Rariya Online

Rariya Online Rariya Online shafi ne na watsa Labarai a harshen Hausa, da su ka shafi kowanne fanni na rayuwar Ɗan Adam.

Za ku iya tuntuɓarmu ta waɗannan hanyoyin, domin bada talla:

Lambar Waya/WhatsApp: +2348039411956

Adireshin Email: [email protected]

Ministan Yaɗa Labarai ya buƙaci shugabannin APC na Neja da su goyi bayan sauye-sauyen TinubuMinistan Yaɗa Labarai da Way...
12/09/2026

Ministan Yaɗa Labarai ya buƙaci shugabannin APC na Neja da su goyi bayan sauye-sauyen Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci shugabannin jam’iyyar APC a Jihar Neja da su mara wa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu baya tare da taimakawa wajen ƙarfafa nasarorin da aka samu a tattalin arziki, tsaro, ababen more rayuwa, ilimi da bunƙasa ƙwarewar ’yan Nijeriya.

Idris ya yi wannan kiran ne ranar Alhamis a Abuja, lokacin da ya karɓi shugabannin APC na ƙananan hukumomi 25 na Jihar Neja, waɗanda s**a kai masa ziyarar nuna goyon baya.

Ya ce: “Dole ne dukkan mu mu haɗa hannu da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu domin ya ƙarfafa nasarorin da muka riga muka samu, tare da ɗora Nijeriya kan ingantaccen turbar tattalin arziki”.

Ministan ya ce Tinubu ya gaji ƙasar cikin mawuyacin yanayin tattalin arziki da tsaro lokacin da ya hau mulki a watan Mayu 2023, yana mai cewa tattalin arzikin ƙasar nan yana fuskantar matsin lamba sosai, yayin da rashin tsaro ya yi matuƙar shafar rayuwa da sana’o’in ’yan Nijeriya.

“Yana da sauƙi a manta da inda muka fito, amma a yau wannan yanayi ya sauya sosai. Yanzu muna da ƙarin damar gudanar da ayyukan ci gaba da ’yan Nijeriya ke gani a sassa daban-daban na ƙasar,” inji Idris.

Ya ce cire tallafin man fetur ya samar da ƙarin kuɗaɗe da gwamnati ke amfani da su wajen saka jari a noma, hanyoyi, kiwon lafiya, ilimi da ci gaban matasa, yayin da sauye-sauyen gwamnati ke taimakawa wajen dawo da amincewar masu zuba jari.

Idris ya kuma ambaci manyan ayyukan ababen more rayuwa, ciki har da Babbar Hanyar Tekun Lagos zuwa Kalaba da Babbar Hanyar Sakkwato zuwa Badagiri, yana mai cewa ana ci gaba da gina hanyoyi a faɗin ƙasar nan.

Dangane da tsaro, ya amince da cewa har yanzu akwai ƙalubale, amma ya ce ƙasar nan tana samun cigaba a hankali wajen dawo da zaman lafiya.

“Shin mun kai inda muke so? A’a. Shin har yanzu muna fuskantar ƙalubale? E. Amma shin muna ganin cigaba a hankali wajen dawo da zaman lafiya a ƙasar nan? E,” inji shi.

Ministan ya kuma ambaci Asusun Ba da Lamunin Ilimi na Nijeriya (NELFUND), yana mai cewa sama da matasa ’yan Nijeriya miliyan ɗaya sun samu damar yin karatun gaba da sakandare ta hanyar shirin.

Ya buƙaci shugabannin na APC da su ci gaba da haɗa kai tare da warware saɓanin da ke tsakanin su ta hanyar tattaunawa, yana mai jaddada muhimmancin mayar da hankali wajen ƙarfafa wa gwamnati gwiwa da kuma ci gaba da ajandar cigaban ta.

“Ya kamata ’yan Nijeriya su yi watsi da duk wani yunƙuri na mayar da mu zuwa wancan zamanin na rashin tabbas,” inji Idris.

Shugaban tawagar kuma Shugaban Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomin APC na Jihar Neja, Hon. Hashimu Izom, ya taya Idris murnar naɗa shi minista tare da yaba masa kan yadda yake wakiltar Jihar Neja a matakin tarayya.

Izom ya yaba wa ministan kan ƙoƙarin sa na ƙarfafa haɗin kan jihar da kuma tallafa wa ayyuka da shirye-shiryen da ke amfanar al’ummar Neja.

Ya ce: “Muna alfahari da kai, ba don kai ne Mohammed Idris Malagi ba, amma saboda kai ɗan asalin Neja ne na haƙiƙa, wanda a duk inda yake yana tsayawa tsayin daka wajen kare Shugaban Ƙasa da wakiltar Jihar Neja har a matakin ƙasa.”

Gwarzo Da Kabo: Fahad Dankabo Ya Fara Sabon Shirin Ƙarfafa Mata Gabanin Zaben 2027Tsohon Dan takarar Majalisar tarayya t...
12/09/2026

Gwarzo Da Kabo: Fahad Dankabo Ya Fara Sabon Shirin Ƙarfafa Mata Gabanin Zaben 2027

Tsohon Dan takarar Majalisar tarayya ta Gwarzo da Kabo a jam'iyyar APC Hon. Fahad Muhammad Dankabo, ya jaddada mubaya’arsa da goyon bayansa ga jam’iyyar All Progressives Congress (APC), tare da tabbatar da aniyarsa ta ci gaba da ayyukan alheri da tallafa wa al’umma.

Fahad Dankabo ya bayyana hakan ne a yayin wani gagarumin taron mata da ya gudana jiya a garin Gwarzo, wanda ya haɗa mata ‘yan akwatu, ‘yan dangwale, ‘yan biyar na mazabu da sauran ƙungiyoyin mata masu goyon bayan tafiyar siyasar gidansa.

A yayin taron, wanda ya gudana cikin zumunci, farin ciki da kwanciyar hankali, Dankabo ya bayyana cewa ayyukan alherin da yake yi wa al’umma ba za su tsaya ba, yana mai cewa akwai ƙarin shirye-shirye na tallafa wa jama’a a nan gaba.

Ya kuma yi wa matan da s**a halarci taron albishir da wani gagarumin shirin ƙarfafa mata (empowerment) da yake shirin aiwatarwa a ƙananan hukumomin Gwarzo da Kabo nan ba da jimawa ba, in Allah ya yarda.

Dankabo ya tabbatar da cewa shirin na daga cikin ƙoƙarinsa na tallafa wa mata, ƙarfafa musu gwiwa da samar da damammaki da za su taimaka wajen inganta rayuwarsu da ta iyalansu.

Taron ya samu halartar mata daga sassa daban-daban na Gwarzo, inda aka gudanar da shi cikin haɗin kai da fahimtar juna. Mahalarta taron sun kammala taron cikin aminci, tare da komawa gidajensu lafiya.

Ƙungiyar Kiristoci ta goyi bayan Tinubu a zaɓen 2027Ƙungiyar "Charismatic Bishops Conference of Nigeria" (CBCN) ta bayya...
10/09/2026

Ƙungiyar Kiristoci ta goyi bayan Tinubu a zaɓen 2027

Ƙungiyar "Charismatic Bishops Conference of Nigeria" (CBCN) ta bayyana goyon bayan ta ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a babban zaɓen 2027.

Shugaban CBCN, Archbishop Prof. Leonard Bature Kawas, shi ne ya bayyana matsayar ƙungiyar a ranar Laraba a Abuja, a lokacin da ake gudanar da babban taron Synod na 2026 na CBCN da ICCABA a Majami'ar Kiristoci ta Ƙasa.

Kawas ya ce ƙungiyar ta yi nazari kan ayyukan gwamnatin Tinubu, tare da bayyana shirin ta na ci gaba da mara wa shugaban ƙasar baya ta hanyar addu’a, bayar da shawarwari da kuma wayar da kai.

Ya ce: “Mun goyi bayan sa a yanzu. Mun goyi bayan sa yau, za mu goyi bayan sa gobe, kuma za mu ci gaba da goya masa baya muddin yana son kasancewa shugaban ƙasar mu.”

Ya ƙara da cewa: “Wannan gida ya amince da shi a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na 2027.”

Da yake jawabi a wajen taron, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci shugabannin addini da su yi amfani da tasirin su wajen ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da kyakkyawar mu’amala tsakanin al’umma gabanin zaɓen 2027.

Ya ce: “Ci gaba da haɗa kan wannan ƙasa na buƙatar fiye da matakan gwamnati. Yana buƙatar jagoranci nagari daga dukkan ɓangarorin al’umma, ciki har da jagorancin addini."

Idris ya yi gargaɗi kan yunƙurin nuna matsalolin tsaron Nijeriya a matsayin yaƙin addini, yana mai cewa ’yan ta’adda da ƙungiyoyin masu aikata laifuka sun kai wa ’yan Nijeriya hare-hare ba tare da la’akari da addinin su ko asalin su ba.

“Kada a bari wani zaɓe ya sa Kirista ya juya wa Musulmi baya, ko Musulmi ya juya wa Kirista baya, ko Arewa ta juya wa Kudu baya, ko wata ƙabila ta juya wa wata baya. Nijeriya tamu ce baki ɗaya,” inji shi.

Da yake wakiltar Shugaban Ƙasa Tinubu, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya yaba wa ma'abota cocin kan gudunmawar su ga zaman lafiya da haɗin kan ƙasa, tare da kira da a samu ƙarin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da shugabannin addini.

Ya ce: “Gwamnati tana buƙatar gudunmawar Kiristoci wajen kyautata ɗabi’a da tarbiyyar al’umma, yayin da Kiristoci suke buƙatar yanayin da zai ba su damar gudanar da ayyukan su da kyau. Fiye da komai, Nijeriya tana buƙatar mu yi aiki tare domin amfanin kowa.”

Wani jigo a siyasar Najeriya, Sani Ahmad Zangina, ya yi kira mai ƙarfi ga gwamnonin jihohi da sauran shugabannin jam’iyy...
05/09/2026

Wani jigo a siyasar Najeriya, Sani Ahmad Zangina, ya yi kira mai ƙarfi ga gwamnonin jihohi da sauran shugabannin jam’iyyar APC da su fito fili su bayyana irin gudunmawar da gwamnatin tarayya ke bai wa jihohinsu, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen sauƙaƙa wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu yaƙin neman zaɓen 2027.

Zangina ya ce lokaci ya yi da gwamnonin APC za su daina ɗaukar dukkan nasarorin da ake samu a jihohinsu a matsayin nasararsu kaɗai, su kuma bayyana wa jama’a yadda gwamnatin tarayya ke taka muhimmiyar rawa wajen samar da kudade da tallafi.

Ya ce ya kamata gwamnonin su yi koyi da Gwamnan Nasarawa, Abdullahi A. Sule (AA Sule), wajen aiwatar da ayyukan alheri da s**a shafi rayuwar jama’a, domin ayyukan da ake gani da idon jama’a su ne mafi ƙarfi wajen neman amincewar masu zaɓe.

A cewar Zangina, kowanne gwamna ya kamata ya rika bayyana wa jama’a irin kudaden da gwamnatin tarayya ke tura wa jiharsa, da kuma irin ayyuka da shirye-shiryen da gwamnatin Tinubu ke tallafawa.

Ya ce idan hakan ya zama al’ada, jama’a za su fahimci irin rawar da Shugaba Tinubu ke takawa wajen tallafa wa jihohi da ƙananan hukumomi.

«“Idan gwamnoni s**a fito s**a bayyana wa jama’a abin da gwamnatin tarayya ke bayarwa, jama’a za su fahimci abin da Tinubu yake yi. A lokacin nan, ba sai Shugaban Ƙasa ya je kowace jiha yana neman ƙuri’a ba; jama’a da kansu za su san wanda ya taimaka musu kuma su zaɓe shi.”»

Zangina ya ƙara da cewa kamfen mafi ƙarfi ba shi ne taron siyasa da cunkoson jama’a ba, illa aikin da jama’a s**a gani kuma s**a amfana da shi.

Ya ce idan gwamnatin Tinubu ta ci gaba da tallafa wa jihohi, yayin da gwamnoni kuma suke bayyana gaskiyar irin wannan tallafi ga jama’a, hakan zai iya sauya yadda masu zaɓe ke kallon gwamnatin tarayya gabanin zaɓen 2027.

Ya kuma yi kira ga shugabannin APC da su mayar da hankali wajen aiki maimakon yawan magana, yana mai cewa tallafa wa marasa ƙarfi, samar da ayyukan more rayuwa da sauƙaƙa wa jama’a halin rayuwa su ne abubuwan da za su fi tasiri a akwatin zaɓe.

A cewarsa, idan jama’a s**a ji daɗin abin da gwamnati ke yi, ba sai an tilasta musu su saurari kamfen ba—ayyukan gwamnati za su iya zama kamfen ɗin kansu.

04/09/2026

*Rasuwar Sarkin Gumel Babban Rashi ce ga Masarautun Gargajiya da Nijeriya* – Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana rasuwar Sarkin Gumel, Mai Martaba Alhaji Dakta Ahmed Muhammad Sani II, CON, a matsayin babban rashi ga Jihar Jigawa da Nijeriya baki ɗaya.

Shettima ya ce marigayi Sarkin ya kasance daga cikin sarakunan gargajiya da s**a sadaukar da shekaru masu yawa wajen tabbatar da zaman lafiya, bunƙasa ilimi, ci gaban al’umma da ƙarfafa haɗin kan ƴan ƙasa.

Mataimakin Shugaban Ƙasan ya bayyana hakan ne ranar Juma’a a Jihar Jigawa, lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayin da Masarautar Gumel, inda ya isar da saƙon ta’aziyyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatin tarayya.

Marigayi Sarkin Gumel na 16 ya rasu a birnin Alkahira na ƙasar Masar a ranar 3 ga Satumba, 2026, bayan shafe kusan shekaru 46 yana mulkin masarautar. Ya hau karagar mulki ne a ranar 16 ga Disamba, 1980.

Mataimakin Shugaban Ƙasan ya ce za a tuna da marigayi Sarkin ne saboda tsawon mulkinsa, tare da hikima, zaman lafiya da kishin al’ummar da ya nuna wajen gudanar da shugabancinsa.

Ya bayyana shi a matsayin uba, mai haɗa kan jama’a, kuma mai bayar da shawarwari, wanda hikimarsa ta taimaka wajen hidimtawa al’umma da ƙasa tsawon kusan rabin ƙarni.

Shettima ya ce duk da cewa mulkin marigayin ya gudana a lokacin da Nijeriya ta fuskanci sauye-sauyen siyasa da zamantakewa da dama, ya ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, ilimi, karatun addinin Musulunci da zaman tare cikin lumana.

Ya ƙara da cewa Shugaba Tinubu yana matuƙar girmama marigayi Sarkin, musamman bisa gudunmawar da ya bayar wajen samar da zaman lafiya da ci gaban al’umma.

Shettima ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin kura-kuransa, Ya karɓi kyawawan ayyukansa, Ya sanya shi cikin Aljannar Firdausi, tare da ba iyalansa, Masarautar Gumel da al’ummar Jihar Jigawa haƙurin jure wannan babban rashi.

Jigo a siyasar Kano, Kuma Tsohon dan takarar majalisar tarayya ta Kabo da Gwarzo Hon. Fahad Dankabo, ya bayyana Gwamnan ...
03/09/2026

Jigo a siyasar Kano, Kuma Tsohon dan takarar majalisar tarayya ta Kabo da Gwarzo Hon. Fahad Dankabo, ya bayyana Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, a matsayin “Father of Future Kano”, tare da bayyana cikakken goyon bayansa ga gwamnan yayin da ake tunkarar babban zaɓen 2027.

Dankabo ya bayyana matsayinsa ne a cikin wani saƙon da ya wallafa, a Shafinsa na Facebook, inda ya yi amfani da kalaman kirari da yabo wajen bayyana salon jagorancin Gwamna Abba da kuma abin da ya kira nasarorin gwamnan wajen tafiyar da jihar.

A cikin saƙon, Dankabo ya kira Abba da “Balaraben Gwamna mai sa duhu ya zama kamar haske”, tare da bayyana shi a matsayin “Balaraben Gwamna mai sirka fire” da kuma wanda ke da “remote” na kashe wuta da ruwan sanyi.

Ya kuma yi amfani da kalmar “Abba-Gida-Gida-Abba”, yana mai cewa sunan Abba ya samu karɓuwa a tsakanin al’ummar jihar Kano.

Dangane da siyasar 2027, Dankabo ya bayyana cewa shi da magoya bayansa za su kasance tare da Gwamna Abba “duk inda ya taka”, yana mai jaddada goyon bayansa ga abin da ya kira Jahadi don “Kano First.”

“Duk inda ka taka muna tare da kai, ko da fire ko ba fire, da ruwan sanyi za mu dafa ganda,” in ji Dankabo.

Ya kuma yi hasashen samun nasarar Abba a zaɓen da ke tafe, inda ya ce da yardar Allah da kuma goyon bayan al’ummar Kano, gwamnan zai ci gaba da jagorantar jihar.

Dankabo ya kammala saƙonsa da kalaman “Falle Biyu Ce Insha Allah”, abin da ke nuni da goyon bayansa ga yiwuwar sake zaɓen Gwamna Abba Kabir Yusuf a 2027.

TIRKASHI: Zamana a gidan Atiku bai amfane ni da komai ba, ni da iyalina duk Tinubu za mu zaɓa — Maitama Lado
02/09/2026

TIRKASHI: Zamana a gidan Atiku bai amfane ni da komai ba, ni da iyalina duk Tinubu za mu zaɓa — Maitama Lado

Shugaba Tinubu ya yi alhinin rasuwar Sarkin ZurmiShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhininsa kan rasuwar Sarkin...
02/09/2026

Shugaba Tinubu ya yi alhinin rasuwar Sarkin Zurmi

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhininsa kan rasuwar Sarkin Zamfaran Zurmi, Mai Martaba Alhaji Bello Sulaiman, wanda ya rasu a ranar Litinin, bayan shafe shekaru biyar a kan karagar mulkin masarautar.

A cikin wata sanarwa da mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Laraba, Shugaba Tinubu ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, Majalisar Masarautar Zurmi, Gwamnatin Jihar Zamfara da al’ummar jihar, da kuma daukacin masarautun Najeriya.

Shugaban ya bayyana marigayin a matsayin basaraken da ake girmamawa, wanda ya jagoranci al’ummarsa cikin hikima, mutunci da jajircewa a wani lokaci mai matuƙar wahala. Ya ce marigayin ya nuna ƙwarewar jagoranci wajen tunkarar matsalolin tsaro da s**a addabi masarautar Zurmi.

Tinubu ya ce Sarkin ya kasance jigo wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da juriya a tsakanin al’ummarsa, yana mai cewa shawarwarinsa masu hikima da ƙoƙarinsa na samar da zaman lafiya sun taimaka ba kawai ga Masarautar Zurmi ba, har ma da Jihar Zamfara da ƙoƙarin dawo da zaman lafiya mai ɗorewa a yankin Arewa maso Yamma.

Shugaban Ƙasar ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta wa marigayin kurakuransa, Ya saka masa da alheri kan ayyukan da ya yi, Ya kuma ba shi Aljannar Firdausi. Ya kuma roƙi Allah Ya bai wa iyalansa da duk waɗanda rasuwar ta shafa haƙuri da ƙarfin zuciyar jure wannan babban rashi.

Wani ɗan asalin ƙaramar hukumar Daura a Jihar Katsina, Sani Ahmad Zangina, ya yi kira ga Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Dikk...
01/09/2026

Wani ɗan asalin ƙaramar hukumar Daura a Jihar Katsina, Sani Ahmad Zangina, ya yi kira ga Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Dikko Umaru Radda, da ya gaggauta sasantawa da Alhaji Ibrahim Masari, yana mai cewa rashin jituwar da ke tsakaninsu na iya yin illa ga muradun Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kuma ci gaban jihar.

Zangina, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana kansa a matsayin ɗan jam’iyyar APC kuma mai biyayya ga Shugaba Tinubu, yana mai cewa ya rubuta sanarwar ne cikin damuwa da kuma fushi kan yadda rikicin siyasa ke gudana a jihar.

Ya ce ba maƙiyin Gwamna Radda ba ne, sai dai yana ganin ya zama wajibi a faɗi gaskiya domin kare muradun jam’iyyar APC, gwamnatin Tinubu da kuma al’ummar Katsina.

A cewar Zangina, tarihi ba zai manta da irin gudunmawar da Ibrahim Masari ya bayar wajen yaɗa siyasar Tinubu a Arewa maso Yamma, musamman a Jihar Katsina, ba.

Ya ce a lokacin da ambaton sunan Bola Ahmed Tinubu a wasu sassan Arewa ke fuskantar ƙalubale, Masari ya tsaya tsayin daka wajen yaɗa saƙon siyasar Tinubu tare da taimakawa wajen ƙarfafa APC a yankin.

Zangina ya ƙara da cewa a matsayinsa na Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Siyasa da Sauran Al’amura, Masari na daga cikin waɗanda ke bayyana irin tallafi, ayyukan ci gaba, naɗe-naɗe da sauran abubuwan da gwamnatin Tinubu ke samarwa al’ummar Arewa.

Sai dai ya yi zargin cewa rashin zaman lafiya a fagen siyasar Katsina na iya rage tasirin waɗannan abubuwa a idon al’umma.

Zangina ya buƙaci Gwamna Radda da ya ajiye duk wani saɓani na siyasa, ya rungumi zaman lafiya domin kare muradin sake zaɓen Shugaba Tinubu a wa’adi na biyu.

Ya ce idan Ibrahim Masari yana da burin zama Gwamnan Katsina, da tuni ya samu damar cimma hakan, saboda a cewarsa, Masari na da magoya baya, tsarin siyasa da kuma karɓuwa a tsakanin al’umma.

Sai dai ya ce Masari ya zaɓi zuwa Abuja domin yi wa Shugaba Tinubu hidima da kuma kare muradun al’ummar Arewa, maimakon neman kujerar gwamna.

Zangina ya bayyana cewa rashin jituwar da ke tsakanin Radda da Masari ba za a kallonta a matsayin rikicin mutane biyu kawai ba, yana mai cewa tana iya shafar burin Shugaba Tinubu na samun wa’adi na biyu da kuma ci gaban Jihar Katsina.

Ya ce yayin da ake fama da rikicin siyasa, al’ummar jihar na ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsaro da tattalin arziki.

Ya ambaci matsalar hare-haren ‘yan bindiga a Kankara, ƙalubalen da manoma ke fuskanta a Batsari, da kuma matsalolin talauci a Daura, Funtua da Malumfashi.

A cewarsa, abin da al’ummar Katsina ke buƙata shi ne ingantaccen shugabanci, tsaro, abinci da mafita ga matsalolin rayuwa, ba rikicin siyasa ba.

Zangina ya gabatar da shawarwari guda uku ga Gwamna Radda.Ya buƙaci Gwamnan da ya kira Ibrahim Masari su zauna su tattauna domin kawo ƙarshen rashin jituwar da ke tsakaninsu, domin maslahar Katsina da kuma muradun Shugaba Tinubu.

Sani ya bayyana Masari a matsayin mutum mai muhimmiyar rawa a harkokin siyasar Shugaba Tinubu, yana mai cewa duk wani rikici da shi na iya yin illa ga dangantakar siyasar Katsina da Abuja.

Ya buƙaci Gwamnan da ya tabbatar da cewa abubuwan da gwamnatin Tinubu ke samarwa Arewa sun haifar da sauyi kai tsaye a rayuwar al’ummar Katsina ta fuskar abinci, tsaro, ayyukan ci gaba da samar da fata.

A ƙarshe, S.A. Zangina ya ce tarihi ba zai fi mayar da hankali kan yawan rikice-rikicen siyasar da aka yi a tsakanin Radda da Masari ba, sai dai kan yadda Jihar Katsina ta kasance wajen samun zaman lafiya, tsaro da ci gaba a ƙarƙashin mulkin Radda.

Ya kuma jaddada cewa irin rawar da Gwamnan zai taka wajen tabbatar da nasarar Shugaba Tinubu a zaɓen 2027 za ta kasance wani ɓangare na abin da tarihi zai yi la’akari da shi.

Zangina ya yi kira ga Gwamna Radda da ya “ajiye takobin rikici”, yana mai cewa Katsina ta fi ƙarfin girman kai, son zuciya da rarrabuwar kai.

“Saboda Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ku ajiye takobin rikici. Katsina ta fi girman kai da son zuciya. Ya isa da girman kai, ya isa da rarrabuwar kai — ku yi aiki domin al’umma,” in ji shi.

Rahoton Zuhair Ali Ibraheem

01/09/2026

YANZU-YANZU: Yadda Dubban Yan Arewa ke rera wakokin kira ga Shugaba Tunubu akan Ya dawo karo na Biyu.

Karkashin kungiyar Tinibu again ta matawalle

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rariya Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share