Hausa24

Hausa24 HAUSA24, Za Ta Kasance Wata Kafar Yada Labarai Da Za Take Kawo Muku Labarai Da Dumi-Dumin Su, Cikin Harshen Hausa!

Fagen harkar yada labarai fage ne mai fadin gaske, da dama sun zo sun tafi bayan sunyi abinda s**a yi, wasu ma sun zo basu yi komai ba sun tafi ba tare da ko labarinsu an ji ba. Mun sani kuma mun aminta igiya biyu ce kadai za ta iya rike mu, har mu ma muyi abinda muka yi. Wadannan igiyoyi su ne: GASKIYA da GOYON BAYANKU, za mu rayuwa idan har akwai wadannan igiyoyi. H24 za ta zamo wata takar yakin

Hausawa ‘yan Nijeriya, domin yakar karya da kare gaskiya a kodayaushe, koda kuwa a hannu masu mulki ne. Ta haka ne kadai za mu cimma burinmu da naku baki daya.

A lissafin gidan yari, shekara daya ba watanni 12 bace, kimanin watanni 8 ne. Saboda haka, tunda Maryam Sanda ta shafe c...
29/10/2025

A lissafin gidan yari, shekara daya ba watanni 12 bace, kimanin watanni 8 ne. Saboda haka, tunda Maryam Sanda ta shafe cikakkun shekaru 6 da watanni 8 din da Maryam Sanda a gidan yari, idan aka juya su zuwa shekarun gidan yari, zai kai kusan shekaru 10.

Tunda yanzu shugaban kasa ya maida zaman gidan yarin da zata yi zuwa shekaru 12, kuma tayi 10 (a lissafin gidan yari), shekaru 2 da s**a rage, ba su wuce watanni 16 ba.

Saboda haka, ka iya cewa nan da shekara 1 da watanni 4 Maryam Sanda zata shaki iskar yanci.

Inji Lauya, Abba Hikima.

YANZU YANZU:} Tinubu ya mayar da Maryam Sanda cikin jerin wadanda za'a yiwa afuwar sassauci maimakon yafewa gaba daga hu...
29/10/2025

YANZU YANZU:} Tinubu ya mayar da Maryam Sanda cikin jerin wadanda za'a yiwa afuwar sassauci maimakon yafewa gaba daga hukuncin ķí§á zuwa shekaru 12 a gidan yari.

A kwanakin baya an hangi sunan Maryam Sanda wacce aka yankewa hukuncin kîṣâ ta hanyar rataya bayan samun ta da ķâ§he mijin Bilyaminu a shekarun baya.

Me zaku ce

BA TAUYE ’ YANCIN ADDINI A NIJERIYA. ___ Ministan Yaɗa Labarai a hirar CNNMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji ...
29/10/2025

BA TAUYE ’ YANCIN ADDINI A NIJERIYA.

___ Ministan Yaɗa Labarai a hirar CNN

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana ƙara maida hankali wajen magance matsalolin tsaro a ƙasar nan domin tabbatar da tsaro da walwalar ’yan ƙasa.

Da yake magana a cikin wata hira da gidan talbijin na CNN ya yi da shi a London a daren Talata, Idris ya ƙaryata iƙirarin da wasu jami’an ƙasashen waje suke yi cewa wai ’yan ta’adda a Nijeriya suna kai hare-hare ne kan Kiristoci kawai.

Ya bayyana cewa irin waɗannan iƙirari ba su da tushe kuma ba su bayyana haƙiƙanin yanayin tsaron ƙasar nan, inda ya jaddada cewa ’yancin yin addini yana cikin kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Ya ce: “Wasu daga cikin iƙirarin da wasu jami’an Amurka s**a yi sun ta’allaƙa ne kan bayanai marasa inganci da kuma zato cewa yawancin waɗanda ake kai wa hare-hare Kiristoci ne. E, ana kai wa Kiristoci hari, amma waɗannan miyagun ba mabiya addini ɗaya kawai suke kai wa farmaki ba. Suna kai wa Kiristoci hari, suna kuma kai wa Musulmi hari, musamman a arewacin ƙasar.”

Idris ya ce masu yaɗa irin waɗannan labaran ƙaryar suna taimaka wa ’yan ta’addar ne, saboda manufar ’yan ta’adda ita ce su haddasa rikici tsakanin Musulmi da Kiristoci a ƙasar.

Ya ƙara da cewa Nijeriya ƙasa ce da ta yi yarda da bambancin addinai, don haka yaɗa labaran ƙarya na nuna rashin jituwa zai iya haifar da rarrabuwar kai.

Ya ce: “Kiran lamarin da cewa hare-haren kan Kiristoci ne kawai zai iya haifar da rarrabuwar kai a Nijeriya. Miyagun suna son a ɗauka kamar ana faɗa ne tsakanin Musulmi da Kiristoci. Mun shaida akwai hare-hare kan Kiristoci, kuma mun shaida akwai hare-hare kan Musulmi. Amma ba daidai ba ne a ce Nijeriya ƙasa ce da ba ta mutunta ’yancin addini, ko a ce ko'ina babu tsaro a Nijeriya. Nijeriya ƙasa ce mai aminci.”

Ministan ya amince cewa akwai matsalolin tsaro, amma kuma gwamnati tana ɗaukar matakai masu ƙarfi da tsari don magance su.

Ya bayyana cewa gwamnati ta ƙarfafa rundunonin tsaro tare da zuba jari a fannoni kamar noma da ayyukan jinƙai domin ƙarfafa zaman lafiya.

Ya ce: “Ko canje-canjen da aka yi na shugabannin hafsoshin tsaro kwanan nan duk don a ƙarfafa tsarin tsaron ƙasar ne, domin gwamnati ta iya magance kowace irin matsala a kan lokaci.”

Gwamnatin jihar Jigawa ta kaddamar da shirin bayar da tallafin Naira 10,000 duk wata ga tsofaffi marasa ƙarfi da masu bu...
28/10/2025

Gwamnatin jihar Jigawa ta kaddamar da shirin bayar da tallafin Naira 10,000 duk wata ga tsofaffi marasa ƙarfi da masu buƙata ta musamman guda 5,740 a fadin Jihar Jigawa. Gwabnan jihar Mallam Umar Namadi Dan Modi ne ya kaddamar da shirin a yau.

A kowace ƙaramar hukuma an zaɓi dattijai 200, sannan a kowace mazaba cikin mazabu 287 na jihar an zaɓi mutane 20, wanda hakan ya kai adadin su 5,740 gaba ɗaya.

HOTUNA:| Sababbin shugabannin rundunonin sojan Najeriya sun kai ziyarar girmamawa ga mai bawa shugaban ƙasa shawara a fa...
28/10/2025

HOTUNA:| Sababbin shugabannin rundunonin sojan Najeriya sun kai ziyarar girmamawa ga mai bawa shugaban ƙasa shawara a fannin tsaro (NSA) Mallam Nuhu Ribadu a yau Talata.

Gwabnatin Kano ta samar da baburan ban ruwa ga bishiyoyin kan titunan cikin Birnin Kano.Yaya ake ban ruwan bishiyoyi a J...
28/10/2025

Gwabnatin Kano ta samar da baburan ban ruwa ga bishiyoyin kan titunan cikin Birnin Kano.

Yaya ake ban ruwan bishiyoyi a Jihar ku ???

PDP:| Sule Lamido Tsohon Gwabnan Jigawa, na son zama shugaban jam'iyar PDP na kasa.A wannan safiya dai an hangi tsohon G...
27/10/2025

PDP:| Sule Lamido Tsohon Gwabnan Jigawa, na son zama shugaban jam'iyar PDP na kasa.

A wannan safiya dai an hangi tsohon Gwabnan a ofishin jam'iyar PDP na kasa dake Abuja domin sayen fom na nuna sha'awar tsaiwa neman shugabancin jam'iyar na kasa.

A ranar 15 - 16 na watan Nuwamba jam'iyar zata gudanar da babban taron jam'iyar a ibadan babban birnin jihar Oyo domin fidda sabon shugabancin jam'iyar.

Me zaku ce.

TARBIYYAR IBADA: Wasu ‘yanmata ne sukā ajiye kayan tallarsu s**a yi sallar La’asar a bàkin kofar Sakatariyar Karamar Huk...
27/10/2025

TARBIYYAR IBADA: Wasu ‘yanmata ne sukā ajiye kayan tallarsu s**a yi sallar La’asar a bàkin kofar Sakatariyar Karamar Hukumar Jahun, dake jihar Jigawa, da yammacin jiya Lahadi.

Wane fata zaku yi musu ?

NIJERIYA ZATA GUDANAR DA TARON FARKO NA IPI AFRICA. Inji Ministan Yada Labarai.Nijeriya ta amince da karɓar baƙuncin bab...
26/10/2025

NIJERIYA ZATA GUDANAR DA TARON FARKO NA IPI AFRICA.

Inji Ministan Yada Labarai.

Nijeriya ta amince da karɓar baƙuncin babban taron farko na ƙasashen nahiyar Afrika na Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Duniya (IPI).

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a wurin wani taro da aka gudanar a birnin Vienna na ƙasar Austriya, inda ya gana da Shugaban Kwamitin Zartarwa na IPI, Mista Marton Gergely; da Daraktan Zartarwa na IPI, Mista Scott Griffen, da kuma wakilin Nijeriya da Afrika a hukumar, wato Mista Raheem Adedoyin.

A cewar sa, “Nijeriya ta amince da gudanar da taron farko na ƙungiyar ta sashen nahiyar Afrika. Wani babban abin girmamawa ne a gare mu mu yi jagoranci kamar yadda muka saba.”

Wannan sanarwar ta biyo bayan matakin hukumar IPI na kafa ƙungiyoyin yankuna domin kula da buƙatu na musamman na kowane yanki a cikin al’ummar IPI ta duniya.

Ministan ya kuma tunatar da membobin yadda Nijeriya ta gudanar da babban taron duniya na IPI a Abuja a shekarar 2018 cikin nasara, inda ya ce ƙasar nan ta shirya sosai don sake gudanar da wani taron.

Ko da yake ba a saka ranar taron ba tukuna, Mista Griffen ya bayyana cewa ofishin IPI da ke Vienna zai tsara cikakkun bayanai tare da Mista Adedoyin da kuma Kwamitin IPI na Nijeriya.

Shugaban Kwamitin Zartarwar IPI, Mista Gergely, ya yaba wa Nijeriya a matsayin jagora wajen tafiyar da dimokiraɗiyya da kuma kare ’yancin ’yan jarida.

Haka zalika, Mista Griffen ya jinjina wa Kwamitin IPI na Nijeriya bisa jajircewar su wajen kare ’yancin manema labarai.

A yayin tattaunawar, Ministan ya jawo hankalin shugabannin na IPI kan buƙatar ƙarin tallafin ƙungiyar ga Makarantar Koyon Aikin Jarida ta Nijeriya (NIJ) da ke Ogba, Legas — makarantar da IPI ta kafa tun a cikin 1971 a lokacin jagorancin marigayi Alhaji Lateef Jakande.

Ya bayyana cewa yanzu haka tsohon Gwamnan Jihar Ogun, Aremo Olusegun Osoba, shi ne shugaban kwamitin gudanarwar makarantar.

Idris, wanda yana ɗaya daga cikin manyan membobin IPI, ya kasance cikin mahalarta babban taron IPI na duniya da bikin cikar ƙungiyar shekara 75 da aka gudanar a Vienna.

Sauran ’yan tawagar Nijeriya a taron sun haɗa da Mista Raheem Adedoyin; da Shugaban IPI Nijeriya, Musikilu Mojeed; da tsohon mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Malam Garba Shehu; da Dakta Fabian Benjamin na JAMB; da Babban Sakatare ga Gwamnan Jihar Kwara, Malam Rafiu Ajakaye; da Shugaban kamfani da jaridar Patrons Media/The Culture, Mista Steve Ayorinde; da Farfesa Abigail Ogwuensi na Jami’ar Legas; da lauya kuma mai bada shawara ga IPI Nijeriya, Mista Tobi Soniyi.

SHUGABA TINUBU YA SAUYA SHUGABANNIN HUKUMOMIN TSAROShugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya yi sauye-sauye a tsarin manyan haf...
24/10/2025

SHUGABA TINUBU YA SAUYA SHUGABANNIN HUKUMOMIN TSARO

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya yi sauye-sauye a tsarin manyan hafsoshin rundunonin tsaron ƙasar, a ci gaba da ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na ƙarfafa tsarin tsaron ƙasa.

Shugaban Ƙasa ya naɗa Janar Olufemi Oluyede a matsayin sabon Shugaban Ma’aikatan Tsaro (Chief of Defence Staff), wanda zai maye gurbin Janar Christopher Musa.

Sabon Shugaban Rundunar Sojojin Ƙasa (Chief of Army Staff) shi ne Manjo Janar W. Shaibu, yayin da Air Vice Marshal S.K. Aneke shi ne Shugaban Rundunar Sojin Sama (Chief of Air Staff). Rear Admiral I. Abbas shi ne sabon Shugaban Rundunar Sojin Ruwa (Chief of Naval Staff).

Shugaban Sashen Leken Asiri na Tsaro (Chief of Defence Intelligence), Manjo Janar E.A.P. Undiendeye, ya ci gaba da rike matsayinsa.

Shugaban Ƙasa, wanda shi ne Kwamandan-in-Chief na Rundunonin Sojojin Najeriya, ya bayyana godiya ta musamman ga Janar Christopher Musa da sauran shugabannin rundunonin tsaro da s**a sauka daga mukamansu bisa ƙaunarsu ga ƙasa da kuma jagorancin nagarta da s**a nuna a lokacin aikinsu.

Shugaban Ƙasa ya umarci sabbin shugabannin rundunonin tsaro da su tabbatar sun cancanci amincewar da aka nuna musu ta hanyar ƙara haɓaka ƙwarewa, faɗakarwa da haɗin kai — waɗanda su ne ginshiƙai na rundunonin tsaron Najeriya.

Dukkan waɗannan nadin suna fara aiki nan take.

HOTUNA:} Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu tare da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima, da sauran al’umma sun gabatar da ...
24/10/2025

HOTUNA:} Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu tare da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima, da sauran al’umma sun gabatar da sallar Juma’a a yau a masallacin Fadar Shugaban Ƙasa da ke A*o Rock. Limamin masallacin, Sheikh Abdulwaheed Suleiman, ne ya jagoranci sallar.

Photo 📸 Abdulaziz.

Bayan awa guda da ya wuce da wallafar labarin mutuwar Hassan Makeup da jaridar Damagaram Post ta yi, daga bisani Hassan ...
23/10/2025

Bayan awa guda da ya wuce da wallafar labarin mutuwar Hassan Makeup da jaridar Damagaram Post ta yi, daga bisani Hassan ya bayyana cewa yana raye, bai mutu ba.

Damagaram Post na daga cikin manyan jaridun intanet da ake mutuntawa tare da tsammanin cewa suna buga labaran gaskiya daga ƙasar Nijar. Amma a wannan karon, jaridar ta wallafa labarin ƙarya game da Hassan Makeup.

Jaridar Hausa24 na neman afuwar ku kan wannan labarin, kasancewar mun buga shi ne bisa dogaro da cewa Damagaram Post ce ta wallafa shi.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa24:

Share