Rariya Online

Rariya Online Rariya Online shafi ne na watsa Labarai a harshen Hausa, da su ka shafi kowanne fanni na rayuwar Ɗan Adam.
(1)

Za ku iya tuntuɓarmu ta waɗannan hanyoyin, domin bada talla:

Lambar Waya/WhatsApp: +2348039411956

Adireshin Email: [email protected]

DA ƊUMI-ƊUMI: Yan bindiga sun yi wa Askarawan jihar Zamfara kwanton bauna sun kashe mutun 8 daga Askarawan a hanyar Funt...
16/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Yan bindiga sun yi wa Askarawan jihar Zamfara kwanton bauna sun kashe mutun 8 daga Askarawan a hanyar Funtua zuwa Gusau.

DA ƊUMI-ƊUMI: Bayan Umurnin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu kan rage farashin kudin aikin Hajji don sauƙaƙa ma al'umma,...
16/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Bayan Umurnin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu kan rage farashin kudin aikin Hajji don sauƙaƙa ma al'umma, Hukumar alhazan Nijeriya NAHCON ta fara zama da hukumomin jin daɗin alhazai na jihohi kan batun rage kudin aikin hajjin na shekarar 2026

BABBAR MAGANA: Ba Abunda ya Sani Kawai Kullum Daga Jima'i Sai Kuma Zance Yadda Za'a yi,”Budurwar Vini Anna Silva yar Kas...
16/10/2025

BABBAR MAGANA: Ba Abunda ya Sani Kawai Kullum Daga Jima'i Sai Kuma Zance Yadda Za'a yi,”Budurwar Vini Anna Silva yar Kasar Brazil

Budurwar zaƙaƙurin Dan wasan kwallon ƙafan nan na real madridrd, Vinicius Wanda ake kira da Anna Silva ta Bayyana Saurayinta a matsayin wanda bai san komai ba sai jima'i.

A cewar ta Vini kullum cikin tunanin kwanciya da Mace kawai yake yi,shiyasa aka kasa gane tunaninsa a wasu abubuwan. “jima'i ne kawai abunsa ya iya, na taɓa gaya masa cewa ni Ina son yin hira dashi, ina son mu zauna tare mu ci abinci tare mu tashi k**ar saura.

“Ba na son mutumin da zai rika maganar batsa kawai da ni, ka gane? Ba zai iya yin hira ta gari ba, sai dai jima'i, maganar jima'i kawai.” in ji ta.

WATA SABUWA: Sarkin Musulmi Ya Nemi A Kafa Dokar Da Za Ta Daidaita Amfani da Kafofin Sada Zumunta a NajeriyaSarkin Musul...
16/10/2025

WATA SABUWA: Sarkin Musulmi Ya Nemi A Kafa Dokar Da Za Ta Daidaita Amfani da Kafofin Sada Zumunta a Najeriya

Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya bukaci gwamnati ta samar da dokoki da za su daidaita amfani da kafofin sada zumunta a Najeriya, saboda yadda ake ta yawan amfani da su ba bisa ka’ida ba, wanda ke barazana ga zaman lafiya da hadin kan al’umma.

Alhaji Sa’ad ya bayyana wannan matsaya ne a lokacin taron Ulaman Arewa da aka gudanar a Kaduna, inda ya nuna damuwa matuka kan yadda malamai da sauran mutane ke amfani da kafafen sada zumunta wajen yada kalaman batanci da fitina.

Ya ce: “Yanzu kowa na iya tashi da safe ya ɗauki wayarsa ya ci mutuncin wani ba tare da tsoro ko ladabtarwa ba. A wasu ƙasashe, ana da dokoki da ke kula da amfani da kafafen sada zumunta, amma a nan ba haka yake ba. Wannan lamari yana barazana ga zaman lafiya da mutunta juna a ƙasarmu.”

Sarkin Musulmin, wanda ya samu wakilci daga Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli, ya ce lokaci ya yi da za a duba hanyoyin kafa dokoki ko ƙa’idoji da za su hana amfani da kafafen sada zumunta wajen yada rikici, ƙiyayya da rashin mutuntawa.

A nasa jawabin, Sheikh Ahmad Gumi ya nuna cewa bai dace a hana kafafen sada zumunta gaba ɗaya ba, amma ya k**ata a inganta dokokin da ake da su yanzu domin su dace da zamani, yayin da shugaban Majalisar Shari’a ta Najeriya ya yi gargadi kan haɗarin da ke tattare da yada bayanan ƙarya da ɓata suna ta hanyar kafafen sada zumunta.

Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma A Katsina Ya Halarci Zanen Suna da Daurin Aure a Rugar ‘Yanbindiga.Mataimakin Shugaba...
16/10/2025

Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukuma A Katsina Ya Halarci Zanen Suna da Daurin Aure a Rugar ‘Yanbindiga.

Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Faskarin jihar Katsina, Hon. Isyaku Wada, ya shiga wani ƙungurmin daji inda Fulanin daji ke zaune, domin halartar walimar suna da ɗaurin aure da aka gudanar a yankin.

Hakazalika, an bayyana cewar, Hon. Wada ya kuma halarci hidimar gidan Alhaji Buji, wanda aka gudanar a rugarsu da ke cikin dajin Birnin Ƙogo, a ranar Laraba.

An dai bayyana Alhaji Buji a matsayin daya daga cikin manyan jagororin Fulanin daji a ƙasar Faskari, wanda tun kafin kulla sulhu a cewar majiyoyi an shede shi a matsayin wanda ba ya cikin masu aikata ta’addanci.

A yayin ziyarar k**ar yadda majiyoyi s**a shaida wa Jaridar Taskar Labarai, shugaban karamar hukumar da tawagarsa sun ziyarci wasu ƙauyuka da ke cikin tsakiyar daji, waɗanda tsawon shekaru babu wanda ke iya zuwa saboda matsalar tsaro, wadanda s**a haɗa da: Birnin Ƙogo, Bangi, Zuru, Kahid da Unguwar Tsamiya.

Wadannan ziyarorin dai ga dukkan alamu na bayyana cewar sulhun da aka kulla a yankin da 'yanbindiga ya k**a hanyar tabbatuwa, koda yake 'yanmagana na cewar ba a yabon kuturu sai ya girma da yatsunsa.

DA DUMI-DUMI: Wani barawon waya ya sace wayar kwamishinan tsaro na jihar Kaduna Barista Sule Shu'aibu (SAN) a wajen wani...
16/10/2025

DA DUMI-DUMI: Wani barawon waya ya sace wayar kwamishinan tsaro na jihar Kaduna Barista Sule Shu'aibu (SAN) a wajen wani taron harkokin tsaro a Kaduna.

Daga DIMOKURADIYYA

BABBAR MAGANA: Daɗi ya Kashe Wani  Jami’in Kwastam, Yayin da Aka Samu Gawarsa a Dakin Otel Bayan Tarayya da Mata 3 a Kat...
16/10/2025

BABBAR MAGANA: Daɗi ya Kashe Wani Jami’in Kwastam, Yayin da Aka Samu Gawarsa a Dakin Otel Bayan Tarayya da Mata 3 a Katsina

Wani jami’in Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS) mai mukamin Assistant Superintendent of Customs (ASC), mai suna Lawal Tukur, ya rasu a dakin otel da ke cikin birnin Katsina, bayan da ya kwana da wasu mata uku.

Rahoton Zagazola Reports ya bayyana cewa, lamarin ya faru ne a ranar Talata, 15 ga Oktoba, a Murjani Hotel da ke cikin garin Katsina, inda jami’in ya sauka.

Bisa ga rahoton, ma’aikatan otel ɗin ne s**a tarar da gawarsa da safe, kimanin karfe 8:30 na safe, inda s**a sanar da hukumomi nan take.

Majiyoyi sun bayyana cewa, an samu kwandon shara dauke da jarkunan roba na wasu abubuwa Dake nuna maganin gargajiya ne a cikin dakin da aka same shi.

An gano cewa matan da s**a kasance tare da marigayin sun hada da: Khadija Ali, mai shekara 34, daga Dutsin Amare Quarters, Katsina; Aisha Lawal, mai shekara 30, daga Ingawa LGA; da Hafsat Yusuf, mai shekara 22, daga Brigade Quarters, Kano.

Rahotanni sun ce Khadija da Aisha ne s**a kwana tare da jami’in, yayin da Hafsat ta iso daga baya, inda ta kwana a otel ɗin ita ma.

An kai gawar marigayin zuwa Asibitin Gwamnatin Tarayya (FMC) Katsina, inda likitoci s**a tabbatar da rasuwarsa kafin a kai shi dakin ajiye gawa don yin binciken likita (autopsy).

Hukumar Kwastam ta Najeriya ta tabbatar da samun labarin, kuma an fara bincike domin gano hakikanin abin da ya jawo mutuwar jami’in.

15/10/2025

Babu ƙarancin wutar lantarki a Maiduguri, sanadiyyar Tashar Wutar Lantarki ta Gaggawa mai Amfani da Iskar Gas (Maiduguri Emergency Gas Power Plant) da Gwamnatin Tarayya ta gina. Haka kuma, a Jami’ar Maiduguri, Gwamnatin Tarayya ta ƙara gina katafariyar tashar wutar lantarki mai amfani da hasken rana (12MW Hybrid Solar Plant) — wanda hakan ya tabbatar da cewa duk wanda ke jinya a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri ba zai yi fargabar ɗaukewar wuta ba a kowane lokaci.

— Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris

DA DUMI-DUMI: Yanzu haka cikin daren nan anata kone-kone a wasu wuraren kasar K**aru, kan zargin za'a murde nasarar da I...
15/10/2025

DA DUMI-DUMI: Yanzu haka cikin daren nan anata kone-kone a wasu wuraren kasar K**aru, kan zargin za'a murde nasarar da Isah Tchiroma Bakary yayi na lashe zaben kasar.

DARA TA CI GIDA: Hukumar DSS ta K**a Tsoffin Jami’anta 2 da Ake Zargi da Damfara Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta ba...
15/10/2025

DARA TA CI GIDA: Hukumar DSS ta K**a Tsoffin Jami’anta 2 da Ake Zargi da Damfara

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta bayyana k**a wasu tsoffin jami’anta biyu, Barry Donald da Victor Onyedikachi Godwin, bisa zargin aikin bogi da amfani da sunan hukumar domin damfarar ‘yan Najeriya.

A cewar sanarwar da hukumar ta fitar, mutanen biyu an kore su daga aiki tun da farko, amma s**a ci gaba da amfani da sunan DSS wajen yaudarar jama’a da karɓar kuɗi daga gare su.

Hukumar ta ce an k**a su ne bayan dogon bincike, inda yanzu haka suke hannun jami’an tsaro domin ci gaba da gudanar da bincike.

DSS ta gargadi jama’a da su kasance masu lura da duk wanda ke amfani da sunan hukumar wajen neman kuɗi ko yin wasu huldodi, tare da tabbatar da cewa suna kai rahoto ga ofishin DSS mafi kusa idan s**a fuskanci irin wannan lamari.

ZARGIN CIN MUTUNCI A MIDIYA: Gobe Za'a Ci Gaba da Sauraron Ƙarar da Shugaban Dillalai ya Shigar da Sarkin Hausawan Marab...
15/10/2025

ZARGIN CIN MUTUNCI A MIDIYA: Gobe Za'a Ci Gaba da Sauraron Ƙarar da Shugaban Dillalai ya Shigar da Sarkin Hausawan Maraba

Rahotannin dake shigo ma jaridar Rariya Online sun bayyana cewar gobe Alhamis 16 ga watan Oktoba za'a ci gaba da zaman sauraren shari'ar da ake yi tsakanin Shugaban Dillalan Filaye da gidaje na yammacin Jihar Nasarawa, Alhaji Nasiru Abdullahi wanda aka fi sani da Nasiru Soja wanda ya shigar da Sarkin Hausawan Maraba, Alhaji Adamu Usman Mani da jama'ar Fadar sa kan zargin cin mutuncinsa a kafar sada zumunta.

Shari'ar wanda aka zauna a baya sai dai an bayar da Belin mai martaba Sarkin Hausawa kan Naira Miliyan biyar sannan kuma wanda zai karbe shi ya tabbatar yana da gida a karamar hukumar Karu dake Jihar.

Shari'ar dai za'a sake gudanarwa a gobe, inda ake yin ta a babban kotun Majistiri dake karamar hukumar Karu. Gobe za'a sake gurfanar da Sarkin a Kotun domin ci gaba da kare kansa kan zargin cin mutuncin Shugaban Dillalan Filaye da aka yi a yanar gizo.

Ku biyo mu a gobe don ganin yanda zamu kawo muku cikakken yanda zaman kotun zata kaya.

WATA SABUWA: “Dukkan Gwamnonin da S**a Soke Ni a Baya Yanzu Suna Jam'iyyar APC” — WikeMinistan Babban Birnin Tarayya Abu...
15/10/2025

WATA SABUWA: “Dukkan Gwamnonin da S**a Soke Ni a Baya Yanzu Suna Jam'iyyar APC” — Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana cewa sauyin sheka na manyan jiga-jigan jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC mai mulki ya tabbatar da cewa matsayinsa na goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi daidai ne.

Wike ya ce waɗanda s**a taɓa sosa masa rai har s**a yi Allah wadai da yadda yake mara wa Tinubu baya, yanzu duk sun koma cikin jam’iyyar APC.

A cewarsa, wannan lamari ya nuna cewa siyasar Najeriya tana canzawa, kuma mutane sun fara gane gaskiya game da shugabancin Shugaba Tinubu da irin ci gaban da ake samu a ƙasar.

Wike ya ƙara da cewa zai ci gaba da aiki tare da gwamnati domin tabbatar da aiwatar da manufofin ci gaba da ke amfanar al’umma baki ɗaya.

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rariya Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share