sun Ziyarci SHEIK YUSUF SAMBO Rigachikun Domin T...
16/02/2025

Yanzu Yanzu:~ Babban Mawakin Hausa Naziru Sarkin Waka Tare Da Tawagarsa Sun Ziyarci SHEIK YUSUF SAMBO Rigachikun Domin Ta’aziyyan Rasuwan Alhaji Auwal Yusuf Sambo

MUTUMIN DA YAFI KOWA SHIGA GIDAN YARI SABODA SIYASA DAN JANI HADEJADaga Umar Dan JaniAlhaji Muhammadu Danjani Hadejia,  ...
16/02/2025

MUTUMIN DA YAFI KOWA SHIGA GIDAN YARI SABODA SIYASA DAN JANI HADEJA

Daga Umar Dan Jani

Alhaji Muhammadu Danjani Hadejia, tsohon shugaban NEPU, tsohon shugaban PRP, tsohon dan majalisar tarayya daga shekarar 1979 shine mahaifinmu.

Dani aka rubuta littafin tarihin rayuwarsa, bazan mantaba lokacin da muka ziyarci Dr Yusuf Bala Usman a gidsnsa dake Zaria, yayi matukar kaduwa lokacin da yaji ni dan cikin Danjani Hadejia ne.

Dr Yusuf Bala Usman yace mahaifinka yana zuwa ABU Zaria yana mana lectures, kuma suna daga dalilin rigingimunmu na fada da rashin gaskiya.

Dr Yusuf Bala Usman yace mun taba karrama Muhammadu Danjani Hadejia a matsayin mutumin da yafi kowa shiga gidan yari a harkar siyasa " Danjani as the most distinguished political prison graduate "

Lokacin da na ziyarci Hajiya Gambo Sawaba Allah yaji kanta , lokacin da abokin tafiya ta ya gabatar dani kawai sai ta barke da kuka, tana cewa Allah don girmanka don darajar ka kaji kan Danjani Hadejia, yaga bala'i kala kala akan kare mutuncin talakawa daga yan' mulkin malaka.

Haka Hajiya Asabe Reza tace anya za'a kara samun mutane irinsu su Danjani kuwa? Kawai sai ta barke da kuka, tace wallahi a gabana aka yiwa Danjani Hadejia bulala tamanin da daurin wata shida saboda ya fadi gaskiya kan wani Sarki.

Muda muka tashi dashi babu abin da ya ragemana na kyautatawa a duniya, wani lokaci da yake a gidan yari duk sanda aka kai masa ziyara duk yawanmu sai ya rubutowa kowa wasika.

Mahaifin mu saboda so da kauna yana kulle a Lagos Kiri kiri prison yabada umarni a siya mana babura don zuwa makaranta.

Baya wasa wajen Islamiyya, kuma tashi mukayi mukaga mutane daban daban a gidanmu, wadanda mahaifinmu ya ke daukar nauyinsu.

Mahaifinmu yasha bakar azaba a rayuwarsa, ya yi dawainiya damu yayansa da wadanda bashine ya haifesu ba.

Hakika munyi rashin uba, wallahi da girmana yana bani abinci a baki.

Ya Allah ka gafartawa marigayi Muhammadu Danjani Hadejia, insha Allahu zamuyi amfani da ranakun haihuwarsa don yi masa addu'oi da tambihin rayuwarsa.

Allah yaji kan Danjani Hadejia da sauran mazan jiya a wannan rana ta tunawa da ranar mahaifi ta Duniya.

'Yan Najeriya suna jin daɗin tasirin manufofin tattalin arzikin Tinubu: Sunday DareMai taimaka wa kan harkokin yada laba...
16/02/2025

'Yan Najeriya suna jin daɗin tasirin manufofin tattalin arzikin Tinubu: Sunday Dare

Mai taimaka wa kan harkokin yada labarai a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, Sunday Dare, a ranar Juma’a, ya ce a yanzu ‘yan Najeriya na jin dadin tasirin manufofin tattalin arzikin gwamnati.

"Tsarin tattalin arzikin Tinubu na ci gaba da yin tasiri ga tattalin arziki da kuma 'yan Najeriya," in ji Mista Dare a cikin wani sakon Twitter.

Ya kara da cewa, “Hauhawar farashin kayan abinci yana yin baya. Farashin manyan kayan abinci suna raguwa. Farashin man fetur yana daidaita."

Me zaku ce?

MUGU BAI DA K**ADaga Datti AssalafiySunansa Abdulrahman Muhammad Ballo, yana yin Facebook, ya hadu da wannan yarinya a F...
16/02/2025

MUGU BAI DA K**A

Daga Datti Assalafiy

Sunansa Abdulrahman Muhammad Ballo, yana yin Facebook, ya hadu da wannan yarinya a Facebook mai suna Hafsa Lawal inda s**a kulla soyayya s**ayi musayen nambar waya

Kwanaki shida da s**a wuce wato ranar 10-2-2025 Abdulrahman ya kira Hafsah akan su hadu, tunda daga wannan ranar aka nemeta aka rasa

'Yan sanda sun karbi nambar wayan Hafsah s**a duba last call da last location dinta wanda hakan ya taimaka aka gano da Abdulrahman tayi waya na karshe, sai akayi tracking dinsa aka k**ashi

Da farko ya musa cewa shi ya ka$heta, yace wai cutar asthma ne yayi aja|inta, da akaje searching gidansu sai aka tarar da g@warta a wani daki ya daddat$a ta ya cire wasu sa$$a na jik!nta

Irin wadannan abubuwa da suke faruwa ya k**ata ya zama babban darasi ga 'yan matan social media, ku shiga taitayinku, ku dinga sanin wadanda zaku hadu da su

Kuma ma imba lalacewa ba babu dalilin da zai sa mace budurwa tabi saurayi hotel ko gidansa, idan aure ne da gaske yake to ya je gidanki ba wai ke ki bishi ba

Allah Ya kare mu daga sharrin cin amanar wadanda muka basu aminci.

Duk Dan Siyasa Mai Tunani Ba Zai Shiga Jam'iyyar APC Ba, Sabida Kuncin Rayuwa Data Jefa Talakawa Ciki, Inji Aminu Waziri...
15/02/2025

Duk Dan Siyasa Mai Tunani Ba Zai Shiga Jam'iyyar APC Ba, Sabida Kuncin Rayuwa Data Jefa Talakawa Ciki, Inji Aminu Waziri Tambuwal

Me zaku ce ?

Daga Muhammad Kwairi Waziri

TIRƘASHI:~ Daga Shafin RFI HAUSA Wasu fusatattun mata da matasa a garin Maru dake Jihar Zamfarar Najeriya, sun bankawa g...
15/02/2025

TIRƘASHI:~ Daga Shafin RFI HAUSA Wasu fusatattun mata da matasa a garin Maru dake Jihar Zamfarar Najeriya, sun bankawa gidan Sarki wuta tare da ƙona motarsa, bayan wani ƙazamin harin da Ƴanta'adda s**a kai garin wanda ya kai ga kwashe mutane cikin su harda limamin garin. Rahotanni sun ce matan tare da matasa sun fusata ne saboda zargin da suke yiwa Sarkin, Alhaji Abubakar Gado, wanda aka fi sani da Banagan Maru na rashin ɗaukar kwararan matakai wajen kare jama'ar garin. Wasu majiyoyin da ba'a tabbatar ba, na zargin Sarkin da alaƙa da wasu Ƴanbindigar da s**a hana zaman lafiya a yankin daku Jihar Zamfara baki daya. Bayanai sun ce lokacin da Ƴanta'addan s**a shiga Maru, sun yi artabu sosai da matasan garin, amma saboda rashin isassun mak**ai aka fi karfin su, abinda ya kai ga ɗibar wasu mutanen garin cikin su harda Liman. Rahotanni sun ce bayan ƙura ta lafa ne, Sarkin Garin ya k**a hanyar zuwa gidan Liman jaje, matakin da ya fusata wasu jama'ar garin, musamman matan aure da matasan, waɗanda s**a afkawa motarsa da jifa aka kuma cinna mata wuta, har sanda jami'an Ƴansanda s**a kai masa ɗauki. Mun yi kokarin jin ta bakin Rundunar Ƴansandan Jihar Zamfara amma abin ya ci tura.

📷 Daily Trust

An yaye ƴansanda mata 1,511 a Akwa Ibom Rundunar Ƴansandan Najeriya a yau Asabar ta yaye jami’an ƴansanda mata su dubu 1...
15/02/2025

An yaye ƴansanda mata 1,511 a Akwa Ibom

Rundunar Ƴansandan Najeriya a yau Asabar ta yaye jami’an ƴansanda mata su dubu 1,511 da su ka ɗauki horo kan dabarun aiki domin inganta tsaron rayuka da dukiyoyi a Akwa Ibom.

Kwamishinan Ƴansanda na jihar, Baba Azare, ya bayyana cewa an yaye jami’an ne bayan wani horo mai zurfi na tsawon watanni uku a rundunar ƴansanda ta 26 da ke Uyo.

Azare ya bayyana cewa, an zabo jami’an ne daga dukkan sassan da ke karkashin rundunar ‘yansanda ta Akwa Ibom, inda ya bayyana horon a matsayin wani shiri na karfafa tsarin tsaro a jihar.

A cewarsa, an sake horas da jami’an mata 1,511 ne da nufin inganta tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin jihar da ma Najeriya baki daya.

Daily Nigerian Hausa

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fitila Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share