Hausa24

Hausa24 HAUSA24, Za Ta Kasance Wata Kafar Yada Labarai Da Za Take Kawo Muku Labarai Da Dumi-Dumin Su, Cikin Harshen Hausa!

Fagen harkar yada labarai fage ne mai fadin gaske, da dama sun zo sun tafi bayan sunyi abinda s**a yi, wasu ma sun zo basu yi komai ba sun tafi ba tare da ko labarinsu an ji ba. Mun sani kuma mun aminta igiya biyu ce kadai za ta iya rike mu, har mu ma muyi abinda muka yi. Wadannan igiyoyi su ne: GASKIYA da GOYON BAYANKU, za mu rayuwa idan har akwai wadannan igiyoyi. H24 za ta zamo wata takar yakin

Hausawa ‘yan Nijeriya, domin yakar karya da kare gaskiya a kodayaushe, koda kuwa a hannu masu mulki ne. Ta haka ne kadai za mu cimma burinmu da naku baki daya.

HOTUNA | Yadda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) kuma Gwamnan...
06/06/2026

HOTUNA | Yadda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) kuma Gwamnan Jihar Kwara, Malam AbdulRahman AbdulRazaq; Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris; tsohon Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Umar Ganduje, da Ministan Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari, tare da sauran manyan baƙi suna daga cikin fitattun mutanen da s**a halarci sallar Juma’a ta musamman a jiya da aka gudanar domin bikin Ranar Dimokiraɗiyya ta bana. An gudanar da wannan zaman addu’a ne a ranar Juma’a, 5 ga Yuni, 2026, a Masallacin Ƙasa da ke Abuja.

Hasbunallahu Wani'imal wakeel | Babban Malamin addini Sheikh Nuru Khalid wanda aka fi sani da (Digital Imam) ya kamu da ...
05/06/2026

Hasbunallahu Wani'imal wakeel | Babban Malamin addini Sheikh Nuru Khalid wanda aka fi sani da (Digital Imam) ya kamu da matsananciyar rashin lafiya a Makka bayan kammala aikin Hajji wanda ya kai ga an saka masa na'urar numfashi ta bada nunfashi (Oxygen)

Ya nemi da a taya shi da addu'a.

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kan jama’a da hukumomin tsaro wajen yaƙi da ta’addanciGwamnatin Tarayya ta yi kira ga ...
05/06/2026

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kan jama’a da hukumomin tsaro wajen yaƙi da ta’addanci

Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ’yan Nijeriya da kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula da hukumomin tsaro da su ƙarfafa haɗin gwiwa a tsakanin su wajen yaƙi da ta’addanci da sauran nau’o’in tsauraran ra’ayoyi da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja a wajen wani babban taron manema labarai.

Ya ce yaƙi da ta’addanci yana buƙatar haɗin kan ƙasa baki ɗaya ba tare da la’akari da bambance-bambancen siyasa da ƙabila da addini ko yanki ba.

Ministan ya ce: “Gwamnatin Tarayya tana kira ga ’yan ƙasa da kafafen yaɗa labarai da hukumomin tsaro da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci, domin duk wani hari da aka kai wa ɗan Nijeriya ɗaya tamkar an kai shi ne ga dukkan ’yan Nijeriya. Ta’addanci ba ya da ƙabila ko addini ko wata alaƙa da siyasa. Manufar sa ita ce haddasa ɓarna kawai.”

Ya bayyana cewa wannan ne ya haifar da ƙaddamar da gangamin , wanda ke kira ga dukkan ’yan Nijeriya da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci da sauran laifuffuka.

Idris ya kuma tabbatar wa da ’yan Nijeriya cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana ci gaba da ƙoƙarin ganin an ceto dukkan ɗalibai da malamai da aka sace a hare-haren da s**a faru a jihohin Oyo da Borno.

Ya ce: “Ina so in tabbatar wa da dukkan ’yan Nijeriya cewa dawo da kowane yaro da kowane malami da ke hannun masu garkuwa cikin ƙoshin lafiya yana ci gaba da kasancewa babban fifikon gwamnati. Shugaban Ƙasa ya bayyana ƙarara cewa babu wani yaro da ya kamata ya kasance a tsare, kuma gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa an gurfanar da masu hannu a waɗannan munanan laifuffuka a gaban shari’a.”

Ministan ya bayyana cewa hukumomin tsaro sun ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri da gudanar da sintiri da kuma ayyukan ceto domin kuɓutar da waɗanda aka sace tare da hukunta masu hannu a lamarin.

Ya ce dakarun rundunar "Operation Hadin Kai" sun samu nasarori a Arewa-maso-gabas, inda s**a kashe 'yan ta’adda da dama tare da lalata sansanonin su da kuma ceto fararen hula.

A cewar sa, ayyukan tsaro a yankunan Arewa-maso-yamma da Arewa-ta-tsakiya da Kudu-maso-gabas da Kudu-maso-kudu sun taimaka wajen rusa sansanonin masu aikata laifi da tarwatsa ƙungiyoyin masu garkuwa da mutane da kuma ƙara kare muhimman kadarorin ƙasa.

Idris ya ce nasarorin da ake samu a yaƙi da ta’addanci suna da alaƙa da ingantaccen haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da musayar bayanan sirri da amfani da fasahar zamani da kuma haɗin gwiwa da ƙasashen waje.

Ya ce: “Abin da ya bambanta wannan tsarin da muke amfani da shi a yanzu shi ne haɗa matakan soji da ayyukan da s**a dogara da bayanan sirri da amfani da fasahar zamani da haɗin gwiwa tsakanin yankuna da kuma sa hannun al’umma. Wannan cikakken tsari yana ci gaba da raunana ƙarfin ƙungiyoyin ’yan ta’adda da masu aikata laifuffuka.”

Ministan ya kuma yi nuni da nasarorin da aka samu a ɓangaren shari’a, ciki har da hukuncin da aka yanke wa waɗanda aka samu da hannu a harin ta’addancin da aka kai Cocin St. Francis da ke Owo a Jihar Ondo a watan Yuni 2022.

Ya ce Gwamnatin Tarayya ta kuma fara ɗaya daga cikin manyan shari’un masu laifin ta’addanci a tarihin ƙasar nan, inda ɗaruruwan waɗanda ake zargi suke fuskantar shari’a.

Ya ce: "Adalci yana daga cikin muhimman ginshiƙan tsaron ƙasa. Bayan matakan soji, gwamnati tana tabbatar da cewa duk masu hannu a ayyukan ta’addanci sun fuskanci hukuncin doka. Shari’un da ake yi wa waɗanda ake zargi da ta’addanci da kuma hukuncin da aka yanke wa wasu daga cikin su na aika saƙo ƙarara cewa ba za a ƙyale masu laifi su tsira daga hukunci ba.”

Ministan ya yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ci gaba da bin ƙa’idojin aikin jarida wajen rahoto kan al’amuran ta’addanci.

Ya ce: “Yayin da ya kamata kafafen yaɗa labarai su ci gaba da bayar da rahotanni cikin sahihanci da nuna ƙwarewa, dole ne mu yi taka-tsantsan kada mu taimaka wa ’yan ta’adda wajen cimma manufofin su ba tare da sani ba. Aikin jarida mai ɗa’a na iya hana su samun irin shaharar da suke nema, tare da tabbatar da cewa jama’a sun samu sahihan bayanai.”

Ya buƙaci ’yan Nijeriya da su kasance masu sa ido tare da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai, sannan su guji yaɗa duk wani saƙo da ke ƙoƙarin haddasa rarrabuwar kai ta fuskar ƙabila ko addini ko siyasa.

Ministan ya sake jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a har sai an kawo ƙarshen ta’addanci da sauran munanan laifuffuka.

“Nijeriya ta sha fuskantar lokuta masu wuya a baya kuma ta fito daga cikin su da ƙarfin ta. Haka nan za mu shawo kan wannan ƙalubale. Idan muka haɗa kai tare da tsayawa tsayin daka kan manufar mu, za mu tabbatar da cewa ta’addanci ba shi da makoma a Nijeriya."

Taron ya samu halartar Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Dakta Binyerem Ukaire; Sufeto-Janar na ’Yan Sanda wanda jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya wakilta; Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Soji, Janar Sama'ila Uba, da wasu manyan jami’an gwamnati da masu ruwa da tsaki a lamarin.

Tsarin Kafa ’Yan Sandan Jihohi Ya Kusa Kammaluwa — inji Fadar Shugaban ƘasaFadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa an samu g...
05/06/2026

Tsarin Kafa ’Yan Sandan Jihohi Ya Kusa Kammaluwa — inji Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba a tattaunawar kafa rundunar ’yan sandan jihohi, inda ake sa ran gabatar da gyaran kundin tsarin mulki nan ba da jimawa ba domin ba da damar aiwatar da shirin.

Babban Ma’aikacin Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ne ya bayyana hakan bayan wata ganawa da aka yi a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja ranar Alhamis, wadda ta haɗa manyan jami’an gwamnati da shugabannin majalisun dokoki kan batun kafa ’yan sandan jihohi.

Gbajabiamila ya ce an fara nazari da tattaunawa kan yadda za a kafa rundunar tun watanni uku zuwa huɗu da s**a gabata bisa umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kuma an samu ci gaba mai yawa a aikin.

Ya bayyana cewa kafa ’yan sandan jihohi ba abu ne da za a yi cikin gaggawa ba, domin akwai batutuwan kundin tsarin mulki da dokoki da dole ne a tantance su sosai kafin aiwatarwa.

A cewarsa, yanzu hankalin masu ruwa da tsaki ya karkata ne kan yadda za a yi gyaran kundin tsarin mulki, sannan daga baya a samar da dokokin da za su ba da cikakken iko da tsarin gudanar da rundunar.

Ya ƙara da cewa mafi yawan ’yan Najeriya da masu ruwa da tsaki sun amince da bukatar kafa ’yan sandan jihohi, inda muhawarar yanzu ba ta kan ko a kafa su ko a’a ba, sai dai yadda za a samar da ingantaccen tsarin doka da gudanarwa domin su yi aiki yadda ya kamata.

Gbajabiamila ya ce za a gabatar wa Shugaba Tinubu cikakken rahoto kan sakamakon ganawar domin ci gaba da matakan da s**a dace.

A cewarsa, manufar kafa ’yan sandan jihohi ita ce ƙarfafa tsaron cikin gida, inganta tattara bayanan sirri daga matakin ƙasa da kuma bai wa gwamnatocin jihohi damar magance matsalolin tsaro cikin sauri da inganci.

Shugaba Tinubu ya sha bayyana cewa tsarin ’yan sandan jihohi na daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen fuskantar ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasar nan, tare da ƙara kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ganawar ta samu halartar Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau I. Jibrin; Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu; Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Lateef Fagbemi; da Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Tunji Disu, tare da sauran manyan jami’an gwamnati.

YANZU-YANZU: Kamar yadda jaridar Ayau ta wallafa  Masu zanga-zanga sun kusa shiga harabar fadar shugaban kasa duk da tul...
04/06/2026

YANZU-YANZU: Kamar yadda jaridar Ayau ta wallafa Masu zanga-zanga sun kusa shiga harabar fadar shugaban kasa duk da tulin jami’an tsaro da aka jibge

Rahoton ICR ya nuna cewa masu zanga-zangar na cigaba da samun karin mutane da yawa wanda a yanzu haka har sun kai harabar ginin sakatariyar Gwamnatin Tarayya dake kusa da fadar Shugaban kasa ta A*o Villa, suna neman sai an sako duka mutanen Najeriya da yan bindiga ke rike da su

Sannan kuma suna son shugaban Ƙasa Tinubu ya sauka nan take saboda ya gaza daqile matsalar tsaro

Me zaku ce?

YANZU-YANZU | Kiciɓus mugun gamo, yau sai gashi an haɗu da Rarara da Sarkin Waka a jirgi daya yayin dawowar su daga Abuj...
03/06/2026

YANZU-YANZU | Kiciɓus mugun gamo, yau sai gashi an haɗu da Rarara da Sarkin Waka a jirgi daya yayin dawowar su daga Abuja

YANZU-YANZU |  Wani Bawan Allah daga Jihar Yobe ya gwangwaje tsohon daraktan fina - finan Hausa Ashiru Nagoma da sabon m...
03/06/2026

YANZU-YANZU | Wani Bawan Allah daga Jihar Yobe ya gwangwaje tsohon daraktan fina - finan Hausa Ashiru Nagoma da sabon machine roba- roba yaban tabbatar da samun lafiyarsa daga jinyar daya samu a shekarun baya.

Furodusa Abubakar Bashir Maishadda ne ya gabatar masa da babur ɗin a yau Laraba a Kano.

YANZU - YANZU | Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Shalkwatar Hukumar 'Great Green Wall' Zuwa Kano Don Inganta AikiGwamnatin ...
03/06/2026

YANZU - YANZU | Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Shalkwatar Hukumar 'Great Green Wall' Zuwa Kano Don Inganta Aiki

Gwamnatin Tarayya ta ɗauki gabarar daidaita ayyukan hukumar yaƙi da kwararar hamada ta kasa, wato National Agency for the Great Green Wall (NAGGW), inda ta mayar da babban ofishinta na gudanar da ayyuka daga birnin tarayya Abuja zuwa jihar Kano.

Ministan Muhalli, Balarabe Abbas Lawal, ne ya bayyana hakan, inda ya bayyana cewa matakin na kunshe ne a karkashin tsarin 'Renewed Hope Agenda’ na Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Manufar hakan ita ce tallafa wa hukumar don ta gudanar da ayyukanta cikin hanzari da nagarta a jihohin da abin ya shafa.

Shirin na 'Great Green Wall' babban yunkuri ne na Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) da ya kunshi kasashe 11, da nufin yaki da kwararar hamada, lalacewar kasa, da kuma radadin sauyin yanayi a yankin Sahel da Sahara.

A nan Najeriya, shirin ya karkata ne a kan jihohi 11 na gaba-gaba da hamada ke barazana musamman ga rayuwarsu, wadanda s**a hada da: Bauchi, Borno, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kebbi, Sokoto, Yobe, Zamfara, da kuma Adamawa.

Ministan ya kara da cewa, babban burin hukumar shi ne shimfida dangar bishiyoyi (Green Wall) mai nisan kilomita 15 a fadi, da kuma tsawon kilomita 1,500 domin kare muhalli, rage radadin sauyin yanayi, samar da wadatar abinci, da kuma rage radadin talauci a karkara.

Tun lokacin da aka kaddamar da shirin a shekarar 2013, kafin daga bisani a mayar da shi cikakkiyar hukuma a 2015, an samu manyan nasarori kamar haka:

Kafa dangar kariya daga iska da yashi (shelterbelts) fiye da guda 100.

Gina madatsun ruwa na sola da iskar gas guda 159 don samar da ruwan sha.

Daukar matasa guda 600 a matsayin dogaran daji (forest guards).

Samar da gonakin bishiyoyin itatuwa na (orchards and woodlots) guda 240 don bunkasa kudin shiga.

Malam Balarabe Abbas Lawal ya jaddada cewa, wannan sauyi zai magance kalubalen da hukumar ta dade tana fuskanta na gudanar da ayyuka daga ofishin haya a Abuja, wanda ke nesa da ainihin inda ayyukan suke a Arewa. Komawa Kano, wadda ita ce cibiyar yankunan da ayyukan s**a shafa, zai ba da damar sanya ido, da samar da kyakkyawar alaka tsakanin gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, da al'ummomin yankunansu.

Jihar Kano riga ta saba da irin wadannan ayyuka, domin tana dauke da ofishin tsara shirye-shiryen dashen bishiyoyi (APCU) tun a shekarar 1988, wanda yanzu ba a amfani da shi yadda ya kamata tun bayan kammala shirin Bankin Duniya na dashen bishiyoyi a yankunan fari (Arid Zone Afforestation Programme) a shekarar 1996. Wannan cigaba a yanzu zai cigaba a hukumar ta NAGGW.

Daga karshe, Ministan ya bayyana yakinin cewa wannan mataki na kusanto da hukumomi kusa da inda suke aiki zai kawo sauyi na gaske ga rayuwar miliyoyin 'yan Najeriya da ke zaune a yankunan da kwararar hamada ke addaba.

02/06/2026

BIDIYO: Yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dawo Abuja a yau bayan kammala bukukuwan babbar sallah a mahaifarsa, Legas.

- M Information

LABARI | Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yada Labarai ga Shugaba Tinubu, Malam Abdulaziz Abdulaziz, Yayi Karin...
01/06/2026

LABARI | Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yada Labarai ga Shugaba Tinubu, Malam Abdulaziz Abdulaziz, Yayi Karin Haske Kan Daukar Masu Tsaron Daji 1,000 a Jihar Oyo.

Tun jiya da jaridu s**a fara bada labarin aniyar ɗaukar masu tsaron daji (Forest Guards) guda 1,000 a jihar Oyo sakamakon kidnapping da aka yi kwanaki na lura wasu mutanenmu na Arewa a Social Media suna ƙorafi ko shaguɓen cewa "an taɓa ƴan gata". A ganin su wannan abu ne kawai za a yi domin Yarabawa saboda matsalar tsaro ta shafe su. To ba haka ba ne.

A yanzu haka akwai jihohi 10 da aka kafa rundunar Forest Guards da kuma jihohi duk a Arewa. Kuma kowanne an ɗauki mutum kimanin 1,000 ɗin ne.

Jihohin da suke da Forest Guards:
1. Borno
2. Yobe
3. Adamawa
4. Kwara
5. Sokoto
6. Kebbi
7. Niger
8. Plateau
9. Benue

Wanda suke kan hanya
1. Kaduna
2. Edo
3. Kogi
4. Bauchi

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa24:

Share