07/06/2026
Babban kotu a Jihar Bauchi mai lamba ta 5, karkashin jagorancin Mai Shari’a Mu’azu Abubakar, ta bayar da umarnin tsare tsohon Akanta Janar na Jihar Bauchi, Dakta Sa’idu Abubakar, a gidan gyaran hali da tarbiyya da ke Bauchi bisa zargin almundahanar kudade da s**a kai kimanin Naira biliyan 40
An gurfanar da Dakta Sa’idu Abubakar a gaban kotu kan sabbin tuhume-tuhume guda 16 da aka yi masa ƙarƙashin Sashe na 116 na Dokar Gudanar da Shari’ar Laifuka ta Jihar Bauchi ta shekarar 2022.
Sai dai wanda ake tuhuma ya musanta dukkan zarge-zargen da ake masa
Bisa ga takardar tuhumar da ke cikin Shari’a mai lamba BA/205C/2025, Gwamnatin Jihar Bauchi ce mai ƙara, yayin da Dakta Sa’idu Abubakar shi ne kaɗai wanda ake tuhuma
Masu gabatar da ƙara sun yi zargin cewa tsakanin ranar 7 ga Disamba, 2023 da 9 ga Janairu, 2024, yayin da yake rike da mukamin Akanta Janar kuma yana da alhakin kula da kudaden gwamnati, ya yi amfani da wasu kudaden gwamnati ba bisa ka’ida ba tare da karkatar da su zuwa amfanin kansa ko wasu manufofi da ba a amince da su ba
An kuma yi zargin cewa kudaden na daga cikin bashin biliyoyin naira da gwamnatin jihar ta karɓo daga cibiyoyin kuɗi daban-daban, wanda aka ce an ware su ne domin wani kwangila da ba ta wanzu na samar da babura 5,000, tare da wasu mu’amalolin banki daban-daban
Masu gabatar da ƙarar sun bayyana cewa irin wannan aiki ya saɓa wa Sashe na 315 kuma hukuncinsa yana ƙarƙashin Sashe na 312 na Dokar Penal Code ta Jihar Bauchi ta shekarar 2022
Daga bisani, Mai Shari’a Mu’azu Abubakar ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake tuhuma tare da ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 2 ga Yuli, 2026, domin sauraron ƙorafin farko da lauyan wanda ake tuhuma ya gabatar
Ana sa ran shari’ar za ta ci gaba da sauraron muhawarar bangarorin biyu kan batutuwan farko kafin a fara cikakken sauraron shari’ar.