UMG News

UMG News Domin samar da labarai masu inganci a ciki da wajen Najeriya da s**a shafi Siyasa da Tattalin Arziki.

14/06/2024

Takaitaccen tarihin
yadda aka gina Babban Masallacin
Kasa dake Abuja da irin
gudunmawar da Kasar Saudiyya ta
bayar wajen gina shi daga bakin
Farfesa Shehu Ahmad Galadanchi da Mai Martaba Etsu Nupe.

Wane fata zaku yiwa Kasar
Saudiyya?

20/05/2024

Bidiyon Shugaban Kasar Iran Ebrahim Raisi , Jim kadan kafin Jirgin da yake ciki ya yi hadari.

Allah Ya jikansa.

07/04/2024

2024 Ramadan: Abinda Yasa Bana Za a yi Azumi 30 - Sheikh Salihu Muhammad Yakub

Me zaku ce?

19/03/2024

Tare da Jigo a Jam'iyyar APC, Hon. Iliyasu Kwankwaso, inda yake bayyana kyawawan manufofin Shugaba Tinubu

19/03/2024

Gwamnatin Tinubu Ba Ta Kabilanci Ba Ce, Ba A Fahimce Shi Ba Ne - Iliyasu Kwankwaso

YAN NAJERIYA KU GAFARCE MU - MTNKamfanin sadarwa na MTN a Najeriya ya nemi afuwar aboka huldarsa sak**akon matsalar ɗauk...
28/02/2024

YAN NAJERIYA KU GAFARCE MU - MTN

Kamfanin sadarwa na MTN a Najeriya ya nemi afuwar aboka huldarsa sak**akon matsalar ɗaukewar sabis da kamfanin ya fuskanta a faɗin ƙasar.

Tun da tsakar ranar Laraba ne dai masu amfani da layin MTN s**a fara fuskantar matsalar ɗaukewar sabis a layukansu.

To sai dai kamfanin cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na X, ya ce hakan ya faru ne sak**akon yankewar wasu wayoyin sadarwar kamfanin, lamarin ya ya shafi kira da kuma fannin intanet a layin.

Kamfanin ya kuma ce injiniyoyinsa na aiki domin shawo kan matsalar, inda ya ce sannu a hankali sabis ɗin ya fara dawowa a wasu yankuna.

KO KUN SAN WANNAN MASALLACIN SHINE NA UKU MAFI GIRMA A DUNIYA An Kaddamar da katafaren masallacin mai suna 'The Great Mo...
26/02/2024

KO KUN SAN WANNAN MASALLACIN SHINE NA UKU MAFI GIRMA A DUNIYA

An Kaddamar da katafaren masallacin mai suna 'The Great Mosque of Algiers' wanda shine mafi girma a Afirka dake a birnin Algiers sannan kuma na uku mafi girma a duniya.

Shugaban Kasar Algeriya, Abdulmadjid Tebboune ne jagoranci kaddamar da masallacin.

Bayan masallatai masu tsarki na Makkah da Madina sai wannan Masallacin, wanda girmansa ya kai kadada saba'in sannan mutum 120,000 ne za su iya yin ibada cikin sa lokaci guda.

Hakazalika Masallacin na da hasumiya mafi tsawo da ake amfani da ita wajen kiran sallah.

An gina masallacin cikin shekara bakwai inda kuma aka kashe sama da dala miliyan 800,000 wajen gina shi.

Ana sa ran za a rika gudanar da salloli a lokacin watan Ramadan da ake shirin farawa nan da mako biyu masu zuwa.

Masallacin wani aiki ne na tsohon shugaba Abdelaziz Bouteflika wanda ya sauka daga kan mulki a 2019 bayan yunkurinsa na neman wa'adi na biyar ya janyo gagarumar zanga-zanga.

ECOWAS TA DAGE TAKUNTUMAN DAKE KAN NIJAR, MALI DA BURKINA FASOƘungiyar Raya Tattalin Arzkin Ƙasashen Afirka ta Yamma, Ec...
24/02/2024

ECOWAS TA DAGE TAKUNTUMAN DAKE KAN NIJAR, MALI DA BURKINA FASO

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzkin Ƙasashen Afirka ta Yamma, Ecowas ta ɗage tarin takunkuman da ta ƙaƙaba wa ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso da kuma Giunea.

Ƙungiyar ta ɗauki matakin ne a wani taron shugabannin ƙasashen ƙungiyar da aka gudanar a Abuja babban birnin Najeriya.

Ƙungiyar ta ce a yanzu za ta iya gayyatar ƙasashen huɗu zuwa tarukanta da s**a shafi tsaro da zaman lafiya.

Ecowas ta ce ɗage takunkuman - wanda zai fara aiki nan take - ta yi shi ne bisa dalilai na jin kai.

Huka kuma ƙungiyar ta jaddada kiranta na sakin hamɓararreb shugaban Nijar Mohamed Bazaoum da sojojin ƙasar ke ci gaba da yi wa ɗaurin talala.

Ecowas ta kaƙaba wa ƙasashe takunkuman ne bayan da sojoji s**a kifar da gwamnatocin fara hula a ƙasashen.

Daga cikin takunkuman da ƙungiyar ta ƙaƙaba wa ƙasashen sun haɗa da rufe iyakokin ƙasashen da na ƙungiyar da kuma yanke wutar lantarki a Nijar da sauran takunkuman karya tattalin arziki.

A makonnin baya-bayan ne ƙasashen Nijar, MAli da Burkina Faso s**a ayyana ficewa daga ƙungiyar bayan da s**a zargi ƙungiyar Ecowas da ƙaƙaba musu takunkuman karya tattalin arziki.

Ecowas ta riƙa fuskantar matsin lamba daga ƙungiyoyi da ɗaiɗaikun mutane kan ta ɗage wa ƙasashen takunkuman.

Ko a makon da ya gabata ma tsohon shugaban mulkin sojin Najeriya Janar Yakubu Gowan wanda shi ne mutum ɗaya tilo da ya rage cikin shugabanin da s**a kafa ƙungiyar, ya yi kira ga shugabanninta da su ɗage wa ƙasashen takunkuman.

Nijar ta samu kanta cikin takunkuman Ecowas bayan da sojojin kasar s**a kifar da gwamnatin farar hula da Mohamed Bazoum cikin watan Yulin shekarar da ta gabata.

24/02/2024

INNALILLAHI...
Matar Auren da Hukumar Hisbah ta k**a, Sa`adatu Mukhtar wacce ta baro gidan Mijinta a Jihar Katsina ta je Kano ta kitsa cewa an yi garkuwa da ita sai an biya Miliyan 30

BENUWAI TA BAIWA BAKIN MAKIYAYA WA'ADIN FICEWA DAGA JIHAR Gwamnatin jihar Benue da ke arewa ta tsakiyar Najeriya, ta bai...
22/02/2024

BENUWAI TA BAIWA BAKIN MAKIYAYA WA'ADIN FICEWA DAGA JIHAR

Gwamnatin jihar Benue da ke arewa ta tsakiyar Najeriya, ta bai wa Fulani makiyaya da ta ce baki ne da ke kwarara cikin jihar da kuma ake zargin na dauke da mak**ai wa’adin makonni biyu su fice a jihar ko su fuskanci fushin hukuma.

Gwamnan jihar Hyacinth Alia ya kafa wani kwamiti na musamman da zai tabbatar da bin umurnin, sannan ya jaddada cewa har yanzu dokar nan da ta haramta kiwon dabbobi a sarari na ci gaba aiki.

To sai dai kungiyar Miyetti Allah reshen jihar ta nesanta kanta da ‘ya’yanta da yin kowane hadin gwiwa da dukan wasu bata garin makiya a cikin jihar.

Address

Abuja
Abuja

Telephone

+2348024473144

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when UMG News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to UMG News:

Share