Hausa Fulani Peace

Hausa Fulani Peace “Zaman Lafiya tsakanin Hausawa da Fulani, Tushen Cigaban Arewa"

Duk wanda ya saurari tattaunawar DCL da ɗan bindiga Kachallah Dan Sadiya zai ƙara fahimtar wannan hanyar ta sulhu domin ...
20/08/2025

Duk wanda ya saurari tattaunawar DCL da ɗan bindiga Kachallah Dan Sadiya zai ƙara fahimtar wannan hanyar ta sulhu domin samar da zaman lafiya ita ce mafita.

A cikin tattaunawar ya yi wata magana wacce ya kamata al'umma su yi nazari su lura, ya bayyana cewa su da su ke wannan ta'addancin a haka akwai ɓurɓushin ilimi a tare da su, amma ragowar masu tasowa ba su da ilimi ko kaɗan, kenan abin a gaba zai ƙara ƙazancewa ne.

A cikin tattaunawar ya bayyana dalilan su na ɗaukar makami, duk wanda ya saurari dalilan na su, zai fahimci tattaunawa da su domin samar da sulhu shi ne zai magance wannan matsalar.

Wannan ya na ƙara fito da gaskiyar tasirin da sulhu zai yi wanda bindiga ba za ta yi ba, domin ana yaƙar su da bindiga har yanzu, amma ba su dena ba, amma a yankunan da aka samu nasarar sulhu an dena wannan ta'addancin, kenan sulhu shi ne mafitar kawo ƙarshen wannan ta'addanci.

Duk wanda ya san yadda Birnin Gwari ta ke a shekarun baya zai tabbatar da amfani sulhun nan, domin a irin yanayin da yankin ya shiga da kuma yadda aka samu zaman lafiya a yanzu ya na ƙara tabbatar da yadda sulhun ya kasance alheri.

Wannan sulhun da kwamitin Sheikh Musa Asadussunnah ya ke jagoranta muna fatan Allah ya ba su nasara, Allah ya magance mana matsalolin tsaron da ke addabar Najeriya.

Allah ya yi mana maganin ƴan ta'adda da ta'addanci a Najeriya.

Ibrahim Imam Ikara
20 August, 2025.

Malamai ba ‘yan kwangila ba ne, su ne ginshikin zaman lafiyaAkwai jita-jita da ake yadawa cewa wai malamai suna karɓar k...
16/08/2025

Malamai ba ‘yan kwangila ba ne, su ne ginshikin zaman lafiya

Akwai jita-jita da ake yadawa cewa wai malamai suna karɓar kuɗi daga wasu yan siyasa don su wayar da kan jama’a akan matsalar kabilanci. Wannan ƙarya ce mai rauni!

Malamai sun dade suna jagorantar al’umma wajen sulhu, faɗakarwa da kawo zaman lafiya.

➡️ Idan malamai ba su yi magana ba, rikice-rikice na ƙaruwa.
➡️ Idan s**a yi magana kuma, a ce wai ‘yan kwangila ne?

Gaskiya ita ce Malamai suna yin wannan aiki saboda Allah da kishin al’umma, domin zaman lafiya shi ne tushen ci gaban kowa.

Allah yatsare muna kai shiekh Musa Yusuf Asadus Sunnah. Amen

07/08/2025

Sheikh Musa Yusuf Asadus Sunnah kadan daga cikin dalilin da yabashi qarfin gwiwar yin sulhu.

07/08/2025

Shin Yin Sulhu Ya Na Nuna Goyon Bayan Ƴan Ta'adda Ne?

Ibrahim Imam Ikara

A yayin da abubuwa su ka su ka lalace, wani rikici ko ta'addanci ko yaƙi ya ƙi ƙarewa ta hanyar amfani da ƙarfi, babbar hanyar da za a wanzar da zaman lafiya shi ne shiga tsakani da tattaunawa domin yin sulhu.

Ko kaɗan yin sulhu ba ya nuna goyon bayan masu ta'addanci, domin masu aikata ta'addanci mutane ne marasa imani da tausayi da su ke ruguza ƙasa da al'umma ta hanyar zubar da jini da munanan ayyukan su.

Matsalar tsaron nan ta damu kowa, an ɗauki tsawon shekara da shekaru ana yin ta, kwatsam sai aka samu wasu malamai kamar su Sheikh Ahmad Gumi, da irin su Sheikh Musa Asadussunnah da su ke da fahimtar sulhu ne mafitar da za a samu al'umma su zauna lafiya, wannan ta'addanci ya tsaya.

Waɗannan malaman sun yi hakan ne domin nuna kishi da kuma sadaukarwa saboda al'umma ta zauna lafiya, zai iya zama butulci yi wa waɗannan malaman mummunan zato, idan ba a yaba musu ba, bai kamata a zage su ba.

Daga cikin hujjojin da malaman da su ka amince a yi sulhu su ke dogara da su akwai tasirin da sulhun ya yi a wasu sassan jihar Kaduna, misali hanyar Kaduna zuwa Abuja, yankin Birnin Gwari, yankin Giwa, hakan ya sa su ke da fahimtar matuƙar za a bi wannan mataki na sulhu al'umma za ta iya samun zaman lafiya da aminci a hanyoyi da garuruwa.

Wannan matsala ta ta'addanci da yankin Arewa ya ke ciki wani abu ne da wasu ba sa son ya ƙare, shi ya sa a duk lokacin da aka ɗakko hanyar daƙile harkokin ta'addanci a ke samun wasu su na ƙara ɗaukar nauyin ruruta wutar domin ba sa son a samu zaman lafiya, wanda har a cikin masu iƙirarin su malaman addini ne ana samun waɗanda ba sa son matsalar ta tsaya saboda sun karɓo kwangilar ruruta wutar fitinar ta hanyar tunzura al'umma da kalaman ɓatanci.

05/08/2025
Allah Ne Kaɗai Zai Biya Ku Da Irin Ƙoƙarin Da Ku Ke Yi Domin Samar Da Zaman Lafiyar Al'umma A Arewacin NajeriyaIbrahim I...
05/08/2025

Allah Ne Kaɗai Zai Biya Ku Da Irin Ƙoƙarin Da Ku Ke Yi Domin Samar Da Zaman Lafiyar Al'umma A Arewacin Najeriya

Ibrahim Imam Ikara

Duk wanda ya saurari bayanan Sheikh Musa Yusuf Asadussunnah kan namijin ƙoƙarin da kwamitin su na sulhu ya ke yi wurin samar da zaman lafiya a yankin da a ke fama da matsalar ƴan bindiga, da kuma yadda su ke sadaukar da rayukan su domin maslahar al'umma da zaman lafiyar al'umma dole ka tausaya musu, kuma ka yi musu addu'ar alheri.

Daga cikin irin nasarar da kwamitin da Malam Musa Asadussunnah ya ke jagoranta ne, wannan babban ɗan bindigan Bello Turji ya fara ajiye makaman yaƙin sa domin rungumar sulhu, sannan su ka saki mutanen da su ka yi garkuwa da su, mata da ƙananan yara sama da mutum 30, wanda sun shafe sama da watanni huɗu a hannun su, bayan shiga tsakani da kwamitin sulhu ya yi.

Idan ka ji yadda mutanen da aka ceto daga hannun masu garkuwa da mutanen ke yi wa malaman nan addu'ar alheri sai ka ji tausayin su, domin su na cikin wani bala'i da su ka yanke ƙauna da rayuwa, sai ga taimakon Allah ta hanyar kwamitin sulhu ya zo gare su.

Masu bincike da masana tsaro sun tabbatar da ba za a iya gamawa da matsalar ƴan bindiga gaba ɗaya ba, sai an bi hanyoyin tattaunawa domin samar da sulhu.

Domin yin yaƙin ya na sake taso da sabbin ƴan bindiga ne da sunan ɗaukar fansar iyayen su, idan kuma aka yi sulhu an kashe bakin tsanya.

Hakan ya sa babbar hanyar kawo maslaha a wannan sha'anin ta'addancin, shi ne sulhu, wanda hakan zai kawo zaman lafiya mai ɗorewa, idan sulhun ya yi nasara.

Wannan abin ne gwamnatin tarayya ta fahimta ya sa aka buɗe ƙofar yin sulhu, kuma ta ba da cikakken goyon baya domin magance matsalolin tsaron Arewacin Najeriya, wanda ya bijirewa sulhu a kashe shi, kuma aka yi sa'a su na ganin girman Malaman Addini, kuma su na saurarar su, don haka wannan babbar dama ce da za a iya amfani da ita wurin samar da zaman lafiyar al'umma.

Idan na ji wasu na zagin waɗannan malaman sai su ba ni tausayi, domin kai ka na can ka na ba

19/07/2025

WAAZIN WALIMAR AUREN RABI DA ANGONTA AMINU DAGA MASSALLACIN NURUL ISLAM EREKE JUNCTION KARMO FCT

MAI GABATARWA MALAM ALIYU ABDULLAHI AKWAI ALLAH DA ALARAMMA SHAFI'U SULEJA

ALLAH YASA ALBARKA ACIKIN WANAN AUREN

18/07/2025

KHUDUBAR JUMA'A KAI TSAYE DAGA SABON MASALLACIN A'A RANO DAKE HANYAR KARMO-KADO LIFE CAMP ROAD FCT ABUJA

MAI TAKEN SAKACIN DA SHUWAGABANIN KEYI DA HAQQIN AL'UMMARSU

TARE DA MALAM USMAN HAMZA ALBAYAN IKARA

YAU JUMA'A 18TH JULY 2025

Allah Ya yi rahama ga Baba Buhari, Ya sanya Aljannah ta zama makomarsa tare da sauran magabatan mu.
16/07/2025

Allah Ya yi rahama ga Baba Buhari, Ya sanya Aljannah ta zama makomarsa tare da sauran magabatan mu.

Jita-jita da Karya Suna da Ila a Rikicin Kabilanci......Yawan yada jita-jita da ƙarya tsakanin al’umma, musamman akan Fu...
13/07/2025

Jita-jita da Karya Suna da Ila a Rikicin Kabilanci......

Yawan yada jita-jita da ƙarya tsakanin al’umma, musamman akan Fulani da Hausawa, na daga cikin abubuwan da ke ƙara rura wutar rikicin kabilanci. Ya kamata mu daina karɓa da yada labaran da ba su da tushe. Mu rika bincike, mu dinga tambaya kafin mu yarda.

Sako mai karfi:

Kafin ka yada labari, ka tabbatar da gaskiyarsa. Saboda

Yanda Kasan Ta'asdubanci Ta Kungiyanci Yake Haram Kuma Mai Yinsu Ba Musulunci Ya Koya Mashi Ba To Haka Muda Fulani Duk D...
08/07/2025

Yanda Kasan Ta'asdubanci Ta Kungiyanci Yake Haram Kuma Mai Yinsu Ba Musulunci Ya Koya Mashi Ba To Haka

Muda Fulani Duk Daya Muke Sai Wanda Yafi Wani Tsoron Allah Amma Azzaluman Cikinsu Zaluncin Da Suke Bama Musulmi Ba Musuluncinma Baya Tare Dasu

Qabilanci Haramunne....!!!!

07/07/2025

Address

Abuja

Telephone

+2349059471717

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Fulani Peace posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Fulani Peace:

Share