05/08/2025
Allah Ne Kaɗai Zai Biya Ku Da Irin Ƙoƙarin Da Ku Ke Yi Domin Samar Da Zaman Lafiyar Al'umma A Arewacin Najeriya
Ibrahim Imam Ikara
Duk wanda ya saurari bayanan Sheikh Musa Yusuf Asadussunnah kan namijin ƙoƙarin da kwamitin su na sulhu ya ke yi wurin samar da zaman lafiya a yankin da a ke fama da matsalar ƴan bindiga, da kuma yadda su ke sadaukar da rayukan su domin maslahar al'umma da zaman lafiyar al'umma dole ka tausaya musu, kuma ka yi musu addu'ar alheri.
Daga cikin irin nasarar da kwamitin da Malam Musa Asadussunnah ya ke jagoranta ne, wannan babban ɗan bindigan Bello Turji ya fara ajiye makaman yaƙin sa domin rungumar sulhu, sannan su ka saki mutanen da su ka yi garkuwa da su, mata da ƙananan yara sama da mutum 30, wanda sun shafe sama da watanni huɗu a hannun su, bayan shiga tsakani da kwamitin sulhu ya yi.
Idan ka ji yadda mutanen da aka ceto daga hannun masu garkuwa da mutanen ke yi wa malaman nan addu'ar alheri sai ka ji tausayin su, domin su na cikin wani bala'i da su ka yanke ƙauna da rayuwa, sai ga taimakon Allah ta hanyar kwamitin sulhu ya zo gare su.
Masu bincike da masana tsaro sun tabbatar da ba za a iya gamawa da matsalar ƴan bindiga gaba ɗaya ba, sai an bi hanyoyin tattaunawa domin samar da sulhu.
Domin yin yaƙin ya na sake taso da sabbin ƴan bindiga ne da sunan ɗaukar fansar iyayen su, idan kuma aka yi sulhu an kashe bakin tsanya.
Hakan ya sa babbar hanyar kawo maslaha a wannan sha'anin ta'addancin, shi ne sulhu, wanda hakan zai kawo zaman lafiya mai ɗorewa, idan sulhun ya yi nasara.
Wannan abin ne gwamnatin tarayya ta fahimta ya sa aka buɗe ƙofar yin sulhu, kuma ta ba da cikakken goyon baya domin magance matsalolin tsaron Arewacin Najeriya, wanda ya bijirewa sulhu a kashe shi, kuma aka yi sa'a su na ganin girman Malaman Addini, kuma su na saurarar su, don haka wannan babbar dama ce da za a iya amfani da ita wurin samar da zaman lafiyar al'umma.
Idan na ji wasu na zagin waɗannan malaman sai su ba ni tausayi, domin kai ka na can ka na ba