Duniya INA Labari

Duniya INA Labari Duniya INA Labari shafi ne da muka samar domin. Labarai
Ilmantarwa
Fadakarwa
Nishadantarwa
(1)

Ankirkiri wanan shafin mai suna DUNIYA INA LABARI saboda inganta harshen hausa da kuma kawo maku
1)Labarai.
2)Ilmantarwa.
3)Nishadantarwa.
4)fadakarwa.

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Daukar Ma’aikata a Mataki na Biyu na Shirin Renewed Hope Ta Ƙarƙashin Hukumar NDEGwamnatin Tar...
29/07/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Daukar Ma’aikata a Mataki na Biyu na Shirin Renewed Hope Ta Ƙarƙashin Hukumar NDE

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da mataki na biyu na daukar ma’aikata karkashin shirin Renewed Hope Employment Initiative (RHEI) ƙarƙashin Hukumar Kula da Ayyukan Yi (NDE), domin rage rashin aikin yi da kuma koyar da matasa dabarun samun sana’o’i da cigaba.

Shugaban Hukumar NDE, Mista Silas Agara ne ya bayyana hakan a yayin kaddamar da Shafin rajista ta yanar gizo a birnin Abuja, inda ya ce tsarin zai kasance cikin gaskiya da adalci, kuma an tsara shi ne domin bai wa kowane dan kasa dama ba tare da nuna bambanci ba. “Mun kammala mataki na farko cikin nasara, kuma mun samar da kayan aiki da cibiyoyi a dukkan jihohi 36 da babban birnin tarayya don gudanar da wannan mataki na biyu cikin sauki,” in ji shi.

Agara ya ce duk wanda ke son shiga shirin zai bukaci lambar NIN da kuma shedar zama a cikin wata jiha ta Najeriya, ko da ba asalin can jihar yake ba. Ya bayyana cewa ’yan Najeriya masu shekaru tsakanin 18 zuwa 45 ne kadai za su iya yin rajista, kuma za su samu horo a fannoni sama da 30 na sana’o’in hannu da fasahar zamani, bisa bukatun tattalin arzikin kowace jiha. “Misali, abin da ke da amfani a Abia ba lallai ya dace da Adamawa ba, shi ya sa muka tsara horon bisa ga bukatun kowacce jiha,” in ji Agara.

An bude Shafin rajista ta yanar gizo kamar haka: www.nderegistrationportal.ng
Za a cigaba da rejista tun daga 28 ga Yuli zuwa 11 ga Agusta, 2025, yayin da za a fara tantance bayanan masu nema daga 12 zuwa 22 ga Agusta. Ya gargadi jama’a da su guji yaudarar masu karbar kudi ko amfani da hanyoyin da ba na hukuma ba. “Shirin kyauta ne gaba daya, kuma duk wani yunkuri na damfara, a gaggauta kai rahoton ga ofisoshin NDE na jihohi ko hedikwata,” in ji shi.

Tinubu Ya Gwangwaje 'Yan Super Falcons Da Kyautar Dala 100,000 Da Kuma Gida Kowannen SuShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu y...
28/07/2025

Tinubu Ya Gwangwaje 'Yan Super Falcons Da Kyautar Dala 100,000 Da Kuma Gida Kowannen Su

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya karrama 'yan rundunar ƙwallon ƙafa ta mata ta Nijeriya, wato Super Falcons, da kyautar karramawa ta ƙasa da kuma kyautar kuɗi da ta gidan kwana saboda nasarar su a gasar Kofin Ƙasashen Afrika na Mata (WAFCON), wanda aka gama ranar Asabar, inda s**a ciyo kofin a karo na 10.

A wurin wata babbar walima da aka yi a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Dutsen A*o a ranar Litinin, Tinubu ya ba da lambar girma ta ƙasa ta Officer of the Order of the Niger (OON) ga kowace daga cikin 'yan wasan su 24.

Haka kuma ya gwangwaje kowace 'yar wasa da kyautar tsabar kuɗi Naira wadda ta yi daidai da Dalar Amurka dubu ɗari ($100,000), da kuma gida mai dakunan kwana uku.

Bugu da ƙari, kowanne daga cikin ma'aikatan kulob ɗin ƙwallon ƙafar an ba shi kyautar dala dubu hamsin ($50,000) (a naira), a matsayin godiya saboda muhimmiyar rawar da s**a taka wajen samun nasarar.

“Wannan ƙungiya ta ƙara janyo wa Nijeriya abin alfahari a duniya," inji Tinubu. “Jajircewar ku da zummar ku da wasan ku sun kasance abin koyo ba kawai ga 'yan wasa masu tasowa ba har ma ga kowane ɗan Nijeriya.

“Na karɓi wannan kofi a madadin dukkanin 'yan Nijeriya, kuma na ce maku: mun gode da sadaukarwar ku da hoɓɓasan ku, da kuma tuna mana da ƙarfin halin 'yan Nijeriya da kuka yi.

“A madadin ƙasar nan da ke cike da godiya, a nan ina bai wa dukkan 'yan wasa da ma'aikatan kulob su 11 kyautar karramawa ta ƙasa mai suna 'Officer of the Order of the Niger' (OON).

“Bugu da ƙari, ina ba da umurnin cewa a ba kowace 'yar wasa da kowane ma'aikacin kulob kyautar gida mai daki uku.

“Wani ƙari kuma shi ne, akwai kyautar tsabar kuɗi a naira wadda ta yi daidai da $100,000 ga kowacce daga cikin 'yan wasa 24, da kuɗi da ya yi daidai da $50,000 ga kowanne daga cikin ma'aikatan kulob su 11.

“Ina ƙara taya ku murna, kuma zan ci gaba da yi maku addu'a. Da wannan, ruhin Nijeriya ba zai gaza ba kuma ba zai taɓa mutuwa ba.”

Gwamnatin Tarayya Ta Tura Manyan Motocin Yaki Guda Shida Don Yaki da Ƙalubalen Tsaro a Jihar KebbiA wani mataki na karfa...
28/07/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Tura Manyan Motocin Yaki Guda Shida Don Yaki da Ƙalubalen Tsaro a Jihar Kebbi

A wani mataki na karfafa tsaro da dakile ayyukan ‘yan bindiga a jihar Kebbi, Gwamnatin Tarayya ta tura manyan motocin yaƙi da aka fi sani da Armoured Personnel Carriers (APCs) guda shida zuwa jihar domin yaki da ayyukan ta’addanci. Wannan na daga cikin matakan da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke dauka wajen fuskantar matsalolin tsaro a sassan kasar nan.

Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi ne ya bayyana hakan yayin da yake duba motocin a harabar Gidan Gwamnati da ke Birnin Kebbi, tare da nuna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da manyan hafsoshin tsaro na kasa.

Gwamnan ya ce Kebbi, musamman yankin kudancin jihar, na fuskantar hare-hare daga ‘yan bindiga da ke shiga daga jihohin Zamfara da Neja, suna kai farmaki sannan su gudu zuwa maboyarsu. Ya ce tura wadannan motocin zai taimaka wajen hana su sake kai hare-hare da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

“Ina mika godiya ta ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa, da Babban Hafsan Sojojin Kasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, da sauran shugabannin hukumomin tsaro bisa wannan matakin gaggawa da s**a dauka domin kare rayukan al’ummar jihar Kebbi,” in ji Gwamna Idris.

Gwamnan ya kara da cewa gwamnati na kara ba da goyon baya ga jami’an tsaro da kuma iyalan jaruman da s**a rasa rayukansu a fafatawa da ‘yan bindiga, domin tabbatar da cewa an samu zaman lafiya mai dorewa a jihar.

A nasa bangaren, Kwamandan Rundunar 223 Light Tank Battalion da ke Zuru, Laftanar Kanar M. S. Saleh, ya nuna wa gwamnan kayan yaki da aka turo, tare da gode wa gwamnatin tarayya da ta jihar bisa hadin kai da tallafi da suke bayarwa domin ganin an shawo kan matsalar tsaro a jihar.

Ya bukaci al’umma da su ci gaba da hada kai da jami’an tsaro ta hanyar bayar da bayanan sirri da za su taimaka wajen gano maboyar ‘yan ta’adda da kuma hana su samun kafa a cikin al’umma.

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar da Tallafin Naira Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Makarantun Gaba da SakandareGwamnatin Tarayya a...
28/07/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar da Tallafin Naira Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Makarantun Gaba da Sakandare

Gwamnatin Tarayya a ranar Lahadi, ta bayyana sabon shirin tallafi na musamman ga ma’aikatan jami’o’i, kwalejojin ilimi da kuma manyan makarantu a fadin Najeriya, mai suna Tertiary Institution Staff Support Fund (TISSF). Wannan sanarwar ta fito ne daga bakin Daraktar Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Mrs Folasade Boriowo, a Abuja.

Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa ne ya kaddamar da shirin, inda ya bayyana shi a matsayin tsarin tallafi da zai inganta walwala da ci gaban ma’aikatan ilimi, ciki har da malaman dake koyar da darussa da kuma ma’aikatan da ba na koyarwa ba. Ya ce wannan yunkuri wani bangare ne na kokarin gwamnati na tallafa wa ma’aikata domin inganta harkar ilimi a matakin gaba da sakandare.

A cewar Ministan, kowane ma’aikaci da ya cancanta na da damar karbar lamuni har zuwa Naira miliyan goma (N10m), muddin bashin bai wuce kaso 33.3 cikin 100 na jimillar albashin sa na shekara guda ba. Daga cikin abubuwan da za a iya amfani da bashin a kai sun hada da siyan ababen hawa, kula da lafiya, da kuma zuba jari a kananan sana’o’i kamar kiwon kaji.

Za a gudanar da wannan shiri ne tare da hadin gwiwar Bankin Masana’antu (Bank of Industry), domin tabbatar da gaskiya da tsantseni wajen rabon kudaden. Wannan mataki yana daga cikin hanyoyin da gwamnati ke bi domin tabbatar da cewa kudin tallafin ya isa hannun masu bukata yadda ya kamata.

Dr. Alausa ya bayyana cewa wannan shiri na TISSF ya na da nasaba da burin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na sauya fasalin harkar ilimi a Najeriya. Ya ce: “Ba tallafi kawai ba ne; wannan wani tsarin karfafa gwiwa ne ga ma’aikatan ilimi domin su rayu cikin walwala, su samu cigaban sana’a, tare da bayar da gudunmuwa mai amfani ga makarantun da suke aiki.”

Wani Matashi Ya Kone Takardun Makarantar Sa Sakamakon Rashin Samun Aikin Gwamnati Da Ya Yi Tsawon Shekaru BiyarMe za ku ...
27/07/2025

Wani Matashi Ya Kone Takardun Makarantar Sa Sakamakon Rashin Samun Aikin Gwamnati Da Ya Yi Tsawon Shekaru Biyar

Me za ku ce.

Daga Mall Ahmad Ringim

Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Matasan Arewa Sun Gargadi Atiku da El-RufaiKun...
26/07/2025

Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Matasan Arewa Sun Gargadi Atiku da El-Rufai

Kungiyar Matasa Ta Arewa (Northern Youth Frontiers) ta bayyana damuwarsu kan yadda wasu 'yan siyasa ke ƙoƙarin amfani da rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari domin yaudarar mutane da neman samun goyon bayansu.

A cewar kungiyar, Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai sun nuna kamar su abokai ne na Buhari domin su karɓi ƙaunar jama'a, alhali sun shafe shekaru suna adawa da akidu da manufofin Buhari tun yana raye.

Wannan abin da suke yi ruɗi ne, karya ce, kuma cin fuska ne ga marigayin shugaban da ya sadaukar da rayuwarsa ga ƙasar nan.

Kungiyar ta ce waɗannan 'yan siyasa ba su taɓa goyon bayan Buhari ba, kuma yanzu suna ƙoƙarin nuna soyayya ta bogi domin su karɓi ra'ayin mutanen Arewa — musamman bayan mutuwar sa.

“Matasan Arewa ba za su bari a ci zarafin Buhari ba.”

Matasan sun ce ba za su yarda a yi amfani da mutuwar Buhari a matsayin hanyar da za a fake domin yaudarar al’umma ba. Sun kuma roƙi jama’ar Arewa da su yi hankali da siyasar ruɗu da wasu ke ƙoƙarin kawowa a cikin lokaci mai muhimmanci na jimami da girmamawa.

Mutuwar Buhari ba siyasa bace. Lokaci ne na tunani da haɗin kai, ba na neman karɓuwa da nuna ƙarya ba.”

Kungiyar ta ƙara da cewa Atiku da El-Rufai su dakata da wannan salon siyasa, su girmama Buhari, su kuma bar mutanen Arewa su zaɓi gaskiya da amintattu, ba masu nuna soyayya ta ɗan lokaci ba.

Ku dakata da fakewa da mutuwar Buhari. Mutumin da kuka ƙi a raye, ba ku da ikon fakewa da shi bayan ya rasu.

✍️ Northern Youth Frontiers
Sakon Gargaɗi daga Matasan Arewa

26/07/2025

Kalli cikakkiyar Halima Umar Saleh da Arewa24 kan yanda ta fuskanci cin zarafi daga wani abokin aiki a zaman ta BBC.

Zabi daya
25/07/2025

Zabi daya

Rayuwar Marigayi Sarkin Gusau cike take da hidima da sadaukarwa ga jama’a —Shugaba TinubuShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu...
25/07/2025

Rayuwar Marigayi Sarkin Gusau cike take da hidima da sadaukarwa ga jama’a —Shugaba Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhini da jimami kan rasuwar Sarkin Katsinan Gusau, Dr Ibrahim Bello, wanda ya rasu da safiyar Juma’a a birnin tarayya Abuja yana da shekaru 71 a duniya.

A cikin wata sanarwa daga mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yada labarai da dabarun watsa bayanai, Mista Bayo Onanuga, Shugaba Tinubu ya bayyana rasuwar marigayi sarkin a matsayin babban rashi da ya wuce iyakar masarautar Gusau, yana mai cewa rayuwarsa cike take da hidima da sadaukarwa ga jama’a a matakai daban-daban na rayuwa.

Shugaban ƙasa ya yabawa marigayin da kishinsa da jajircewa wajen kula da walwala da ci gaban jama’arsa. Ya ce za a ci gaba da tunawa da sarkin bisa jagoranci na nagarta da baiwar jagoranci da Allah ya h**e masa.

Shugaba Tinubu ya mika sakon ta’aziyyarsa ga gwamnatin jihar Zamfara, al’ummar Gusau da kuma iyalan marigayin, tare da addu’ar Allah ya jikan sa, ya sa Aljannah Firdausi ta zama makoma gare shi.

A Shekarun Baya Na Yi Tashen Da Babu Irin Abinda Ban Mallaka Ba A Masana'antar Fim, Amma Yanzu Har Gudun Saka Ni A Fim A...
25/07/2025

A Shekarun Baya Na Yi Tashen Da Babu Irin Abinda Ban Mallaka Ba A Masana'antar Fim, Amma Yanzu Har Gudun Saka Ni A Fim Ake Yi Saboda Ana Kallo Na Da Kuskuren Da Na Yi A Baya, Cewar Ummi Nuhu

Ummi Nuhu ta kara da cewa duk da cewa tana kaunar harkar fim har yanzu, amma koda ta je neman a saka ta a fim, sai a ki saka ta, saboda ana waiwayar kuskuren da ta yi a baya.

Cikin kuka Ummi, ta ce a yanzu ba ta da wata sana'a da ta iya illa harkar fim gashi kuma an daina yi da ita, kuma tana fama da rashin lafiya wanda ya kamata a ce ana saka ta a fim domin ta kula da kanta.

Tsohuwar jarumar dai ta bayyana hakan ne a hirar ta da Hadiza Gabon a shorinta na 'Gabon Talk Shaw', kamar yadda Rariya ta nakalto.

Wani karin abin tausayi a lamarin Ummi Nuhu shine, ta ce har yanzu ba ta taba yin aure ba, duk da cewa shekarunta sun ja.

Yanda jama'ah ke tururuwa domin halartar sallar magrib a masallacin Manzon Allah s. A. W. Dake birnin Madina.Allah karaw...
24/07/2025

Yanda jama'ah ke tururuwa domin halartar sallar magrib a masallacin Manzon Allah s. A. W. Dake birnin Madina.

Allah karawa Annabi Daraja.

Tsohuwar ma’aikaciyar BBC Hausa, Halima Umar Saleh, ta bayyana cewa ta sha fama da tsangwama da kyara yayin da take aiki...
23/07/2025

Tsohuwar ma’aikaciyar BBC Hausa, Halima Umar Saleh, ta bayyana cewa ta sha fama da tsangwama da kyara yayin da take aiki a BBC Hausa.

Halima ta bayyana hakan ne ta cikin wata tattaunawa da ta yi da gidan talabijin na Arewa24.

A cewarta, wani abokin aiki ya taba yi mata barazana har da cewa zai sa a kore ta daga aiki, duk da cewa ya amince tana yin aikinta yadda ya kamata.

Halima ta ce irin waɗannan ƙalubalen da ta fuskanta ne s**a taimaka wajen yanke shawarar barin BBC.

A yayin da tattaunawar ta ci gaba da janyo martani a shafukan sada zumunta, wasu tsofaffin ma’aikatan BBC Hausa ma sun bayyana irin abubuwan da s**a fuskanta a lokacin da suke aiki da kafar.

Mohammed Sani Aliyu ya bayyana cewa shi ma ya bar aikin ne "saboda yadda wurin ya koma muhalli mai cike da matsin lamba da da rashin jin daɗi”, yana mai kira da a gudanar da bincike kan yadda ake tafiyar da ɓangaren gudanarwar sashen Hausa na BBC.

Ita kuwa Fauziyya Kabir Tukur ta ce lokaci ya yi da za a karkata hankali kan halin da ma’aikatan ke ciki, tana mai danganta sauke bidiyon da Arewa24 ta yi da yiwuwar akwai gaskiya a korafin Halima.

Tuni dai wasu daga cikin masu sauraron tashar ta BBC s**a rubutawa shalkwatar tashar dake birnin Landan ƙorafi dangane da batun, tare da neman a gudanar da bincike a kai.

📌 Shin a wurin aikinku kun taɓa fuskantar irin wannan matsin lamba ko tsangwama?

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Duniya INA Labari posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Duniya INA Labari:

Share