Rariya Online

Rariya Online Rariya Online shafi ne na watsa Labarai a harshen Hausa, da su ka shafi kowanne fanni na rayuwar Ɗan Adam.

Za ku iya tuntuɓarmu ta waɗannan hanyoyin, domin bada talla:

Lambar Waya/WhatsApp: +2348039411956

Adireshin Email: [email protected]

Wani jigo a tafiyar Pantamiyyah, Comrade Albishir, ya bayyana cewa al’ummar Gombe za su more ingantaccen tsaro da ci gab...
08/06/2026

Wani jigo a tafiyar Pantamiyyah, Comrade Albishir, ya bayyana cewa al’ummar Gombe za su more ingantaccen tsaro da ci gaba idan s**a bai wa Professor Isa Ali Pantami damar jagoranci.

A cewarsa, Pantami mutum ne da ya nuna kwarewa, gaskiya da kishin al’umma, yana mai jaddada cewa dukiya da rayukan Gwambawa za su samu kariya da kwanciyar hankali a karkashin jagorancinsa.

Comrade Albishir ya yi kira ga al’ummar jihar da su yi la’akari da irin gudummawar da Pantami ya bayar a fannoni daban-daban, yana mai cewa idan aka ba shi dama, zai kawo ci gaba mai ɗorewa da inganta rayuwar jama’a a fadin jihar.

YANZU-YANZU: Dalibai 31,711 Sun Amfana da Tallafin Karatu na Sanata Yakubu Lado Dan Marke a KatsinaWasu masu ruwa da tsa...
07/06/2026

YANZU-YANZU: Dalibai 31,711 Sun Amfana da Tallafin Karatu na Sanata Yakubu Lado Dan Marke a Katsina

Wasu masu ruwa da tsaki a harkar ilimi a Jihar Katsina sun yi kira ga attajirai, kamfanoni da masu rike da manyan mukaman gwamnati a jihar da su yi koyi da Sanata Yakubu Lado Dan Marke wajen tallafa wa ilimi da kuma taimaka wa dalibai marasa galihu su cimma burinsu na neman ilimi.

Kiran ya fito ne a wani taron manema labarai da aka gudanar, inda masu jawabin s**a bayyana cewa ilimi shi ne ginshikin ci gaban kowace al’umma, don haka akwai bukatar masu hannu da shuni su kara zuba jari a wannan fanni domin taimakawa matasa.

Sun ce tsadar kudin makaranta, kudin gudanarwa da kuma halin matsin tattalin arziki da ake ciki sun sanya samun ilimi ya zama babban kalubale ga iyalai da dama, musamman masu karamin karfi.

A cewarsu, gidauniyar tallafin karatu ta Sanata Yakubu Lado Dan Marke ta zama wata babbar hanya da ke taimaka wa daliban Jihar Katsina masu karatu a jami’o’i da manyan makarantu daban-daban a fadin Najeriya.

Sun bayyana cewa Yakubu Lado Dan Marke, wanda ya taba zama shugaban karamar hukumar Kankara, dan majalisar wakilai da kuma sanata mai wakiltar shiyyar Katsina ta Kudu, ya kafa gidauniyar ne domin rage wa dalibai radadin matsalolin kudi da ke barazana ga ci gaban karatunsu.

Bayanan da aka gabatar a taron sun nuna cewa tun bayan kafa gidauniyar a shekarar 2023, ta bayar da tallafin karatu ga dalibai masu karatu a makarantu da jami’o’i daban-daban, ciki har da ABU Zaria, BUK Kano, UMYUK Katsina, FUDMA Dutsinma, UDUS Sokoto, FUD Dutse, FCE Katsina, FCE Kano, FCE Zaria, KADPOLY da Yusuf Bala Usman College, Daura.

Tallafin ya shafi masu karatun Diploma, HND, NCE, Digiri na Farko, Digiri na Biyu da Digiri na Uku, tare da wadanda ke karatu a tsarin Full-Time, Part-Time, Distance Learning da kuma Vocational Training.

Masu jawabin sun ce kididdigar da suke da ita ta nuna cewa dalibai 31,711 ne s**a amfana da tallafin karatun gidauniyar tsakanin shekarar 2023 zuwa 2026.

Sun kara da cewa bayanan biyan kudade sun nuna cewa an kashe sama da Naira biliyan 1.2 wajen gudanar da shirin tallafa wa daliban a cikin wannan lokaci.

A cewarsu, wannan gagarumar gudunmawa ta taimaka wa dubban dalibai wajen ci gaba da karatunsu duk da kalubalen tattalin arzikin da ake fuskanta a kasar nan.

Masu taron sun yabawa Sanata Yakubu Lado Dan Marke bisa abin da s**a kira gagarumin aikin alheri da yake yi wajen bunkasa ilimi, tare da bayyana cewa irin wannan tsari na iya taimakawa wajen rage yawan matasan da ke ficewa daga makaranta saboda matsalolin kudi.

Sun kuma yi kira ga attajirai, kamfanoni da sauran masu ruwa da tsaki a Jihar Katsina da su rungumi irin wannan tsari na tallafa wa ilimi domin fadada damar samun ilimi ga matasa da kuma taimakawa wajen gina kyakkyawar makomar jihar da kasa baki daya.

Masu jawabin sun kara da cewa akwai bukatar a samar da karin tallafi ga dalibai, musamman wajen magance matsalolin sufuri da sauran kalubalen da daliban manyan makarantu ke fuskanta a kullum.

Sun ce idan masu hali da kamfanoni s**a rungumi irin wannan tsari, hakan zai taimaka matuka wajen bunkasa ilimi da samar da ingantattun matasa masu amfani ga al’umma da kasa baki daya.

Tsarin Kafa ’Yan Sandan Jihohi Ya Kusa Kammaluwa — Fadar Shugaban ƘasaFadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa an samu gagaru...
07/06/2026

Tsarin Kafa ’Yan Sandan Jihohi Ya Kusa Kammaluwa — Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba a tattaunawar kafa rundunar ’yan sandan jihohi, inda ake sa ran gabatar da gyaran kundin tsarin mulki nan ba da jimawa ba domin ba da damar aiwatar da shirin.

Babban Ma’aikacin Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ne ya bayyana hakan bayan wata ganawa da aka yi a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja ranar Alhamis, wadda ta haɗa manyan jami’an gwamnati da shugabannin majalisun dokoki kan batun kafa ’yan sandan jihohi.

Gbajabiamila ya ce an fara nazari da tattaunawa kan yadda za a kafa rundunar tun watanni uku zuwa huɗu da s**a gabata bisa umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kuma an samu ci gaba mai yawa a aikin.

Ya bayyana cewa kafa ’yan sandan jihohi ba abu ne da za a yi cikin gaggawa ba, domin akwai batutuwan kundin tsarin mulki da dokoki da dole ne a tantance su sosai kafin aiwatarwa.

A cewarsa, yanzu hankalin masu ruwa da tsaki ya karkata ne kan yadda za a yi gyaran kundin tsarin mulki, sannan daga baya a samar da dokokin da za su ba da cikakken iko da tsarin gudanar da rundunar.

Ya ƙara da cewa mafi yawan ’yan Najeriya da masu ruwa da tsaki sun amince da bukatar kafa ’yan sandan jihohi, inda muhawarar yanzu ba ta kan ko a kafa su ko a’a ba, sai dai yadda za a samar da ingantaccen tsarin doka da gudanarwa domin su yi aiki yadda ya kamata.

Gbajabiamila ya ce za a gabatar wa Shugaba Tinubu cikakken rahoto kan sakamakon ganawar domin ci gaba da matakan da s**a dace.

A cewarsa, manufar kafa ’yan sandan jihohi ita ce ƙarfafa tsaron cikin gida, inganta tattara bayanan sirri daga matakin ƙasa da kuma bai wa gwamnatocin jihohi damar magance matsalolin tsaro cikin sauri da inganci.

Shugaba Tinubu ya sha bayyana cewa tsarin ’yan sandan jihohi na daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen fuskantar ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasar nan, tare da ƙara kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ganawar ta samu halartar Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau I. Jibrin; Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu; Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Lateef Fagbemi; da Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Tunji Disu, tare da sauran manyan jami’an gwamnati.

Sarkin Argungu Ya Bukaci Al’umma Su Mallaki Makamai Don Kare Kansu Daga 'Yanbindiga, Ya H**e Su Da Su Tsaya Cikin Doka.M...
05/06/2026

Sarkin Argungu Ya Bukaci Al’umma Su Mallaki Makamai Don Kare Kansu Daga 'Yanbindiga, Ya H**e Su Da Su Tsaya Cikin Doka.

Mai Martaba Sarkin Kabin Argungu, Muhammadu Sama’ila Mera, ya yi kira ga al’ummomin da ke fama da matsalolin tsaro da su yi tunanin mallakar makamai da doka ta amince da su domin kare rayukansu da dukiyoyinsu daga hare-haren ’yanbindiga da sauran masu aikata laifuka.

Sarkin ya bayyana hakan ne a wani taro da ya haɗa hakimai, shugabannin ƙauyuka da na unguwanni a fadarsa da ke Argungu, inda ya ce matsalar rashin tsaro ta kai matakin da ke buƙatar al’umma su ƙara taka rawa wajen kare kansu cikin bin doka, Jaridar Taskar Labarai ta ruwaito.

A cewarsa, bai kamata jama’a su kasance cikin fargaba ba yayin da ake ta kai hare-hare a garuruwansu ko kuma a yi garkuwa da mata da yara ba tare da wata kariya ba. Ya ce al’ummomi za su iya haɗa kuɗaɗensu domin sayen makaman da doka ta halatta, tare da amfani da su wajen kariyar kai idan buƙata ta taso.

Sai dai Sarkin ya jaddada cewa ba ya ƙarfafa karya doka ko ɗaukar fansa a hannu. Ya bayyana cewa manufarsa ita ce al’umma su samu damar kare kansu cikin tsarin doka, ba tare da haifar da rikice-rikice ko ramuwar gayya ba.

Ya kuma yi kira ga sarakuna, malamai da shugabannin al’umma da su ƙara wayar da kan jama’a kan muhimmancin zaman lafiya, haɗin kai da kuma ba jami’an tsaro cikakken goyon baya wajen yaƙi da matsalar rashin tsaro.

Kalaman Sarkin dai na zuwa ne a daidai lokacin da wasu yankuna a Arewacin Nijeriya ke ci gaba da fuskantar hare-haren ’yanbindiga, satar mutane domin neman kuɗin fansa da sauran matsalolin tsaro da s**a jefa al’umma cikin damuwa.

Duk da kiran da ya yi na mallakar makamai cikin tsarin doka, Sarkin ya nanata cewa haɗin gwiwa tsakanin jama’a da hukumomin tsaro shi ne hanya mafi inganci wajen tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro.

Ɗan siyasa kuma mai sharhi kan harkokin siyasa, Alhaji Sani Ahmad Zangina, ya yi zargin cewa wasu daga cikin jam’iyyun a...
05/06/2026

Ɗan siyasa kuma mai sharhi kan harkokin siyasa, Alhaji Sani Ahmad Zangina, ya yi zargin cewa wasu daga cikin jam’iyyun adawa ne ke ɗaukar nauyin ayyukan ta’addanci da rashin tsaro a Najeriya domin ɓata sunan gwamnatin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

Zangina ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce akwai wasu ‘yan adawa da ke amfani da matsalolin tsaro a matsayin makamin siyasa domin rage wa gwamnati farin jini a idon al’umma.

Ya ce, “Wallahi ‘yan jam’iyyar adawa ke ɗaukar nauyin ta’addanci a Najeriya saboda a ɓata gwamnatin Shugaba Tinubu mai adalci,” yana mai kira ga hukumomin tsaro da su binciki duk wanda ake zargi da hannu wajen rura wutar rashin tsaro a ƙasar
Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata hujja ko rahoton hukumomin tsaro da ya tabbatar da zargin da Zangina ya yi kan jam’iyyun adawa. A lokuta daban-daban, jam’iyyun adawa sun sha s**ar gwamnatin tarayya kan yadda take tafiyar da matsalolin tsaro da tattalin arziki a ƙasar.

Zangina ya kuma yabawa gwamnatin Tinubu kan matakan da take ɗauka wajen magance matsalolin tsaro da bunƙasa tattalin arzikin ƙasa, yana mai cewa lokaci ne da ya kamata ‘yan Najeriya su haɗa kai domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

DA DUMI-DUMI: Kungiyar One North Movement Ta Yi Alkawarin Marawa Dr. Jamilu Ishaq Baya A Zaben Gwamnan Gombe Na 2027Shug...
04/06/2026

DA DUMI-DUMI: Kungiyar One North Movement Ta Yi Alkawarin Marawa Dr. Jamilu Ishaq Baya A Zaben Gwamnan Gombe Na 2027

Shugabannin Kungiyar One North Movement, wadda ke fafutukar ganin Shugaba Tinubu ya ci gaba da jagorancin Najeriya, sun kai ziyarar sada zumunci ga ɗan takarar gwamnan Jihar Gombe, Dr. Jamilu Ishaq, inda s**a yi masa alkawarin ba shi cikakken goyon baya a zaɓen gwamna na shekarar 2027.

A yayin ziyarar, Shugaban kungiyar, Abba Mohammed Aliyu, wanda aka fi sani da Abba G, ya bayyana cewa Dr. Jamilu Ishaq mutum ne mai kishin talakawa da ci gaban al’umma. Ya kuma yi ikirarin cewa babu yadda za a kwatanta gudunmawar da wasu ke bayarwa da irin tasirin da Dr. Jamilu ke da shi wajen tallafawa jama’a.

Abba G ya kalubalanci tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Farfesa Isa Ali Pantami, inda ya ce idan an isa a kawo matasa goma daga cikin ’ya’yan talakawa da Pantami ya taimaka musu wajen samun aiki a lokacin da yake rike da mukami.

A nasa jawabin, Dr. Jamilu Ishaq ya nuna godiyarsa ga shugabannin kungiyar bisa wannan ziyara da goyon bayan da s**a nuna masa. Ya kuma yi alkawarin cewa idan Allah Ya ba shi nasarar zama gwamnan Jihar Gombe, zai mayar da hankali wajen inganta rayuwar al’umma tare da bunkasa ayyukan ci gaba a dukkan sassan jihar.

Ya kara da cewa manufarsa ita ce tabbatar da adalci, ci gaba da walwalar al’ummar Gombe ba tare da nuna bambanci ba.

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Shalkwatar Hukumar 'Great Green Wall' Zuwa Kano Don Inganta AikiGwamnatin Tarayya ta ɗauki...
03/06/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Shalkwatar Hukumar 'Great Green Wall' Zuwa Kano Don Inganta Aiki

Gwamnatin Tarayya ta ɗauki gabarar daidaita ayyukan hukumar yaƙi da kwararar hamada ta kasa, wato National Agency for the Great Green Wall (NAGGW), inda ta mayar da babban ofishinta na gudanar da ayyuka daga birnin tarayya Abuja zuwa jihar Kano.

Ministan Muhalli, Balarabe Abbas Lawal, ne ya bayyana hakan, inda ya bayyana cewa matakin na kunshe ne a karkashin tsarin 'Renewed Hope Agenda’ na Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Manufar hakan ita ce tallafa wa hukumar don ta gudanar da ayyukanta cikin hanzari da nagarta a jihohin da abin ya shafa.

Shirin na 'Great Green Wall' babban yunkuri ne na Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) da ya kunshi kasashe 11, da nufin yaki da kwararar hamada, lalacewar kasa, da kuma radadin sauyin yanayi a yankin Sahel da Sahara.

A nan Najeriya, shirin ya karkata ne a kan jihohi 11 na gaba-gaba da hamada ke barazana musamman ga rayuwarsu, wadanda s**a hada da: Bauchi, Borno, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kebbi, Sokoto, Yobe, Zamfara, da kuma Adamawa.

Ministan ya kara da cewa, babban burin hukumar shi ne shimfida dangar bishiyoyi (Green Wall) mai nisan kilomita 15 a fadi, da kuma tsawon kilomita 1,500 domin kare muhalli, rage radadin sauyin yanayi, samar da wadatar abinci, da kuma rage radadin talauci a karkara.

Tun lokacin da aka kaddamar da shirin a shekarar 2013, kafin daga bisani a mayar da shi cikakkiyar hukuma a 2015, an samu manyan nasarori kamar haka:

Kafa dangar kariya daga iska da yashi (shelterbelts) fiye da guda 100.

Gina madatsun ruwa na sola da iskar gas guda 159 don samar da ruwan sha.

Daukar matasa guda 600 a matsayin dogaran daji (forest guards).

Samar da gonakin bishiyoyin itatuwa na (orchards and woodlots) guda 240 don bunkasa kudin shiga.

Malam Balarabe Abbas Lawal ya jaddada cewa, wannan sauyi zai magance kalubalen da hukumar ta dade tana fuskanta na gudanar da ayyuka daga ofishin haya a Abuja, wanda ke nesa da ainihin inda ayyukan suke a Arewa. Komawa Kano, wadda ita ce cibiyar yankunan da ayyukan s**a shafa, zai ba da damar sanya ido, da samar da kyakkyawar alaka tsakanin gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, da al'ummomin yankunansu.

Jihar Kano riga ta saba da irin wadannan ayyuka, domin tana dauke da ofishin tsara shirye-shiryen dashen bishiyoyi (APCU) tun a shekarar 1988, wanda yanzu ba a amfani da shi yadda ya kamata tun bayan kammala shirin Bankin Duniya na dashen bishiyoyi a yankunan fari (Arid Zone Afforestation Programme) a shekarar 1996. Wannan cigaba a yanzu zai cigaba a hukumar ta NAGGW.

Daga karshe, Ministan ya bayyana yakinin cewa wannan mataki na kusanto da hukumomi kusa da inda suke aiki zai kawo sauyi na gaske ga rayuwar miliyoyin 'yan Najeriya da ke zaune a yankunan da kwararar hamada ke addaba.

Dan Gwagwarmaya Alhaji Sani Ahmad Zangina   ya bayyana fushinsa kan jaridar Mikiya da ya zarga da yi masa rashin adalci,...
03/06/2026

Dan Gwagwarmaya Alhaji Sani Ahmad Zangina ya bayyana fushinsa kan jaridar Mikiya da ya zarga da yi masa rashin adalci, inda ya yi gargadin cewa ba zai yafe musu ba duk da cewa, a cewarsa, sun samu afuwa daga DSP Barau Jibril a baya.

Zangina ya bayyana cewa yana girmama tarihin wasu manyan shugabannin Najeriya da s**a haɗa da Ahmadu Bello, Abubakar Tafawa Balewa da Aminu Kano, yana mai cewa irin waɗannan mutane ba kasafai ake samun irinsu ba a ƙasar nan.

Sai dai wakilin jaridar Rariya Online ya nemi Wayar Shugaban Hukumar gudanarwa ta jaridar Mikiya wato, M Inuwa MH ta wayar tarho amma wayar sa a kashe.

Rahotanni da ke fitowa sun nuna cewa akwai damuwa kan lafiya Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai yayin da yake ci gaba...
03/06/2026

Rahotanni da ke fitowa sun nuna cewa akwai damuwa kan lafiya Tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai yayin da yake ci gaba da kasancewa a hannun jami'an ICPC.

A baya ne Iyalensa s**a yi ikirarin cewa an hana likitansa damar ganinsa tare da duba yanayin lafiyarsa, sannan sun kuma zargi jami'an tsaron da hana masa isar da abinci da magunguna kamar yadda doka ta tanada.

Sai dai a baya, ICPC ta musanta wasu rahotannin da s**a yi ikirarin cewa El-Rufai ya fuskanci matsananciyar matsalar lafiya a tsare, tana mai cewa wasu daga cikin bayanan da ke yawo a kafafen sada zumunta ba su da tushe.

Tsohon gwamnan na fuskantar bincike kan zarge-zargen da s**a shafi cin hanci da rashawa da kuma wasu harkokin kuɗi da ake dangantawa da mulkinsa a Kaduna, zarge-zargen da ya sha musantawa. ICPC ta tabbatar da cewa yana hannunta ne bisa umarnin kotu da kuma ci gaba da gudanar da bincike.

BABBAR MAGANA: Babu Kotu Ko Daya da Ta Taba Daure Ni Kan Sata, Amma Sardauna Har Gidan Yari Kan Sata An Kai Shi — Obi Ya...
03/06/2026

BABBAR MAGANA: Babu Kotu Ko Daya da Ta Taba Daure Ni Kan Sata, Amma Sardauna Har Gidan Yari Kan Sata An Kai Shi — Obi Ya Jaddada Aniyarsa Ta Kare Darajar Arewa

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rariya Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share