10/10/2025
TARIHIN ‘YAN BINDIGA A NAJERIYA
1. Ma’anar ‘Yan Bindiga
A kalmar Hausa, ‘yan bindiga na nufin mutanen da ke ɗaukar mak**ai (k**ar bindiga) suna sata, garkuwa da mutane, ko kai hare-hare domin neman kuɗi ko wani buri na siyasa ko ƙabilanci.
A turance ana kiran su da “bandits”.
Su ba kungiya ɗaya ce ba, amma rukuni-rukuni ne na mutane dake aiki a dazuka daban-daban, musamman a Arewa maso yamma da tsakiyar Najeriya.
2. Asalin Matsalar
Tashin hankalin ‘yan bindiga ya fara bayyana a hankali bayan shekarar 2010, musamman a jihohin:
Zamfara, Katsina, Kaduna, Niger, Sokoto, Kebbi, da wasu sassan Plateau da Nasarawa.
Asalin matsalar ta samo tushe daga abubuwa k**ar:
Rashin tsaro da ayyukan satar shanu (cattle rustling),
Rashin aikin yi da talauci,
Rikice-rikicen manoma da makiyaya,
Rashin adalci a rabon arziki,
Da kuma rashin hukunta masu laifi a baya.
Da farko, matsalar ta fara ne da satar shanu da satar kaya, daga baya ta rikide zuwa sace mutane domin kudin fansa.
3. Yadda Rikicin Ya Tsananta
Daga shekara ta 2014 zuwa 2018, matsalar ta ƙara ta’azzara.
‘Yan bindiga sun fara kai hare-hare kan:
Kauyuka da gidajen manoma,
Hanyoyin mota (road attacks),
Masu noma da makiyaya,
Da kuma jami’an tsaro.
A wannan lokaci ne aka fara samun garkuwa da mutane da yawa a lokaci guda, har wasu makarantu da dalibai ke zama abin hari.
Misalai:
Sace daliban makaranta a Kankara, Katsina (2020)
Tegina, Niger State (2021)
Birnin Yauri, Kebbi (2021)
Kaduna–Abuja Train Attack (2022)
4. Dalilan Dake Kawo Faruwar Matsalar
Masana sun bayyana wasu muhimman dalilai k**ar:
1. Talauci da rashin aikin yi yawancin matasan da s**a shiga suna cikin tsananin talauci.
2. Rashin ilimi, rashin wayewa yasa suna yarda da jagororinsu.
3. Rashin tsaro da hukunci, babu tsauraran matakai akan masu laifi.
4. Rashin daidaito a rabon arziki, wasu suna ganin gwamnati tafi kula da wasu yankuna fiye da wasu.
5. Fadace-fadace tsakanin manoma da makiyaya, wanda ya rikide zuwa makami.
5. Yankunan Da Matsalar Tafi Kamari
Zamfara State shine asalin yankin da ‘yan bindiga s**a fara kafa sansanoni da yawa a dazukan Dansadau, Tsafe, da Maru.
Katsina da Niger suna fama da hare-haren da s**a shafi sace mutane da kona kauyuka.
Kaduna da Sokoto, hare-haren kan hanya da garkuwa da matafiya.
A wasu wurare, suna kafa sansanoni a cikin daji, suna gudanar da harkokin su k**ar ƙungiya.
6. Ire-iren Ayyukan Su
‘Yan bindiga suna aikata abubuwa da dama k**ar:
Satar mutane domin kudin fansa,
Kona gidaje da kauyuka,
Satar shanu da dukiyoyi,
Kashe jama’a idan aka ƙi biyan fansa,
Tursasa jama’a su bar garuruwansu.
Wasu daga cikinsu ma suna da mak**ai masu ƙarfi, k**ar AK-47, RPG, da motoci masu bindiga.
7. Martanin Gwamnati
Gwamnatin Najeriya ta dauki matakai daban-daban, ciki har da:
Ayyukan soji da ‘yan sanda, k**ar Operation Sharan Daji, Operation Hadarin Daji, da Operation Whirl Stroke.
Takaita cinikin man fetur da wayoyi a wasu yankuna domin hana su samun kayan aiki.
Kiran zaman lafiya da tattaunawa da wasu gwamnoni s**a yi, amma bai dawwama ba.
Kulle kasuwanni da hana amfani da babura (okada) a wasu jihohi.
Duk da haka, har yanzu matsalar bata gushe gaba ɗaya ba.
8. Sak**akon Matsalar
Rikicin ‘yan bindiga ya jawo:
Mutuwar dubban mutane,
Raba miliyoyin jama’a daga gidajensu,
Rashin aikin noma a yankunan karkara,
Karuwar talauci da yunwa,
Durkushewar tattalin arzikin Arewa maso yamma.
9. Hanyoyin Magance Matsalar
1. Wayar da kan matasa da ilimi.
2. Kirkirar ayyukan yi da tallafi a karkara.
3. Karfafa shari’a da hukunta masu laifi cikin gaskiya.
4. Kulla zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya.
5. Taimakawa al’umma su samu tsaro ta hanyar sa ido da hadin kai da jami’an tsaro.
10. Kammalawa
Tarihin ‘yan bindiga a Najeriya ya nuna cewa rashin adalci, talauci, da rashin tsaro sune tushen matsaloli.
Amma idan aka tashi da niyyar gaskiya, haɗin kai, da ilimi za'a iya kawo ƙarshen wannan fitina.
Zaman lafiya ba zai tabbata ba sai an magance talauci, rashin ilimi, da rashin adalci.
Allah ya kawo mana zaman lafiya mai dorewa a wannan qasar tamu mai albarka, Ameen.
In shaa Allah ana muka kawo qarshen wannan darasin namu na tarihi, zamuyi tunani muga wani darasi zamu dauko nan bada jimawa ba in shaa Allah.
✍️: Muhammad Khalid Hussaini
(De GENERAL)
10/10/2025