20/06/2026
Da Dumi Dumi || Kakakin Majalisar Wakilai, Akin Rotimi Jnr, Ya Shiga Takun-Saka da Tsagin ‘Yan Adawa
Daga Uduimoh Ben
Majalisar Wakilai ta Najeriya ta bayyana cewa nauyin samar da mafita, ƙarfafa hukumomi, da tallafa wa aiwatar da manufofi yadda ya kamata nauyi ne na kowa da kowa, ba wai na wani ɓangare ko tsagi kaɗai ba.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kakakin Majalisar Wakilai, Akin Rotimi Jnr, ya fitar domin mayar da martani kan batutuwan da Tsagin ‘Yan Adawa (Minority Caucus) s**a tayar.
Sanarwar ta amince cewa batutuwan da aka gabatar suna nuna damuwar jama'a ta gaskiya, tare da jaddada bukatar ci gaba da sa ido, haɗin kai, da haɗin gwiwa tsakanin dukkan rassan gwamnati.
Sai dai Rotimi Jnr ya bayyana cewa matsalolin tsaro da Najeriya ke fuskanta ba sabbin matsaloli ba ne, kuma ba za a iya magance su da mataki guda kawai ba. Ya ce Majalisar Dokoki tare da bangaren zartarwa da hukumomin tsaro suna ci gaba da ƙarfafa tsarin tsaron ƙasa ta hanyar dokoki, kasafin kuɗi, da sa ido kan ayyukan gwamnati.
Sanarwar ta kuma nuna cewa hukumomin tsaro suna ci gaba da gudanar da ayyuka a sassa daban-daban na ƙasar nan, ciki har da murkushe ƙungiyoyin masu aikata laifuka, ceto waɗanda aka sace, da samar da zaman lafiya a yankunan da ke fuskantar matsaloli.
Rotimi Jnr ya ƙara da cewa ‘yan majalisa, ba tare da la’akari da jam’iyyar da suke ciki ba, ba su takaita ga yin sharhi kawai ba. Ya buƙaci Tsagin ‘Yan Adawa su yi amfani da hanyoyin da kundin tsarin mulki ya tanada wajen tsara martanin ƙasa da sauye-sauyen da ake buƙata.
Sanarwar ta tunatar da Tsagin ‘Yan Adawa cewa su ma wani ɓangare ne na gwamnati ta fuskar majalisa, kuma suna da alhakin taimakawa wajen ƙarfafa tsaron ƙasa.
A gefe guda kuma, Tsagin ‘Yan Adawa ya buƙaci shugabancin Majalisar Wakilai ya ɗauki alhakin da ya rataya a wuyansa, yana mai cewa majalisa ba za ta zama yar rakiyar bangaren zartarwa ba.
A wata sanarwa da sabon kakakin Tsagin ‘Yan Adawa, Afam Ogene, ya fitar, ya ce .