Hausa24

Hausa24 HAUSA24, Za Ta Kasance Wata Kafar Yada Labarai Da Za Take Kawo Muku Labarai Da Dumi-Dumin Su, Cikin Harshen Hausa!

Fagen harkar yada labarai fage ne mai fadin gaske, da dama sun zo sun tafi bayan sunyi abinda s**a yi, wasu ma sun zo basu yi komai ba sun tafi ba tare da ko labarinsu an ji ba. Mun sani kuma mun aminta igiya biyu ce kadai za ta iya rike mu, har mu ma muyi abinda muka yi. Wadannan igiyoyi su ne: GASKIYA da GOYON BAYANKU, za mu rayuwa idan har akwai wadannan igiyoyi. H24 za ta zamo wata takar yakin

Hausawa ‘yan Nijeriya, domin yakar karya da kare gaskiya a kodayaushe, koda kuwa a hannu masu mulki ne. Ta haka ne kadai za mu cimma burinmu da naku baki daya.

JAWABIN TINUBU KAN TSARO A YAYI JAWABIN KASA NA CIKA 65. Muna aiki tukuru don inganta tsaron kasa, don tabbatar da cewa ...
01/10/2025

JAWABIN TINUBU KAN TSARO A YAYI JAWABIN KASA NA CIKA 65.

Muna aiki tukuru don inganta tsaron kasa, don tabbatar da cewa tattalin arzikinmu ya samu ingantaccen ci gaba. Dakarun sojojinmu da sauran hukumomin tsaro suna aiki ba dare ba rana, suna sadaukar rayuwarsu don kiyaye rayukanmu da dukiyoyin mu. Kuma suna cin nasara a yakin da muke yi da ta'addanci, fashi, da ma sauran manyan laifuka.

Muna ganin nasarorin su a cikin jinin su da gumin su don kawar da Ta'addancin Boko Haram a Arewa maso Gabas, ta'addancin IPOB/ESN a Kudu maso Gabas da fashi da garkuwa da mutane. Dole ne mu ci gaba da yaba musu da jinjinawa jaruntakarsu a matsayinmu na al'ummar da ke yaba kyauta da tukuici. Zaman lafiya ya dawo ga daruruwan al'ummominmu da aka 'yanta a Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas, kuma dubban mutanenmu sun dawo gida lafiya.

KAJI RABO:| Tsohon mai taimakawa mirgayi shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari kan kafafen sadarwa na zamani Bashir Ahmad, ya g...
30/09/2025

KAJI RABO:| Tsohon mai taimakawa mirgayi shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari kan kafafen sadarwa na zamani Bashir Ahmad, ya ginawa wani bawan Allah gida bayan anyi sanarwar neman taimako a Facebook..

Me zaku ce ?

29/09/2025

BURIN TINUBU SHINE SAMAR DA ADALCI WA YAN NIJERIYA.

Burin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu shine kowanne ɗan Najeriya ya samu abin daya kamata, ya samu na romon dimokuraɗiyya a matsayin sa na ɗan Najeriya, ko tafannin ilimi, kiwon lafiya, harkar noma, ko kasuwanci da kuma sauran harkoki na ra yuwa na yau da kullum

- ⁠Ministan Labarai da Wayar da Kai Mohammed Idris.

_ Shu'aib kabir..

Gwamnatin Tarayya naci gaba da aikin haƙo rijiyoyin mai guda uku a yankin Kolmani na jihohin Bauchi da Gombe. Gwamnatin ...
29/09/2025

Gwamnatin Tarayya naci gaba da aikin haƙo rijiyoyin mai guda uku a yankin Kolmani na jihohin Bauchi da Gombe. Gwamnatin ta mai da hankali sosai kan wannan aiki, Inji Ministan yaɗa Labarai da Wayar da Kai Mohammed Idris

27/09/2025

SHEKARU 65 DA SAMUN YANCIN KAI.

Tinubu Ya Buƙaci Ƙarin Haɗin Kai Yayin Da Nijeriya Ke Cika Shekara 65 da Samun ’Yancin Kai

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su zauna cikin haɗin kai da zaman lafiya domin cigaban ƙasa baki ɗaya.

Wata sanarwa da Dakta Suleiman Haruna, Daraktan Hulɗa da Jama’a na Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, ya sanya wa hannu, ta ce Shugaban Ƙasar ya bayyana hakan ne a ranar Juma'a a Babban Masallacin Ƙasa da ke Abuja, a lokacin sallar Juma’a ta musamman da aka shirya a matsayin wani ɓangare na bukukuwan cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai.

Shugaban Ƙasa, wanda Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya wakilta, ya bayyana cewa Nijeriya za ta iya cika mafarkin ubannin ƙasa ne kawai idan ’yan ƙasa sun zauna cikin zaman lafiya, sun jure bambance-bambancen su, kuma sun dage wajen aiki tuƙuru.

Ya ce: “A ko yaushe akwai bambance-bambance, amma saƙon Shugaban Ƙasa na fata, haɗin kai da zaman tare ne. Dole ne dukkan ’yan Nijeriya su rungumi waɗannan ɗabi’u yadda tare za mu samu cigaba da wadata da Shugaban Ƙasa ya yi alƙawari tun bayan hawan sa mulki.”

Ya ƙara da cewa ko da yake ƙasar nan tana cikin wani yanayi na sauyi, gwamnatin Tinubu tana samun cigaba a hankali wajen shawo kan matsalolin da ake fuskanta.

Ya yi kira ga ’yan ƙasa da su yi haƙuri yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin juya halin da tattalin arzikin ƙasa yake ciki.

Yayin da yake taya ’yan Nijeriya murnar cikar ƙasar nan shekara 65 da samun ’yancin kai, Shugaban ya roƙe su da su ci gaba da yin addu’a ga shugabanni da ƙasa domin samun makoma mai haske.

Dangane da taken bikin na bana, wato “Nijeriya a 65: A Haɗa Kai Don Gina Ƙasa Mafi Girma,” ministan ya ce Shugaban Ƙasa na kira ga ’yan Nijeriya gaba ɗaya, ba tare da la’akari da ƙabila, addini, bambancin siyasa ko matsayi ba, da su haɗa kai domin gina Nijeriya wadda muke mafarki da ita.

Ya kuma lissafa wasu nasarori da gwamnatin Tinubun ta samu, inda ya ce Nijeriya ta samu gagarumin cigaba a ɓangarorin tattalin arziki, tsaro, noma, da kuma wasu muhimman sassa.

Ya ce: “Abin da ake buƙata yanzu shi ne ’yan Nijeriya su yi aiki tare.”

Ya kuma yi wa al’ummar ƙasa fatan a yi bukin cikin zaman lafiya da murna.

Ministan Noma da Bunƙasa Ƙarkara, Alhaji Mohammed Abubakar Kyari, wanda ya halarci sallar Juma’ar, ya ce Nijeriya tana kan hanyar dawo da martabar da ta rasa a idon ƙasashen duniya.

Shi kuma Etsu Nupe wanda shi ne Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Neja, Mai Martaba Alhaji Yahaya Abubakar, wanda tare da shi aka yi sallar, ya yi kira ne da a zauna lafiya, kuma ya yi addu’ar samun wadata da cigaban ƙasa a wannan cikar Nijeriya shekara 65 da zama 'yantacciya.

26/09/2025

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya isa Ibadan, babban birnin jihar Oyo, domin halartar nadin sarauta na Mai Martaba Rashidi Adewolu Ladoja a matsayin Olubadan na Ibadan na 44.

DA DUMI-DUMI: Masarautar Daura ta amince da nada Rarara Sarkin Wakar Kasar Hausa. Mai zaku ce ?
25/09/2025

DA DUMI-DUMI: Masarautar Daura ta amince da nada Rarara Sarkin Wakar Kasar Hausa.

Mai zaku ce ?

NAJERIYA TA NEMI KUJERAR DINDINDIN A KWAMITIN TSARO NA MAJALISAR DINKIN DUNIYA.Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya sake jaddad...
25/09/2025

NAJERIYA TA NEMI KUJERAR DINDINDIN A KWAMITIN TSARO NA MAJALISAR DINKIN DUNIYA.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya sake jaddada bukatar a bai wa Najeriya kujerar dindindin a Kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, a matsayin ɓangare na sauye-sauyen da ake son yi wa tsarin majalisar.

Tinubu, wanda Mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima, ya wakilta, ya yi wannan kira ne a lokacin da yake jawabi a zauren tattaunawa na babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 80 a birnin New York.

“Ya zama dole Najeriya ɓ ta samu kujerar dindindin a Kwamitin tsaro. Wannan wani muhimmin ɓangare ne na sauye-sauye domin dawo da amincewa ga wannan hukuma, wacce ita ce ginshikin tsarin haɗin gwiwa na duniya,” in ji shi.

Shugaban ya ce Majalisar Dinkin Duniya za ta dawo da martabarta ne kawai idan ta dace da yanayin duniya na yanzu, ba ta bar tarihi ya daure ta ba.

Ya bayyana cewa lokacin da aka kafa Majalisar Dinkin Duniya, Najeriya ƙasa ce ƙarƙashin mulkin mallaka mai mutane miliyan 20, ba tare da samun wakilci a teburin da ake yanke hukunci kan makomarta ba.

“Yanzu kuwa, mu ƙasa ce mai ‘yanci, muna da fiye da mutane miliyan 236, kuma an yi hasashen nan da shekaru masu zuwa mu zama ƙasa ta uku mafi yawan jama’a a duniya. Najeriya ta dade tana zama ginshikin tsaro a nahiyar Afirka, kuma abar dogaro a aikin kiyaye zaman lafiya na duniya,” in ji Tinubu.

Ya bayyana cewa sojojin Najeriya sun taka rawa a cikin ayyuka 51 daga cikin 60 na kiyaye zaman lafiya da Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar tun bayan samun ‘yancin kai a 1960.

Shugaban ya kuma ce ƙasar ba ta tsaya ga kanta ba wajen yakar ta’addanci, inda ta yi aiki tare da makotan ƙasashen Afirka ta hanyar Multinational Joint Task Force (MNJTF).

Tinubu ya ce Najeriya ta koyi darasi daga doguwar gwagwarmaya da ta yi da ƙungiyoyin tsattsauran ra’ayi.

Ya kuma ce dalilin da ya sa Najeriya ke magana kan rikicin Gaza, harin da aka kai Qatar da sauran tashin hankula a yankin shi ne saboda ƙwarewar da ƙasar ta samu daga irin wannan rikice-rikice da ba sa ƙarewa inda aka fara.

Shugaban ya ƙara da cewa Najeriya tana goyon baya ga shirin babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na UN80 Initiative, wanda ya yi kira da a sauya tsarin hukumar domin ya dace da zamani, a kuma kawo ƙarshen maimaita ayyuka da ɓata kuɗi.

AN GUDANAR DA JANA'IZAR KARE.Daga, Suwidi Sunusi Gaya.A safiyar laraba da misalin ƙarfe 8:00 na safe, al’ummar garin Mah...
25/09/2025

AN GUDANAR DA JANA'IZAR KARE.

Daga, Suwidi Sunusi Gaya.

A safiyar laraba da misalin ƙarfe 8:00 na safe, al’ummar garin Mahuta dake Kabo jihar Kano sun gudanar da jana’iza tare da binne wani kare mai suna 'Wizzy', mallakin marigayi Abdullahi ɗan Alhaji (wanda aka fi sani da Cuwa Cuwa).

Bayan kammala binne karen, jama’a da dama ne s**a halarta tare da yin addu’o’in na neman rahama ga mamallakin kare, marigayi Abdullahi.

Rahotanni sun nuna cewa matasa masu dawa dama ne s**a halarci binne karen ne s**a, ciki har da shugaban ‘yan Vigilante na garin Mahuta, Ado Usman Mahuta, kasancewar karen ya zama zakaran gwajin dafi wajen wayar da tsaro a yankin.

Al’umma sun bayyana alhininsu tare da addu’ar Allah ya musanya musu da mafi alkhairi.

Allah ya kyauta.

Gwamnatin Najeriya ta jaddada matsayar ta na tabbatar da yancin ƙasar Falasɗinu a Majalisar Dinkin DuniyaGwamnatin Taray...
25/09/2025

Gwamnatin Najeriya ta jaddada matsayar ta na tabbatar da yancin ƙasar Falasɗinu a Majalisar Dinkin Duniya

Gwamnatin Tarayya ta Najeriya ta bayyana cewa, mafita ta samar da ƙasashe biyu ita ce hanya mafi kyau da za ta kawo dawwamammen zaman lafiya ga al’ummar Falasdinu.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda Mataimakin sa, Kashim Shettima, ya wakilta, ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 80 a birnin New York.

Tinubu ya ce: “Ba mu yarda da ganin rayuwar ɗan Adam ta makale cikin jayayya marar ƙarewa ba. Shi ya sa muke tsayawa ba tare da shakka ba, muna cewa mafita ta samar da ƙasashe biyu masu yancin kan su ita ce hanya mafi kyau ga zaman lafiya a Falasdinu.”

Ya ƙara da cewa da daɗewa al’ummar Falasdinu suna fuskantar rikice-rikicen da s**a jawo zubar da jini da tashin hankali.

“Ba mu zo a matsayin masu ɓangaranci ba, mun zo ne a matsayin masu burin kawo maslaha. Mun zo a matsayin ‘yan’uwa a duniyar da bai kamata ta rage darajar rayuwa ta mutum ɗaya zuwa wani abin wasa a siyasa ba.”

Shugaban ya bayyana cewa mutanen Falasdinu ba “ƙurar rikici” ba ce, su ma ‘yan Adam ne kamar kowa da kowa, masu daraja da ‘yancin rayuwa irin wanda sauran mutane ke morewa.

Ya jaddada cewa Najeriya na goyon bayan ƙimar zaman lafiya da haɗin kai a maimakon tashin hankali, ramuwar gayya da zubar da jini.

Tinubu ya ce, Najeriya za ta ci gaba da yin aiki ta hanyar dandalin haɗin gwiwa na ƙasa da ƙasa don ƙarfafa doka da samar da amincewa tsakanin ɓangarorin dake hamayya.

Dangane da al’amuran cikin gida kuma, shugaban ya ce Najeriya ta ɗauki matakai masu wahala don sake fasalin tattalin arziki da kawar da tallafin man fetur da kuma tsarin canjin kuɗi, domin a samu ci gaba da bunƙasar tattalin arzikin da zai kawo zaman lafiya mai dorewa.

GWAMNA ABBA KABIR YUSUF YA SAKA ‘YAN FANSHO CIKIN FARIN CIKIA yau, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kaddamar da ...
24/09/2025

GWAMNA ABBA KABIR YUSUF YA SAKA ‘YAN FANSHO CIKIN FARIN CIKI

A yau, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kaddamar da aikin biyan bashin kudaden fansho na naira biliyan 5. Wannan shi ne kashi na biyar daga cikin kudaden da ake bin tsoffin ma’aikata da s**a yi ritaya, da kuma iyalan wadanda s**a rasu, wanda gwamnatin da ta gabata ta gaza biya.

A yayin bikin kaddamarwar, Mai Girma Gwamna ya umarci Babban Akawun Jihar tare da Kwamishinan Kudi da su saki kudaden nan take domin a tura musu. Haka kuma ya basu umarnin su fara shirin biyan kashi na shida nan ba da jimawa ba.

Yanzu haka dai, gwamnatin Kano ta riga ta biya kaso mai yawa daga cikin kudaden fansho da ta gada daga tsohuwar gwamnati.

Mai zaku ce ?

📷 Ofishin Gwabna

👇👇👇👇
23/09/2025

👇👇👇👇

ZUBAR DA ƘIMAR NAJERIYA: Yar Najeriya za ta kwanta da maza 100 cikin awanni 24 domin shiga kundin Bajinta

Daga Muryoyi

Wata matashiya daga yankin kudancin Najeriya Mandy Kiss ta sanar da shirin shiga kundin Bajinta na "Guinness World Record (GWR)" ta hanyar yin lalata da maza 100 cikin awanni 24 a Ikorodu, dake Lagos, ranar 30 ga watan Oktoba.

Muryoyi ta ruwaito kodayake har yanzu ba a tabbatar ko GWR zasu amince da wannan yunƙuri nata ba. Amma wasu na ganin “Lamarin ya ƙara nuna yadda kafafen sada zumunta ke ba wa mutane damar yin abubuwan ban mamaki don neman suna, ko da kuwa suna sabawa al’ada da tarbiyya.”

Shin wannan ba neman batawa Najeriya suna bane? Me zaku ce?

LIKE //
SHARE //
FOLLOW => Muryoyi

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa24:

Share