Duniya INA Labari

Duniya INA Labari Shafi ne da aka samar da zaiyi kokari na shiga lungu da sako domin kawo maku sahihan Labaran abubuwan da suke faruwa.

Kuma Kofar mu a bude take na tallata maku hajar ku ga sama da mutun 100,000 da muke dasu, masu bibiyar shafin Ankirkiri wanan shafin mai suna DUNIYA INA LABARI saboda inganta harshen hausa da kuma kawo maku
1)Labarai.
2)Ilmantarwa.
3)Nishadantarwa.
4)fadakarwa.

Tinubu ya yi kira ga malaman addini da su yi amfani da muryarsu wajen yaki da ta’addanciShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ...
10/08/2026

Tinubu ya yi kira ga malaman addini da su yi amfani da muryarsu wajen yaki da ta’addanci

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga malaman addini a Najeriya, Afirka da sauran sassan duniya da su ci gaba da anfani da muryoyinsu kan yaki da ta’addanci, garkuwa da mutane, da kuma amfani da addini wajen kashe-kashe da tashin hankali. Tinubu ya ce babu wata ibada ta gaskiya da za ta samu ci gaba ta hanyar zubar da jinin mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.

Shugaban Ƙasar ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadi a Kano, a cikin saƙon fatan alheri da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya isar a madadinsa a wajen babban Mauludin Shehu Ahmad Al-Tijani (RTA). Ya ce malaman addini na da muhimmiyar rawar da za su taka wajen wayar da kan matasa, koyar da zaman lafiya, ilimin addini da kyawawan ɗabi’u, tare da yin kira ga shugabannin siyasa da su yi adalci da nuna tausayi.

Tinubu ya ce matsalolin da duniya ke fuskanta, da s**a haɗa da yaƙe-yaƙe, matsin tattalin arziki, yunwa, ta’addanci da rikice-rikicen da ake haddasawa ta hanyar addini da ƙabilanci, sun ƙara nuna muhimmancin rawar shugabannin addini wajen wanzar da zaman lafiya. Ya ce ɗariƙar Tijjaniyya, saboda faɗin hanyoyin sadarwarta a Afirka ta Yamma da Arewa, na da damar taimakawa wajen sasanta rikice-rikice, yaƙi da tsattsauran ra’ayi da jagorantar matasa zuwa tsarkin zuciya.

Shugaban Ƙasar ya kuma bayyana Najeriya a matsayin ƙasa mai matuƙar muhimmanci ga zaman lafiyar yankin saboda matsayinta a tsakanin Afirka ta Yamma, Sahel, Tafkin Chadi da Tekun Guinea. Ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da kare ’yancin ’yan Najeriya na gudanar da addininsu, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da malaman addini da sarakunan gargajiya domin tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da mutunta juna.

Tinubu ya kuma yi ta’aziyyar marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya ce rashinsa ya yi matuƙar tasiri a taron, yana mai bayyana shi a matsayin malami, uba kuma mai fafutukar zaman lafiya da kyakkyawar fahimta.

‎Alummar Jihar Nasarawa sunyi murna da ayyukan Shugaba Tinubu na Raya Kasa.‎‎Tinubu na shirin Sauya tsarin arewa daga Du...
09/08/2026

‎Alummar Jihar Nasarawa sunyi murna da ayyukan Shugaba Tinubu na Raya Kasa.

‎Tinubu na shirin Sauya tsarin arewa daga Duhu zuwa Haske.

‎ A yayin da ake ci gaba da bayyana ayyukan raya ƙasa da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa a sassan Najeriya, wasu wakilan kafafen yaɗa labarai sun isa Jihar Nasarawa domin ganin ayyukan da idonsu tare da tantance yadda suke tasiri ga rayuwar al’ummar jihar.

‎Ziyarar ta bai wa wakilan kafafen yaɗa labarai damar zagayawa wasu muhimman wurare da ake aiwatar da manyan ayyukan more rayuwa, da wakilan Fadar Shugaban kasa, Karkashin Hadimin Shugaba Tinubu, Bayo Onanuga, da Hadimin Shugaba Tinubu a bangaren kafafen yada labarai, Abdulaziz-abdulaziz, da Dada Olusegun, da sauran tawagar su.
‎A ziyarci masana’antun bunƙasa sana’o’in hannu a ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Tinubu, tare da haɗin gwiwar gwamnatin Jihar Nasarawa ƙarƙashin jagorancin Gwamna jihar, Injiniya Abdullahi A. Sule.

‎Manyan ayyukan more rayuwa
‎Daga cikin wuraren da tawagar ta ziyarta akwai katafariyar Sakatariyar Gwamnatin Jihar Nasarawa, wadda ke daga cikin manyan gine-ginen dgwamnati da ake amfani da su wajen inganta ayyukan gudanar da mulki da samar da yanayi mai kyau ga ma’aikatan gwamnati da al’umma.

‎Haka kuma, tawagar ta duba wasu manyan hanyoyi, ciki har da hanyar Shabu, wadda ke da muhimmiyar alaƙa da zirga-zirgar jama’a da harkokin kasuwanci zuwa wasu sassan jihar da kuma hanyar Taraba.

‎Wadannan ayyuka, a cewar mazauna yankin, suna taimakawa wajen rage wahalhalun sufuri tare da buɗe ƙofofin kasuwanci da zuba jari.

‎Wata muhimmiyar cibiyar da tawagar ta ziyarta ita ce wuraren koyar da walda da sauran sana’o’in hannu, waɗanda aka samar domin bai wa matasa damar samun sana’a da dogaro da kansu.

An bayyana cewa irin waɗannan shirye-shirye na da matuƙar muhimmanci wajen rage zaman kashe wando da kuma bai wa matasa damar zama masu amfani ga kansu, iyalansu da al’umma.

Shugaba Tinubu, tare da haɗin gwiwar gwamnatin Jihar Nasarawa, na

09/08/2026

‎“Duk wasu ayyuka da akeyi a Jihar Nasarawa, Kudi ne da Shugaba Tinubu ya ware don gudanar da ayyuka a dukkan jihohi” inji Sakataren Gwamnatin Jihar Nasarawa, Injiniya Labaran Magaji.

08/08/2026

Aikin sake gina da faɗaɗa babbar hanyar Makurdi zuwa Enugu wadda ta haɗa jihohin Arewa da Kudu-maso-Gabas mai tsahon kilomita 266 wadda shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu yake gudanarwa.

:

Shugaba Tinubu ya karɓi baƙuncin Babban Khalifan Tijjaniyya na Aljeriya a Fadar A*o RockShugabannin ɗarikar Tijjaniyya d...
07/08/2026

Shugaba Tinubu ya karɓi baƙuncin Babban Khalifan Tijjaniyya na Aljeriya a Fadar A*o Rock

Shugabannin ɗarikar Tijjaniyya daga Najeriya, Aljeriya da Senegal sun kai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ziyara a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Tawagar ta haɗa da Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi daga Najeriya, Babban Khalifan Tijjaniyya na Aljeriya, Sheikh Ali Al-Arabi, da kuma fitaccen malamin addinin Musulunci daga Senegal, Sheikh Muhammad Al-Mahy.

Ziyarar ta gudana ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda shugabannin s**a gana da Shugaba Tinubu.

📸: Fadar Shugaban Ƙasa

07/08/2026

Inda Ranka

Sojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kwato Dabbobi 281 da ’Yan Bindiga S**a Sace a SakkwatoDaga Aliyu ...
05/08/2026

Sojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kwato Dabbobi 281 da ’Yan Bindiga S**a Sace a Sakkwato

Daga Aliyu Samba

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta 8 Division Garrison sun ceto mutum 14 da aka yi garkuwa da su tare da kwato dabbobi 281 da wasu ’yan bindiga s**a sace bayan sun kai hari ƙauyen Horo Birni da ke Ƙaramar Hukumar Shagari a Jihar Sakkwato.

Wata majiya mai tushe a rundunar sojin ta shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata, inda dakarun s**a gaggauta kai ɗauki bayan samun kiran neman agaji daga mazauna yankin.

Majiyar ta ce da isar sojojin, sun yi arangama da ’yan bindigar da ke tafiya da mutanen da s**a yi garkuwa da su tare da dabbobin da s**a sace daga ƙauyen.

Ta bayyana cewa sojojin sun yi wa ’yan bindigar ruwan wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa cikin ruɗani bayan sun samu raunukan harbin bindiga, s**a bar mutanen da s**a sace da kuma dabbobin.

A cewar majiyar, sojojin sun yi nasarar ceto mutane 14 tare da kwato shanu 195, tumaki 84, rakuma biyu da kuma babura biyu.

Ta ƙara da cewa gaggawar da sojojin s**a yi wajen kai ɗauki ta taimaka wajen ceton rayuka da dukiyoyin al’umma, tana mai yabawa haɗin gwiwar jami’an tsaro da ya taimaka wajen nasarar aikin.

Majiyar ta jaddada cewa dakarun sojin na ci gaba da kasancewa cikin shiri domin yaƙi da duk wani nau’in ta’addanci da laifuffuka, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken haɗin kai da kuma kai rahoton duk wani abin da ba su yarda da shi ba.

Manufofin Tinubu Na Bunƙasa Masana'antu Suna Samar Da Ayyuka, Ayyukan Yi Da Ƙirƙire-ƙirƙire – Ministan Yaɗa LabaraiMinis...
05/08/2026

Manufofin Tinubu Na Bunƙasa Masana'antu Suna Samar Da Ayyuka, Ayyukan Yi Da Ƙirƙire-ƙirƙire – Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce manufofin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na bunƙasa masana'antu a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata suna ci gaba da samar da manyan ayyuka, ayyukan yi, ƙirƙire-ƙirƙire, da damarmakin tattalin arziki a faɗin ƙasar nan.

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Talata a hedikwatar Hukumar Bunƙasa Kimiyya da Injiniya ta Ƙasa (NASENI) da ke Abuja, yayin rangadin da Tawagar Yaɗa Labarai ta Fadar Shugaban Ƙasa ta kai hukumar.

Ya ce an ƙaddamar da Rangadin Yaɗa Labarai na Ajandar Sabunta Fata ne domin bai wa 'yan Nijeriya damar ganin ayyuka da shirye-shiryen da Gwamnatin Tarayya take aiwatarwa da idon su.

Ministan ya ce: “Muna son 'yan Nijeriya su gani da idon su yadda manufofin gwamnati ke komawa ayyuka na zahiri, samar da ayyukan yi, ƙirƙire-ƙirƙire, da damarmaki. Ana ƙara tabbatar da gaskiya idan hukumomin gwamnati suna hulɗa kai-tsaye da jama'a, kuma ana ƙara ƙarfafa ɗaukar nauyi idan 'yan ƙasa za su iya tantance cigaban da aka samu da kansu.”

Idris ya bayyana NASENI a matsayin muhimmiyar hukuma da ke jagorantar sauyin masana'antun Nijeriya ta hanyar kimiyya, aikin injiniya da fasaha, inda take aiwatar da ayyuka a fannonin masana'antun cikin gida, makamashi mai sabuntawa, aikin gona na zamani, fasahar zamani, da bunƙasa ƙwarewar ma'aikata.

A cewar sa, manufar Shugaba Tinubu ita ce gina tattalin arziki mai ɗorewa kuma mai dogaro da kai, wanda ya ta'allaƙa kan ƙirƙire-ƙirƙire, ƙara darajar kayayyakin cikin gida da kuma ƙarfafa gasa a fannin masana'antu.

Ya ce: “Manufar mu a bayyane take; ita ce sauya Nijeriya daga ƙasar da ta fi zama mai amfani da kayayyaki zuwa ƙasar da ke samarwa, ƙirƙire-ƙirƙire da fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje.”

Ministan ya ƙara da cewa Ajandar Sabunta Fata ta sanya bunƙasa masana'antu, fasaha da ƙarfafa matasa a matsayin ginshiƙan sauya tattalin arzikin ƙasa, ta

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Aikin Gyaran Titin Mando–Birnin Gwari Kan Naira Biliyan 178.1Daga Aliyu SambaGwamnatin ...
04/08/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Aikin Gyaran Titin Mando–Birnin Gwari Kan Naira Biliyan 178.1

Daga Aliyu Samba

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da aikin sake gina Titin Mando zuwa Birnin Gwari mai tsawon kilomita 122.8 a Jihar Kaduna, wanda aka ware wa kuɗaɗen da s**a kai Naira biliyan 178.1. Titin ya tashi daga Mando da ke kusa da Filin Jirgin Sama na Kaduna zuwa iyakar Jihar Neja.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya wakilta wajen ƙaddamar da aikin a ranar Talata, ya ce aikin zai taimaka wajen inganta harkokin sufuri, ƙarfafa tsaro da kuma bunƙasa tattalin arzikin yankin. Ya ce titin na daga cikin manyan ayyukan raya ƙasa da za su ƙara haɗa yankunan Arewacin Najeriya da Kudu maso Yammacin ƙasar, tare da sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki.

Shugaban ya bayyana cewa aikin na cikin manyan ayyukan hanyoyin tarayya da gwamnatinsa ta amince da su a watan Mayun 2026 domin faɗaɗa ababen more rayuwa a faɗin ƙasar. Ya kuma tuna cewa tun lokacin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa a shekarar 2022 ya yi alƙawarin sake gina titin idan aka zaɓe shi, yana mai cewa fara aikin ya nuna yadda gwamnatinsa ke cika alƙawuran da ta ɗauka ga 'yan Najeriya.

Tinubu ya ce tsawon shekaru da dama Titin Birnin Gwari ya kasance cikin halin lalacewa sakamakon rashin kulawa da gyara yadda ya kamata. Ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya ta ƙuduri aniyar kawo ƙarshen wannan matsala ta hanyar ci gaba da zuba jari a ayyukan hanyoyi, yana mai jaddada cewa matsayin Jihar Kaduna a matsayin ƙofar shiga yankin Arewa ya sa samar da ingantattun hanyoyi ya zama wajibi domin bunƙasa kasuwanci, zirga-zirga da ci gaban yankin.

Da yake jawabi, Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya ce aikin ya nuna ƙudirin gwamnatin Shugaba Tinubu na samar da ababen more rayuwa da za su inganta rayuwar al'umma kai tsaye. Ya ce baya ga ƙarfafa tsaro a hanyar, aikin zai buɗe damar bunƙasa noma a yankin, wanda zai taimaka wajen ƙara samar da abinci da kuma yaƙi da yunwa.

Umahi ya kuma bayya

04/08/2026

Aikin samar da gidaje na gwamnatin tarayya Renewed Hope Estate and Housing ya samar da gidaje ga ma buƙata da samar ayyukan yi ga matasa kamar yadda muka shaida a yayin ziyarar

Address

<fg=bff0000f> Zaku Iya Samun Labaran Mu A Kasashen Duniya, Musamman, Kasashen Africa, Nigeria, Niger, Ghana, Chadi. . . .
Abuja
SOKOTO,KANO,KADUNA,ABUJA,KATSINA,LAGOS

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Duniya INA Labari posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Duniya INA Labari:

Shortcuts

Share