Daily Feeds

Daily Feeds Daily Feeds is a Nigeria-based Digital Media Company that has its Head Office in Abuja, Nigeria.

AC MAIWADA: Matashin Bakatsinen Da Ya Shahara A Fannin Hulɗa Da Jama'a A Harkokin GwamnatiDaga Muhammad Bashir, Muhammad...
26/07/2025

AC MAIWADA: Matashin Bakatsinen Da Ya Shahara A Fannin Hulɗa Da Jama'a A Harkokin Gwamnati

Daga Muhammad Bashir, Muhammad Aliyu Rimaye

A kaf taron matasan da ke aiki a ma’aikatun gwamnati a yanzu—musamman a hukumomin tsaro—sa'annan suke taka muhimmiyar rawa a fannin bunƙasa martabar hukumomin, ba yadda za a yi; a kasa ambaton sunan Assistant Comptroller of Customs Abdullahi Aliyu Maiwada, wanda a halin yanzu shi ne Jami'in Hulɗa da Jama'a na Ƙasa (National PRO) a Hukumar Kwastam ta Ƙasa (NCS).

AC Maiwada, wanda ko shekaru 40 da haihuwa bai kai ba, yana haskakawa a matsayin ɗaya daga cikin matasan da s**a rungumi tsarin jagoranci cikin kwarjini da ladabi da kuma ƙware wa—ta yadda tuni waɗansu har sun fara kwatanta hasken aikinsa da tauraron Sirius da ke sararin samaniya. A matsayinsa na kakakin hukumar, yana wakiltar Hukumar Kwastam da tsantsar sanin makamar aiki, ta hanyar gudanar da ayyukansa cikin basira da kuma yin amfani da dabarun Public Relations na zamani don inganta martabar hukumar da kuma gina kyakkyawar alaka da al’umma.

A ƙarƙashin jagorancinsa, Sashen Hulɗa da Jama'a na Hukumar Kwastam ya lashe kyaututtuka irinsu WCO Meritorious Award na shekarar 2024 da kuma Kyautar Mafi Ƙwazo a Fannin Yada Labarai daga NIPR a shekarar 2025. Haka zalika, a shekarar 2023, wani kamfanin dillacin labarai na Image Merchant Limited ya karrama shi da Kyautar Kakakin Hukuma Mafi Cancanta.

Duk da cewa Maiwada ya shahara a matakin ƙasa, da dama daga cikin jama’a ba su san cewa ɗan Jihar Katsina ne ba, wanda bugu da ƙari, an haife shi ne ma a Karamar Hukumar Katsina. A gaskiya, yana da ginshiƙan zuri’a masu tarihi da tasiri a ilimi da shugabanci a Arewacin Najeriya.

A bangaren mahaifinsa kuma, AC Maiwada ya fito ne daga gidan ilimi mai daraja—domin bayan kakansa, marigayi Alhaji Abubakar Maiwada—ya kasance ɗaya daga cikin manyan malamai a fannin Ilimi na Musamman, wato Special Education, tun daga shekarun 1960s har zuwa 1990s—hatta mahaifinsa, Alhaji Aliyu Maiwada, shi ma farfesa ne da ya karantar a Jami'ar Bayero—kafin rasuwarsa a shekarar 2020. Haka nan, tarihi ya nuna yadda kakan na sa ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa makarantu kamar Tudun Maliki Special School a Jihar Kano, wanda har ya zuwa yanzu ba a daina alfahari da shi ba. Wannan bajimin malami, shi ya haifi Farfesa Danjuma Maiwada, wanda ya kasance Farfesa na farko daga Jihar Katsina—wanda har yanzu shi ma ake alfahari da irinsa a Arewacin Najeriya.

A bangaren mahaifiya kuwa, an haife shi cikin zuriyar sarauta da ilimi. Kakan mahaifiyarsa, Muhammad Gidado, shi ne ɗan fari ga Sarkin Katsina, Sarki Dikko. Wannan zuri’a itace ta haifi Muhammad Salisu wanda ake yiwa al—kunya da Nalado, kuma shi ne kakansa na uwa, mutum mai tarin ilimi da tarihi a masarautar Katsina.

Abdullahi Aliyu Maiwada ya fara karatunsa ne na farko tun yana da ƙuruciya a cikin jami'ar Bayero ta Kano, wato Staff Primary School Kano (1992–1997), ya ci gaba da sakandire a Government Science Secondary School Dutsin-Ma dake Jihar Katsina. Bayan nan kuma ya karanci ilimin taswirar ƙasa, wato Geography Education a matsayin digiri na farko a Bayero University Kano, daga baya kuma yayi digirin—digirgir a fannin kula da muhalli, wato Environmental Management a shekarar 2011.

AC Abdullahi Maiwada ya sake komawa makaranta inda ya samu wata digirin a fannin Mass Communication da Media Arts daga Crescent University Abeokuta daga bisani ma ya zarce har zuwa karatun PhD a jami'ar tarayya dake Abuja—wato University of Abuja.

Tun bayan shiga Hukumar Kwastam da yayi a shekarar 2011, AC Maiwada ya rike manyan mukamai daban-daban. Ya fara aiki a matsayin Jami’in Hulda da Jama’a a Hedikwatar Shiyyar B ta Kaduna (2013–2017), daga nan zuwa Jihar Ogun (2017–2020), kafin a dawo da shi Hedikwata a Abuja a matsayin wakilin Hukumar Kwastam a tashar NBCN. Daga nan, aka ɗaga shi zuwa Mataimakin Kakakin Hukumar na Ƙasa daga shekarar 2022 zuwa 2023. Sa'annan an naɗa shi cikakken Kakakin Hukumar (April 2023).

Yana da shaidar zama mamba a ƙungiyoyin ƙwararru da dama ciki har da Nigerian Institute of Public Relations (NIPR), African Public Relations Association (APRA), Association of Communication Scholars and Professionals of Nigeria (ACSPN) da sauransu.

AC Abdullahi Maiwada mutum ne da ke da kwazo da hangen nesa da kuma kaifin tunani wajen ganin Hukumar Kwastam ta kasance abar misali a fannoni da dama, musamman a bangaren sadarwa da wayar da kai. Yana martaba ilimi; yana aiki da kwarewa da kuma gaskiya; yana kuma kare mutuncin aikinsa da zuri'arsa da kuma jiharsa.

Wannan matsahin Bakatsinen, wanda ya fito daga tsatson ilimi a bangarori da dama, ya cancanci yabo da goyon baya daga dukkan Arewacin Najeriya—ba ma jihar Katsina ba kawai. A yau, idan ana maganar sabbin jagorori da za su shugabanci sabuwar Najeriya, tabbas Maiwada yana daga cikin fitattun matasa da s**a cancanci a amince masu.

Tsarin Zamanantar Da Kasuwanci Na Hukumar Kwastom TMP Zai Samarwar Gwamnati Harajin Dala Biliyan 250Janar Manaja na tsar...
06/06/2024

Tsarin Zamanantar Da Kasuwanci Na Hukumar Kwastom TMP Zai Samarwar Gwamnati Harajin Dala Biliyan 250

Janar Manaja na tsarin zamanantar da kasuwanci na hukumar hana fasa kwauri ta kasa mai taken TMP, Ahmad Ogunshola a ranar Talata 4 ga watan Yuni ya bayyana fatan cewa tsarin zamanantarwa da aka fito da shi zai taimakawa Najeriya mussaman a fannin tattara kudaden shiga.

A yayin ziyarar manema kabarai a ofishin jami'an shirin a birnin tarayya Abuja, Ahmad ya ce " Shirin zai samar da harajin Dala Biliyan 250 ga gwamnatin tsawon lokacin da aka dibar masa".

Acewarsa, shirin ya riki babbar damar habbaka tattara kudaden shiga ta hanyar amfani da fasahar zamani "Wanda hakan zai zama mai Alfanu ga Gwamnatin tarayya".

Shirin na TMP zai hada da shigar da ayyukan kasuwanci na hukumar hana fasa kwauri ta kasa da kuma bunkasa abinda masu ruwa da tsaki ke koya a fannin hada hadar kasuwanci. Hakan zai hada da bin hanyoyin samun amincewa wajen shige da ficen kayayyaki da biyan kudin harajin shigo da kaya da kuma sakin kayan.

Ya bayyana cewa shirin na zamanantarwar zai matso da Najeriya kusa a fannin hada hadar kasuwancin duniya ta hanyar amfani da fasahar zamani. Haka kuma shirin zai tallafawa kudurin gwamnati na bunkasa tattalin arziki ta hanyar saukaka kasuwancin kasa da kasa.

Ogunshola yayi bayanin cewa aiwatar da dukkan shirin na TMP zai shafi dukkan ayyukan hukumar Kwastom, ciki har da karbar haraji da tantance kayayyaki da kokarin yaki da fasa kwauri.

Da yake jawabi ga manema labarai, mai magana da yawun hukumar hana fasa kwauri ta kasa, CSC Abdullahi Maiwada ya ce ziyarar an yita ne domin yiwa al'umma jawabi kan ci gaban da aka samu daga tsarin na TMP wanda aka fara tsawon shekaru domin kula al'amuran kasuwanci.

Hukumar hana fasa kwauri ta kasa ta hada kai da shirin domin samar da na'urar tantance madaukai wacce zata iya tantance madaukai 200 cikin awa guda. Wannan tsari karkashin jagorancin babban konturola janar, Adewale Adeniyi an yi shi ne domin rage lokacin tantance madaukan kaya.

"Abin da ake son cimmawa shi ne zamanantar da dukkan hanyoyon da mayar da ita mafi sauki da gamsarwa", inji Ogunshola. Shirin dai ana yinsa a rukunin gidaje na hukumar kwastom dake Abuja wanda ya baiwa kwararru a fannin fasahar sadarwa damar samar da tsarin hada hadar kudi ma shige da ficen kaya.

Tsarin da aka dibarwa shekaru 20 ya kasu zuwa mataki 3

1. Mataki na 1(Shekaru daga 1 zuwa 6): samar da na'uara ciki har da na'urar zahiri da na fasahar zamami.
2. Mataki na(Daga shekara 7 zuwa 13):Kula da tsarin shirin da maye gurbin na'urori da ake bukata.
3. Mataki na (Shekaru 14 zuwa 20) mayar da tsrain zuwa ga jami'an hukumar kwastom tare da tallafin shirin na TMP wajen basu horo.

Da yake karin bayani, CSC, Usman Abba yayi bayyana irin alfanun shirin wanda zai baiwa masu shigo da kaya damar ganin yadda ake tantance kayan. " Tsarin zai bada damar bibiya a kan lokaci da rage ayyukan barna", inji Abdullahi Maiwada jami'in hulda da jama'a na hukumar Kwastom.

Wannan ci gaban na fasahar zamani anasa rai zai bunkasa tashoshin ruwan Najeriya wajen gamsasshen aiki da kuma yin kafada da kafada da tsarin da duniya ke kai a yanzu.

COWA Apapa Command Holds Maiden Meeting, Solicits Comptroller Olomu's SupportBy Muhammad BashirAs Nigeria Customs Servic...
01/06/2024

COWA Apapa Command Holds Maiden Meeting, Solicits Comptroller Olomu's Support

By Muhammad Bashir

As Nigeria Customs Service deploys Comptroller Babatunde Olomu to head Apapa Command, the Command's chairperson of the Customs Officers' Wives Association (COWA), Mrs. Funsho Olomu, has called on officers' wives at the Apapa Command to join the association to benefit from its goodies.

Mrs. Olomu made this call in Lagos on Thursday 30th May, 2024, when she led her executives members on a courtesy visit to the Customs Area Controller, Babatunde Olomu, adding "our association considers every wife of officer as a family member, hence the need to come en masse to become registered members of the association."

The meeting, which is first of its kind since the appointment of Mrs. Olomu as the new chairperson of COWA's Apapa branch, revolved around paving ways to sensitise members and revive the activities of the association in the command.

Customs Area Comptroller Babatunde Olomu, on his part, expressed delight to see the team and promised to support them in all ramification within his power, adding "my contribution to COWA will continue to be sustained, and I will intimate my officers during our parade to encourage their wives to be part of the good initiative of COWA."

In a separate occasion, Mrs. Olomu also coordinated another historic visit to Marine Beach and Liverpool Road barracks, where they engaged other officers' wives and rubbed minds with them on key plans to strengthen the presence of the association in the formation.

Also, in her efforts to key into President Kikelomo's agenda of cushioning women with skills to become self-relient, Mrs. Funsho further visited the spa area within the Command complex, where she vowed to conduct national healthy wife wealthy life quarterly programmes.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily Feeds posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily Feeds:

Share