Hausa24

Hausa24 HAUSA24, Za Ta Kasance Wata Kafar Yada Labarai Da Za Take Kawo Muku Labarai Da Dumi-Dumin Su, Cikin Harshen Hausa!

Fagen harkar yada labarai fage ne mai fadin gaske, da dama sun zo sun tafi bayan sunyi abinda s**a yi, wasu ma sun zo basu yi komai ba sun tafi ba tare da ko labarinsu an ji ba. Mun sani kuma mun aminta igiya biyu ce kadai za ta iya rike mu, har mu ma muyi abinda muka yi. Wadannan igiyoyi su ne: GASKIYA da GOYON BAYANKU, za mu rayuwa idan har akwai wadannan igiyoyi. H24 za ta zamo wata takar yakin

Hausawa ‘yan Nijeriya, domin yakar karya da kare gaskiya a kodayaushe, koda kuwa a hannu masu mulki ne. Ta haka ne kadai za mu cimma burinmu da naku baki daya.

Gwamnatin Tarayya za ta fara bai wa ɗalibai 100MB na data kyauta a kowace ranaGwamnatin Tarayya ta sanar da shirin fara ...
10/09/2026

Gwamnatin Tarayya za ta fara bai wa ɗalibai 100MB na data kyauta a kowace rana

Gwamnatin Tarayya ta sanar da shirin fara bai wa ɗalibai 100MB na data kyauta a kowace rana, domin sauƙaƙa musu damar samun ilimi ta kafafen intanet.

Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan a yau, Alhamis, a Abuja, yayin taron ƙaddamar da shirin samar da damar shiga shafukan yanar gizo da manhajojin ilimi kyauta.

A cewar ministan, shirin zai fara aiki daga 1 ga Oktoba, 2026, domin bai wa ɗalibai damar yin amfani da shafukan yanar gizo da manhajojin ilimi cikin sauƙi, tare da inganta damar samun kayan karatu na zamani.

Gwamnatin Kano za ta samar da babura masu ƙafa uku ƙirar motar asibiti ga mazabu 484Gwamnatin Jihar Kano na shirin samar...
10/09/2026

Gwamnatin Kano za ta samar da babura masu ƙafa uku ƙirar motar asibiti ga mazabu 484

Gwamnatin Jihar Kano na shirin samar da babura masu ƙafa uku, waɗanda aka ƙera su da tsarin motar asibiti, ga kowace daga cikin mazabu 484 na jihar.

Matakin na daga cikin shirye-shiryen gwamnatin jihar na sauƙaƙa jigilar marasa lafiya, musamman daga yankunan karkara zuwa asibitoci, tare da inganta samun kulawar lafiya cikin sauƙi da gaggawa.

Bashir Ahmad Ya Buƙaci Kamfanin OPay Ta Sake Duba Batun K**a Haifa Abubakar.Tsohon hadimin shugaban ƙasa Buhari, Hon. Ba...
10/09/2026

Bashir Ahmad Ya Buƙaci Kamfanin OPay Ta Sake Duba Batun K**a Haifa Abubakar.

Tsohon hadimin shugaban ƙasa Buhari, Hon. Bashir Ahmad, ya roƙi kamfanin gudanar da hulɗar kuɗi na OPay ta sake duba batun k**a Haifa Abubakar kan wani saƙon ƙarya data wallafa cewa kamfanin na shirin rufe ayyukansa daga Najeriya.

Bashir Ahmad, ya ce Haifa ta amince da kuskurenta, ta goge saƙon kuma ta ba da haƙuri k**ar yadda OPay ta buƙata. ya kara da cewa "idan ta cika abin da kamfanin ya nema, akwai tambaya kan dalilin da ya sa har yanzu aka k**a ta"

ME ZAKU CE???

Yayi sujadar godiya ga Allah da sanatan Borno ta kudu Sanata Ndume yayi rabon Motoci da Babura ga masoyansa.
10/09/2026

Yayi sujadar godiya ga Allah da sanatan Borno ta kudu Sanata Ndume yayi rabon Motoci da Babura ga masoyansa.

CINCIRINDON MUTANE A KAHUTUCincirindon jama’a ne s**a halarci taron ƙaddamar da ƙungiyar yaƙin neman zaɓen Shugaban Ƙasa...
10/09/2026

CINCIRINDON MUTANE A KAHUTU

Cincirindon jama’a ne s**a halarci taron ƙaddamar da ƙungiyar yaƙin neman zaɓen Shugaban Ƙasa Tinubu mai suna Tripple R, wadda shahararren mawaki Rarara ke jagoranta.

Ana gudanar da taron ne a halin yanzu a ƙauyen Rarara, wato Kahutu a jihar Katsina inda jama’a daga sassa daban-daban s**a taru domin halartar taron.

Ƙungiyar Rarara (Tripple R) naci gaba da gudanar da tarukanta domin nemawa Bola Tinubu Masoya.
10/09/2026

Ƙungiyar Rarara (Tripple R) naci gaba da gudanar da tarukanta domin nemawa Bola Tinubu Masoya.

Jarumi a Kannywood Tanimu Akawu ya samu sauki, ya koma harkokinsa na yau da kullum. Inda aka hangoshi cikin taron Trippl...
10/09/2026

Jarumi a Kannywood Tanimu Akawu ya samu sauki, ya koma harkokinsa na yau da kullum. Inda aka hangoshi cikin taron Tripple R.

Allah ya kara bamu lafiya.

Ƙungiyar Kiristoci ta goyi bayan Tinubu a zaɓen 2027Ƙungiyar "Charismatic Bishops Conference of Nigeria" (CBCN) ta bayya...
10/09/2026

Ƙungiyar Kiristoci ta goyi bayan Tinubu a zaɓen 2027

Ƙungiyar "Charismatic Bishops Conference of Nigeria" (CBCN) ta bayyana goyon bayan ta ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a babban zaɓen 2027.

Shugaban CBCN, Archbishop Prof. Leonard Bature Kawas, shi ne ya bayyana matsayar ƙungiyar a ranar Laraba a Abuja, a lokacin da ake gudanar da babban taron Synod na 2026 na CBCN da ICCABA a Majami'ar Kiristoci ta Ƙasa.

Kawas ya ce ƙungiyar ta yi nazari kan ayyukan gwamnatin Tinubu, tare da bayyana shirin ta na ci gaba da mara wa shugaban ƙasar baya ta hanyar addu’a, bayar da shawarwari da kuma wayar da kai.

Ya ce: “Mun goyi bayan sa a yanzu. Mun goyi bayan sa yau, za mu goyi bayan sa gobe, kuma za mu ci gaba da goya masa baya muddin yana son kasancewa shugaban ƙasar mu.”

Ya ƙara da cewa: “Wannan gida ya amince da shi a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na 2027.”

Da yake jawabi a wajen taron, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci shugabannin addini da su yi amfani da tasirin su wajen ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da kyakkyawar mu’amala tsakanin al’umma gabanin zaɓen 2027.

Ya ce: “Ci gaba da haɗa kan wannan ƙasa na buƙatar fiye da matakan gwamnati. Yana buƙatar jagoranci nagari daga dukkan ɓangarorin al’umma, ciki har da jagorancin addini."

Idris ya yi gargaɗi kan yunƙurin nuna matsalolin tsaron Nijeriya a matsayin yaƙin addini, yana mai cewa ’yan ta’adda da ƙungiyoyin masu aikata laifuka sun kai wa ’yan Nijeriya hare-hare ba tare da la’akari da addinin su ko asalin su ba.

“Kada a bari wani zaɓe ya sa Kirista ya juya wa Musulmi baya, ko Musulmi ya juya wa Kirista baya, ko Arewa ta juya wa Kudu baya, ko wata ƙabila ta juya wa wata baya. Nijeriya tamu ce baki ɗaya,” inji shi.

Da yake wakiltar Shugaban Ƙasa Tinubu, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya yaba wa ma'abota cocin kan gudunmawar su ga zaman lafiya da haɗin kan ƙasa, tare da kira da a samu ƙarin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da shugabannin addini.

Ya ce: “Gwamnati tana buƙatar gudunmawar Kiristoci wajen kyautata ɗabi’a da tarbiyyar al’umma, yayin da Kiristoci suke buƙatar yanayin da zai ba su damar gudanar da ayyukan su da kyau. Fiye da komai, Nijeriya tana buƙatar mu yi aiki tare domin amfanin kowa.”

DA ƊUMI-ƊUMIMatashi Ya Kai Ƙorafi Ofishin ’Yan Sanda Kan Zargin Yanke Yatsarsa Saboda Neman Naira Miliyan 80Wani matashi...
10/09/2026

DA ƊUMI-ƊUMI

Matashi Ya Kai Ƙorafi Ofishin ’Yan Sanda Kan Zargin Yanke Yatsarsa Saboda Neman Naira Miliyan 80

Wani matashi ya kai ƙorafi a Ofishin ’Yan Sanda da ke Rano, inda ya zargi wani mutum da yi masa alkawarin ba shi Naira miliyan 80 idan ya samo masa ɗan yatsan mutum mai rai.

A cewar matashin, bayan ya yi ƙoƙarin nemo ɗan yatsan wani mutum amma ya kasa, sai ya yanke shawarar amfani da ɗan yatsansa da kansa, inda ya yanke shi sannan ya miƙa wa mutumin da ya yi masa alkawarin kuɗin.

Sai dai, matashin ya ce bayan ya miƙa masa ɗan yatsan, mutumin ya ƙi ba shi kuɗin da ya yi masa alkawari.

Rahotanni sun bayyana cewa matashin ya kai lamarin gaban ’yan sanda domin neman a binciki batun tare da ɗaukar matakin da ya dace.

Me zaku ce ?

10/09/2026

Cewa nai zan bata 500 naɗan shafata

- Inji wani matashi da ake zargi da lalata karamar yarinya

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa24:

Shortcuts

Share