Duniya INA Labari

Duniya INA Labari Shafi ne da aka samar da zaiyi kokari na shiga lungu da sako domin kawo maku sahihan Labaran abubuwan da suke faruwa.

Kuma Kofar mu a bude take na tallata maku hajar ku ga sama da mutun 100,000 da muke dasu, masu bibiyar shafin Ankirkiri wanan shafin mai suna DUNIYA INA LABARI saboda inganta harshen hausa da kuma kawo maku
1)Labarai.
2)Ilmantarwa.
3)Nishadantarwa.
4)fadakarwa.

Labari Cikin Hoto: Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) kuma Gwa...
06/06/2026

Labari Cikin Hoto: Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) kuma Gwamnan Jihar Kwara, Malam AbdulRahman AbdulRazaq; Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris; tsohon Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Umar Ganduje, da Ministan Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari, tare da sauran manyan baƙi suna daga cikin fitattun mutanen da s**a halarci sallar Juma’a ta musamman da aka gudanar domin bikin Ranar Dimokiraɗiyya ta bana. An gudanar da wannan zaman addu’a ne a ranar Juma’a, 5 ga Yuni, 2026, a Masallacin Ƙasa da ke Abuja.

Yadda shugaban karamar hukumar Mafara Hon. Yahaya Yari ya haye saman dutse a cikin daji inda 'yan bindiga ke yawo tare d...
05/06/2026

Yadda shugaban karamar hukumar Mafara Hon. Yahaya Yari ya haye saman dutse a cikin daji inda 'yan bindiga ke yawo tare da bayyana cewa ya shirya mutuwa akan al'ummarsa da yake shugabanci.

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kan jama’a da hukumomin tsaro wajen yaƙi da ta’addanciGwamnatin Tarayya ta yi kira ga ...
05/06/2026

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci haɗin kan jama’a da hukumomin tsaro wajen yaƙi da ta’addanci

Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ’yan Nijeriya da kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula da hukumomin tsaro da su ƙarfafa haɗin gwiwa a tsakanin su wajen yaƙi da ta’addanci da sauran nau’o’in tsauraran ra’ayoyi da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja a wajen wani babban taron manema labarai.

Ya ce yaƙi da ta’addanci yana buƙatar haɗin kan ƙasa baki ɗaya ba tare da la’akari da bambance-bambancen siyasa da ƙabila da addini ko yanki ba.

Ministan ya ce: “Gwamnatin Tarayya tana kira ga ’yan ƙasa da kafafen yaɗa labarai da hukumomin tsaro da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci, domin duk wani hari da aka kai wa ɗan Nijeriya ɗaya tamkar an kai shi ne ga dukkan ’yan Nijeriya. Ta’addanci ba ya da ƙabila ko addini ko wata alaƙa da siyasa. Manufar sa ita ce haddasa ɓarna kawai.”

Ya bayyana cewa wannan ne ya haifar da ƙaddamar da gangamin , wanda ke kira ga dukkan ’yan Nijeriya da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci da sauran laifuffuka.

Idris ya kuma tabbatar wa da ’yan Nijeriya cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana ci gaba da ƙoƙarin ganin an ceto dukkan ɗalibai da malamai da aka sace a hare-haren da s**a faru a jihohin Oyo da Borno.

Ya ce: “Ina so in tabbatar wa da dukkan ’yan Nijeriya cewa dawo da kowane yaro da kowane malami da ke hannun masu garkuwa cikin ƙoshin lafiya yana ci gaba da kasancewa babban fifikon gwamnati. Shugaban Ƙasa ya bayyana ƙarara cewa babu wani yaro da ya k**ata ya kasance a tsare, kuma gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa an gurfanar da masu hannu a waɗannan munanan laifuffuka a gaban shari’a.”

Ministan ya bayyana cewa hukumomin tsaro sun ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri da gudanar da sintiri da kuma ayyukan ceto domin kuɓutar da waɗanda aka sace tare da hukunta masu han

Tsarin Kafa ’Yan Sandan Jihohi Ya Kusa Kammaluwa — Fadar Shugaban ƘasaFadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa an samu gagaru...
05/06/2026

Tsarin Kafa ’Yan Sandan Jihohi Ya Kusa Kammaluwa — Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba a tattaunawar kafa rundunar ’yan sandan jihohi, inda ake sa ran gabatar da gyaran kundin tsarin mulki nan ba da jimawa ba domin ba da damar aiwatar da shirin.

Babban Ma’aikacin Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ne ya bayyana hakan bayan wata ganawa da aka yi a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja ranar Alhamis, wadda ta haɗa manyan jami’an gwamnati da shugabannin majalisun dokoki kan batun kafa ’yan sandan jihohi.

Gbajabiamila ya ce an fara nazari da tattaunawa kan yadda za a kafa rundunar tun watanni uku zuwa huɗu da s**a gabata bisa umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kuma an samu ci gaba mai yawa a aikin.

Ya bayyana cewa kafa ’yan sandan jihohi ba abu ne da za a yi cikin gaggawa ba, domin akwai batutuwan kundin tsarin mulki da dokoki da dole ne a tantance su sosai kafin aiwatarwa.

A cewarsa, yanzu hankalin masu ruwa da tsaki ya karkata ne kan yadda za a yi gyaran kundin tsarin mulki, sannan daga baya a samar da dokokin da za su ba da cikakken iko da tsarin gudanar da rundunar.

Ya ƙara da cewa mafi yawan ’yan Najeriya da masu ruwa da tsaki sun amince da bukatar kafa ’yan sandan jihohi, inda muhawarar yanzu ba ta kan ko a kafa su ko a’a ba, sai dai yadda za a samar da ingantaccen tsarin doka da gudanarwa domin su yi aiki yadda ya k**ata.

Gbajabiamila ya ce za a gabatar wa Shugaba Tinubu cikakken rahoto kan sak**akon ganawar domin ci gaba da matakan da s**a dace.

A cewarsa, manufar kafa ’yan sandan jihohi ita ce ƙarfafa tsaron cikin gida, inganta tattara bayanan sirri daga matakin ƙasa da kuma bai wa gwamnatocin jihohi damar magance matsalolin tsaro cikin sauri da inganci.

Shugaba Tinubu ya sha bayyana cewa tsarin ’yan sandan jihohi na daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen fuskantar ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasar nan, tare da ƙara kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ganawar ta samu halartar Mataimakin Shugaban Majalis

DA DUMI-DUMINSA: Kotu Ta Bada Umarnin Gwanjon Kadarorin Sirikin Tsohon Shugaban Kasa Buhari Bisa Taurin BashiDaga Saiful...
04/06/2026

DA DUMI-DUMINSA: Kotu Ta Bada Umarnin Gwanjon Kadarorin Sirikin Tsohon Shugaban Kasa Buhari Bisa Taurin Bashi

Daga Saifullahi Lawal Imam

Babbar Kotun Jihar Kaduna ta bada umarnin yin gwanjon wasu kadarori mallakin tsohon ɗan majalisar tarayya, kuma Tsohon Dan Takarar Gwamnan Jihar Kaduna, kuma Sirikin Tsohon Shugaban Kasa Marigayi Muhammadu Buhari wato Alhaji Mahmood Sani Sha’aban (Danburam Zazzau), sak**akon wata takaddama ta bashi da ta daɗe tana gudana tsakaninsa da fitaccen ɗan kasuwar nan Alhaji Umar Faruk Abdullahi, a ranar Litinin, 1 ga Yuni, 2026.

Kadarorin da kotun ta yi gwanjonsu sun haɗa da fili da gine-ginen da ke G.R.A Zaria, wadanda ke bayan gidansa da yake zaune, dake gaban Makarantar Sakandaren Therbow a Zariya, mai takardar Shaidar Mallaka (C of O) mai lamba KD 3984; da kuma fili da gine-ginen da ke kan Plot No. 3, Churchill Road, GRA Zaria, mai Takardar Shaidar Mallaka mai lamba KD 11226.

Sauran kadarorin sun haɗa da fili da gine-ginen da ke Tulips, mahadar MTD da ke gefen titin Queen Elizabeth, GRA Zaria, mai Takardar Shaidar Mallaka mai lamba KD 15052, da kuma kamfanin Mazari Nails Limited da ke kan babbar hanyar Kaduna zuwa Kano, mai Takardar Shaidar Mallaka mai lamba KD 6246.

Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala gwanjon, Mista Abdullahi Yahaya, SAN,wanda kuma shine lauyan mai kara Umar Faruk Abdullahi,ya ce abin da aka gudanar a ranar shi ne gwanjo da sayar da kadarorin wanda ake bin bashi k**ar yadda hukuncin Babbar Kotun Shari’a ta 1 da ke Zariya ya tanada.

Ya ƙara da cewa kotun ta ƙwace kadarori guda biyar na wanda ake bin bashin, inda huɗu daga cikinsu suke a Zariya, yayin da ɗaya ke Kano.

Idan za a tuna ita wannan shari’ar ta samo asali ne daga wata yarjejeniyar bashi da aka kulla a shekarar 2018 tsakanin Hon. Sani Mahmud Sha’aban (Dan Buram Zazzau) da Alhaji Umar Faruk Abdullahi domin taimaka wa Sha’aban wajen warware wata matsala da ta shafi k**a shi da tsare shi a gidan yari a kasar Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa (U

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Shalkwatar Hukumar 'Great Green Wall' Zuwa Kano Don Inganta AikiGwamnatin Tarayya ta ɗauki...
03/06/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Shalkwatar Hukumar 'Great Green Wall' Zuwa Kano Don Inganta Aiki

Gwamnatin Tarayya ta ɗauki gabarar daidaita ayyukan hukumar yaƙi da kwararar hamada ta kasa, wato National Agency for the Great Green Wall (NAGGW), inda ta mayar da babban ofishinta na gudanar da ayyuka daga birnin tarayya Abuja zuwa jihar Kano.

Ministan Muhalli, Balarabe Abbas Lawal, ne ya bayyana hakan, inda ya bayyana cewa matakin na kunshe ne a karkashin tsarin 'Renewed Hope Agenda’ na Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Manufar hakan ita ce tallafa wa hukumar don ta gudanar da ayyukanta cikin hanzari da nagarta a jihohin da abin ya shafa.

Shirin na 'Great Green Wall' babban yunkuri ne na Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) da ya kunshi kasashe 11, da nufin yaki da kwararar hamada, lalacewar kasa, da kuma radadin sauyin yanayi a yankin Sahel da Sahara.

A nan Najeriya, shirin ya karkata ne a kan jihohi 11 na gaba-gaba da hamada ke barazana musamman ga rayuwarsu, wadanda s**a hada da: Bauchi, Borno, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kebbi, Sokoto, Yobe, Zamfara, da kuma Adamawa.

Ministan ya kara da cewa, babban burin hukumar shi ne shimfida dangar bishiyoyi (Green Wall) mai nisan kilomita 15 a fadi, da kuma tsawon kilomita 1,500 domin kare muhalli, rage radadin sauyin yanayi, samar da wadatar abinci, da kuma rage radadin talauci a karkara.

Tun lokacin da aka kaddamar da shirin a shekarar 2013, kafin daga bisani a mayar da shi cikakkiyar hukuma a 2015, an samu manyan nasarori k**ar haka:

Kafa dangar kariya daga iska da yashi (shelterbelts) fiye da guda 100.

Gina madatsun ruwa na sola da iskar gas guda 159 don samar da ruwan sha.

Daukar matasa guda 600 a matsayin dogaran daji (forest guards).

Samar da gonakin bishiyoyin itatuwa na (orchards and woodlots) guda 240 don bunkasa kudin shiga.

Malam Balarabe Abbas Lawal ya jaddada cewa, wannan sauyi zai magance kalubalen da hukumar ta dade tana fuskanta na gudanar da ayyuka daga ofishin haya a Abuja, wanda ke nesa da ainihin inda ayyuka

Wane Ne Gwaninka A Zaɓen 2027?
03/06/2026

Wane Ne Gwaninka A Zaɓen 2027?

03/06/2026

BIDIYO: Yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dawo Abuja a yau bayan kammala bukukuwan babbar sallah a mahaifarsa, Legas.

Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yada Labarai ga Shugaba Tinubu, Malam Abdulaziz Abdulaziz, Yayi Karin Haske Ka...
01/06/2026

Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yada Labarai ga Shugaba Tinubu, Malam Abdulaziz Abdulaziz, Yayi Karin Haske Kan Daukar Masu Tsaron Daji 1,000 a Jihar Oyo.

Tun jiya da jaridu s**a fara bada labarin aniyar ɗaukar masu tsaron daji (Forest Guards) guda 1,000 a jihar Oyo sak**akon kidnapping da aka yi kwanaki na lura wasu mutanenmu na Arewa a Social Media suna ƙorafi ko shaguɓen cewa "an taɓa ƴan gata". A ganin su wannan abu ne kawai za a yi domin Yarabawa saboda matsalar tsaro ta shafe su. To ba haka ba ne.

A yanzu haka akwai jihohi 10 da aka kafa rundunar Forest Guards da kuma jihohi duk a Arewa. Kuma kowanne an ɗauki mutum kimanin 1,000 ɗin ne.

Jihohin da suke da Forest Guards:
1. Borno
2. Yobe
3. Adamawa
4. Kwara
5. Sokoto
6. Kebbi
7. Niger
8. Plateau
9. Benue

Wanda suke kan hanya
1. Kaduna
2. Edo
3. Kogi
4. Bauchi

Mutanen Gombe waye Kukeso??Pantami ko Jamilu.?? Duk wanda aka fi zaba, Gobe Insha Allah zan wallafa Hotonshi da fatan Na...
31/05/2026

Mutanen Gombe waye Kukeso??

Pantami ko Jamilu.??

Duk wanda aka fi zaba, Gobe Insha Allah zan wallafa Hotonshi da fatan Nasara tare da bayyana cewa Mutanen Gombe shi ne s**a fi so Anma a Shafina.

Wannna Gwanji ne kawai na Shafin Sada Zumunta...

Address

<fg=bff0000f> Zaku Iya Samun Labaran Mu A Kasashen Duniya, Musamman, Kasashen Africa, Nigeria, Niger, Ghana, Chadi. . . .
Abuja
SOKOTO,KANO,KADUNA,ABUJA,KATSINA,LAGOS

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Duniya INA Labari posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Duniya INA Labari:

Share