Hausa Fulani Peace

Hausa Fulani Peace “Zaman Lafiya tsakanin Hausawa da Fulani, Tushen Cigaban Arewa"

05/08/2025
Allah Ne Kaɗai Zai Biya Ku Da Irin Ƙoƙarin Da Ku Ke Yi Domin Samar Da Zaman Lafiyar Al'umma A Arewacin NajeriyaIbrahim I...
05/08/2025

Allah Ne Kaɗai Zai Biya Ku Da Irin Ƙoƙarin Da Ku Ke Yi Domin Samar Da Zaman Lafiyar Al'umma A Arewacin Najeriya

Ibrahim Imam Ikara

Duk wanda ya saurari bayanan Sheikh Musa Yusuf Asadussunnah kan namijin ƙoƙarin da kwamitin su na sulhu ya ke yi wurin samar da zaman lafiya a yankin da a ke fama da matsalar ƴan bindiga, da kuma yadda su ke sadaukar da rayukan su domin maslahar al'umma da zaman lafiyar al'umma dole ka tausaya musu, kuma ka yi musu addu'ar alheri.

Daga cikin irin nasarar da kwamitin da Malam Musa Asadussunnah ya ke jagoranta ne, wannan babban ɗan bindigan Bello Turji ya fara ajiye makaman yaƙin sa domin rungumar sulhu, sannan su ka saki mutanen da su ka yi garkuwa da su, mata da ƙananan yara sama da mutum 30, wanda sun shafe sama da watanni huɗu a hannun su, bayan shiga tsakani da kwamitin sulhu ya yi.

Idan ka ji yadda mutanen da aka ceto daga hannun masu garkuwa da mutanen ke yi wa malaman nan addu'ar alheri sai ka ji tausayin su, domin su na cikin wani bala'i da su ka yanke ƙauna da rayuwa, sai ga taimakon Allah ta hanyar kwamitin sulhu ya zo gare su.

Masu bincike da masana tsaro sun tabbatar da ba za a iya gamawa da matsalar ƴan bindiga gaba ɗaya ba, sai an bi hanyoyin tattaunawa domin samar da sulhu.

Domin yin yaƙin ya na sake taso da sabbin ƴan bindiga ne da sunan ɗaukar fansar iyayen su, idan kuma aka yi sulhu an kashe bakin tsanya.

Hakan ya sa babbar hanyar kawo maslaha a wannan sha'anin ta'addancin, shi ne sulhu, wanda hakan zai kawo zaman lafiya mai ɗorewa, idan sulhun ya yi nasara.

Wannan abin ne gwamnatin tarayya ta fahimta ya sa aka buɗe ƙofar yin sulhu, kuma ta ba da cikakken goyon baya domin magance matsalolin tsaron Arewacin Najeriya, wanda ya bijirewa sulhu a kashe shi, kuma aka yi sa'a su na ganin girman Malaman Addini, kuma su na saurarar su, don haka wannan babbar dama ce da za a iya amfani da ita wurin samar da zaman lafiyar al'umma.

Idan na ji wasu na zagin waɗannan malaman sai su ba ni tausayi, domin kai ka na can ka na ba

19/07/2025

WAAZIN WALIMAR AUREN RABI DA ANGONTA AMINU DAGA MASSALLACIN NURUL ISLAM EREKE JUNCTION KARMO FCT

MAI GABATARWA MALAM ALIYU ABDULLAHI AKWAI ALLAH DA ALARAMMA SHAFI'U SULEJA

ALLAH YASA ALBARKA ACIKIN WANAN AUREN

18/07/2025

KHUDUBAR JUMA'A KAI TSAYE DAGA SABON MASALLACIN A'A RANO DAKE HANYAR KARMO-KADO LIFE CAMP ROAD FCT ABUJA

MAI TAKEN SAKACIN DA SHUWAGABANIN KEYI DA HAQQIN AL'UMMARSU

TARE DA MALAM USMAN HAMZA ALBAYAN IKARA

YAU JUMA'A 18TH JULY 2025

Allah Ya yi rahama ga Baba Buhari, Ya sanya Aljannah ta zama makomarsa tare da sauran magabatan mu.
16/07/2025

Allah Ya yi rahama ga Baba Buhari, Ya sanya Aljannah ta zama makomarsa tare da sauran magabatan mu.

Jita-jita da Karya Suna da Ila a Rikicin Kabilanci......Yawan yada jita-jita da ƙarya tsakanin al’umma, musamman akan Fu...
13/07/2025

Jita-jita da Karya Suna da Ila a Rikicin Kabilanci......

Yawan yada jita-jita da ƙarya tsakanin al’umma, musamman akan Fulani da Hausawa, na daga cikin abubuwan da ke ƙara rura wutar rikicin kabilanci. Ya kamata mu daina karɓa da yada labaran da ba su da tushe. Mu rika bincike, mu dinga tambaya kafin mu yarda.

Sako mai karfi:

Kafin ka yada labari, ka tabbatar da gaskiyarsa. Saboda

Yanda Kasan Ta'asdubanci Ta Kungiyanci Yake Haram Kuma Mai Yinsu Ba Musulunci Ya Koya Mashi Ba To Haka Muda Fulani Duk D...
08/07/2025

Yanda Kasan Ta'asdubanci Ta Kungiyanci Yake Haram Kuma Mai Yinsu Ba Musulunci Ya Koya Mashi Ba To Haka

Muda Fulani Duk Daya Muke Sai Wanda Yafi Wani Tsoron Allah Amma Azzaluman Cikinsu Zaluncin Da Suke Bama Musulmi Ba Musuluncinma Baya Tare Dasu

Qabilanci Haramunne....!!!!

07/07/2025
07/07/2025

Raba hausawa da Fulani bakomai face faɗa da Addinin Musulunci

06/07/2025

KAI TSAYE GAGARUMAR MUHADARA DAGA BABBAN MASALLACIN JUMA'A NA DEIDEI YAN TOMATOE FCT ABUJA

MAITAKEN:FITINAR QABILANCI A AREWACIN NIGERIA.

MALAMI NA UKU MALAM USMAN HAMZA ALBAYAN IKARA ALLARAMMA TUKUR JAKADA

6TH JULY 2025CE-11TH MUHARRAM 1447AH

ALLAH YABADA IKON SAURARO AMEEN.

06/07/2025

MUHADARA
ME TAKEN
FITINAR QABILANCI A AREWACIN NIGERIA

ME KARATU NA 2
TARE DA
SHAIKH MUHAMMAD SANI ISAH
DA
ALARAMMA SHAFI'U

Masjidu Abi huraira DEI-DEI ABUJA
11/01/1447
06/07/2025

Faisal Idris
MUHADARA
ME TAKEN
FITINAR QABILANCI A AREWACIN NIGERIA
TARE DA
SHAIKH ABDURRASHID SHUAIBU
DA
ALARAMMA IBRAHIM ABDURRASHID

Masjidu Abi huraira DEI-DEI ABUJA
11/01/1447
06/07/2025

Faisal Idris

06/07/2025

KAI TSAYE GAGARUMAR MUHADARA DAGA BABBAN MASALLACIN JUMA'A NA DEIDEI YAN TOMATOE FCT ABUJA

MAITAKEN:FITINAR QABILANCI A AREWACIN NIGERIA.

MALAMI NA FARKO MALAM ABDURRASHID SHUAIBU SABURI DA IBRAHIM ABDURRASHID

YAU LAHADI 6TH JULY 2025CE-11TH MUHARRAM 1447AH

ALLAH YABADA IKON SAURARO AMEEN.

Address

Abuja

Telephone

+2349059471717

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Fulani Peace posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Fulani Peace:

Share