Daily Nigerian Hausa

Daily Nigerian Hausa A credible Hausa online newspaper with a head office in Nigeria’s capital, Abuja.
(1)

Sabbin Hafsoshin Tsaro sun gana da Ministan tsaro, BadaruMinistan Tsaro na ƙasa, Mohammed Badaru Abubakar ya karɓi sabbi...
28/10/2025

Sabbin Hafsoshin Tsaro sun gana da Ministan tsaro, Badaru

Ministan Tsaro na ƙasa, Mohammed Badaru Abubakar ya karɓi sabbin shugabannin rundunonin tsaro na ƙasa a ofishin sa a yau Talata a Abuja.

Cikin waɗanda s**a halarta akwai Babban Hafsan Tsaro, Laftanar Janar OO Oluyede; Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Mejar Janar W. Shaibu; Babban Hafsan Sojojin Ruwa, Rear Admiral I. Abbas; da Babban Hafsan Sojojin Sama, Air Vice Marshal S. K. Aneke.

Hadimin Ministan Safwan Sani Imam ya ce Ziyarar ta nuna kudirin Ministan na ƙarfafa haɗin kai da haɗin gwiwa tsakanin rundunonin tsaro domin kare martabar ƙasar da tabbatar da tsaron iyakokinta, bisa jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Hamas ta yi mana almundahana wajen miƙa gawarwakin mutanen mu da ta yi garkuwa da su - Isra'ila Isra'il ta tabbatar da c...
28/10/2025

Hamas ta yi mana almundahana wajen miƙa gawarwakin mutanen mu da ta yi garkuwa da su - Isra'ila

Isra'il ta tabbatar da cewa gawar mutumin da Hamas ta miƙa mata a ranar Litinin ba ta cikin gawarwakin da ƙungiyar ta yi garkuwa da su da aka tsara za ta mayar da su.

Har yanzu dai ana neman gawarwaki 13 daga cikin waɗanda Hamas ta yi garkuwa da su, waɗanda ake tunanin za ta miƙa domin cika sharuɗan yarjejeniyar tsagaita wuta da Shugaba Trump ya tsara domin kawo ƙarshen yaƙin Gaza.

Isra'ila ta ce wannan gawar da aka miƙa mata na cikin waɗanda ake tunanin an yi garkuwa da su, s**a mutu a Gaza aka binne su a can.

Hukumomin Isra'ila na dai ganin wannan a matsayin yunƙurin Hamas na karya alƙawarin da aka shiga domin kawo ƙarshen yaƙin.

Yanzu haka dai Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu yana ganawa da jami'an gwamnatinsa domin tattauna matakin da zai ɗauka.

Daga cikin matakan da ake tunanin Isra'ila za ta ɗauka akwai ƙara faɗaɗa wuraren da take da iko da su a Gaza.

Shugabannin ƙasashe 5 mafi daɗewa a mulki a Afirka Teodoro Obiang Nguema Mbasogo, Equatorial Guinea, ya na kan mulki tun...
28/10/2025

Shugabannin ƙasashe 5 mafi daɗewa a mulki a Afirka

Teodoro Obiang Nguema Mbasogo, Equatorial Guinea, ya na kan mulki tun 1979 har zuwa yau.

Paul Biya, Cameroon, ya na kan mulki tun 1982 har zuwa yau, bayan ya sake lashe zaben shugaban kasa.

Denis Sassou Nguesso, Jamhuriyar Congo, ya na kan karagar mulki tun1979 zuwa1992 sannan ya kuma hawa daga 1997 zuwa yau.

Yoweri Museveni, Uganda ya na kan mulki tun 1986 zuwa yau.

Isaias Afwerki, Eritrea tun 1993 da ya ɗare kujerar mulki har yau bai sauka ba.

Tinubu ya aike wa majalisar dattawa buƙatar tabbatar da naɗin sabbin hafsoshin tsaro na ƙasa. Shugaban majalisar dattawa...
28/10/2025

Tinubu ya aike wa majalisar dattawa buƙatar tabbatar da naɗin sabbin hafsoshin tsaro na ƙasa.

Shugaban majalisar dattawa, Goodwill Akpabio ne ya karanta wasikar a zaman majalisar na yau Talata.

Ƴan ƙasashen waje 170 sun aika da neman izinin zama ƴan NajeriyaGwamnatin Tarayya ta fara duba bukatar mutane 170 ƴan ƙa...
28/10/2025

Ƴan ƙasashen waje 170 sun aika da neman izinin zama ƴan Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta fara duba bukatar mutane 170 ƴan ƙasashen waje da su ka gabatar domin neman zama ƴan Najeriya.

Ministan Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin ta hanyar shafin WhatsApp na ma’aikatar, bayan ya jagoranci zaman kwamitin ba da shawara kan batun zama ɗan ƙasa a birnin Abuja.

A cewarsa, kwamitin wanda ya ƙunshi wakilai daga muhimman hukumomin gwamnati k**ar Ma’aikatar Shari’a da Ma’aikatar Harkokin Waje da Hukumar Tsaro ta farin kaya (DSS), da Hukumar Shige da Fice ta Najeriya (NIS), na da alhakin tantancewa da kuma bayar da shawarwarin wadanda s**a cancanta ga Shugaba Bola Tinubu domin amincewa.

Dakta Tunji-Ojo ya sake jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da bin gaskiya da adalci, da bin ƙa’idoji wajen aiwatar da tsarin ba da zama ɗan ƙasa, yana mai cewa zama ɗan Najeriya “girmamawa ce da dole a cancanci samu.”

Ministan ya bayyana cewa kowanne ɗan takara zai fuskanci tsauraran matakai na tantancewa da s**a haɗa da binciken baya, izinin tsaro, da tabbatar da zama da gudunmawarsa ga ci gaban ƙasa.

Bayan kammala wannan matakai, kwamitin na mika shawarwarinsa ga Shugaban Ƙasa domin la’akari da kuma yuwuwar amincewa.

Duk wani mai shirin rikici a zaɓen Anambra zai ɗanɗana kuɗar sa - Ribadu Mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan tsaron kasa...
28/10/2025

Duk wani mai shirin rikici a zaɓen Anambra zai ɗanɗana kuɗar sa - Ribadu

Mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan tsaron kasa, NSA, Nuhu Ribadu, ya yi gargadi cewa duk wani nau’i na tada rikici a lokacin zaben gwamna na Jihar Anambra zai gamu da martani mai karfi da gaggawa daga hukumomin tsaro.

Ribadu ya bayar da wannan gargadi ne a yau Talata a Abuja yayin taron kwamitin haɗin gwiwa na hukumomin tsaro kan harkokin zabe, ICCES, tare da jami’an Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC.

VANGUARD ta rawaito cewa Ribadu, wanda Hassan Yahaya Abdullahi, Daraktan Tsaron Cikin Gida a Ofishin NSA ya wakilta, ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ta tanadi cikakkun matakan tsaro domin tabbatar da zabe cikin aminci da kuma sahihanci a ranar 8 ga Nuwamba.

“Yayin da muke shirin gudanar da zaben gwamna a Jihar Anambra a ranar 8 ga Nuwamba, 2025, mun samar da tsare-tsare masu karfi na tsaro,” in ji Ribadu.

Mutane 170 ƴan ƙasashen waje sun nemi zama ƴan NajeriyaGwamnatin Tarayya ta fara duba  bukatar mutane 170 ƴan ƙasashen w...
28/10/2025

Mutane 170 ƴan ƙasashen waje sun nemi zama ƴan Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta fara duba bukatar mutane 170 ƴan ƙasashen waje da s**a gabatar domin neman zama ƴan Najeriya.

Ministan Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin ta hanyar shafin WhatsApp na ma’aikatar, bayan ya jagoranci zaman kwamitin ba da shawara kan batun zama ɗan ƙasa a birnin Abuja.

A cewarsa, kwamitin wanda ya ƙunshi wakilai daga muhimman hukumomin gwamnati k**ar Ma’aikatar Shari’a da Ma’aikatar Harkokin Waje da Hukumar Tsaro ta farin kaya (DSS), da Hukumar Shige da Fice ta Najeriya (NIS), na da alhakin tantancewa da kuma bayar da shawarwarin wadanda s**a cancanta ga Shugaba Bola Tinubu domin amincewa.

Dakta Tunji-Ojo ya sake jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da bin gaskiya da adalci, da bin ƙa’idoji wajen aiwatar da tsarin ba da zama ɗan ƙasa, yana mai cewa zama ɗan Najeriya “girmamawa ce da dole a cancanci samu.”

Ministan ya bayyana cewa kowanne ɗan takara zai fuskanci tsauraran matakai na tantancewa da s**a haɗa da binciken baya, izinin tsaro, da tabbatar da zama da gudunmawarsa ga ci gaban ƙasa.

Bayan kammala wannan matakai, kwamitin na mika shawarwarinsa ga Shugaban Ƙasa domin la’akari da kuma yuwuwar amincewa.

Gwamnatin Kano ta samar da baburan ban-ruwa ga bishiyoyin kan t**i Gwamnatin jihar Kano ta samar da wasu babura masu zub...
28/10/2025

Gwamnatin Kano ta samar da baburan ban-ruwa ga bishiyoyin kan t**i

Gwamnatin jihar Kano ta samar da wasu babura masu zubar da ruwa don yin ban-ruwa ga bishiyoyin da aka shuka don ƙawata titunan birnin jihar da kuma damar da yanayi da iska lafiyayya a jihar.

Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Dakta Dahir Muhammad Hashim ne ya baiyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce baburan na zamani ne da aka samar da su don kare shi ko kin daga lalacewa.

A cewar Dakta Hashim, ma'aikatar sa na karɓar ƙorafe-ƙorafe na yadda aka fara lalata shukokin da kuma barin dabbobi su na cinye wa, lamarin da ya sanya ya kai ziyarar gani-da-ido don daukar matakin da ya dace.

"Biyo bayan wasu ƙorafe-ƙorafe da al’ummar Jihar Kano s**a gabatar mana, a yau mun kai ziyara gani-da-ido zuwa wasu daga cikin wuraren da muke aikin ƙawata tituna da shuke-shuke, a inda muka duba halin da suke ciki, tare da kafa matakan da s**a dace domin tabbatar da ingancin lafiyarsu," .

Hashim ya tabbatar wa da al'ummar Kano cewa ma'aikatar sa ba za ta bari shuke-shuken su lalace ba.

"Ina tabbatar wa jama’ar Kano cewar ba za mu bari waɗannan shuke-shuken su lalace ba saboda ƙarancin ruwa, kamuwa da cututtuka ko kuma ɓarna daga dabbobi ko mutane ba.

" A halin yanzu, Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya samar da mashinan ban-ruwa na zamani da za'a riƙa amfani dasu wurin bawa bishiyoyin ruwa a faɗin jihar. Haka kuma muna ɗaukar matakan tabbatar da kariya da dorewar wannan shirin mai muhimmanci tare da tabbatar da kyakkyawan yanayi a jihar Kano baki ɗaya.

"Muna kira ga al’ummar Jihar Kano su ci gaba da ba mu haɗin kai ta hanyar bayar da rahotanni idan aka sami matsala, tare da guje wa duk wani abu da zai lalata ko kuma rage darajar wannan aiki na ci gaban muhalli," in ji Kwamishinan.

A karo na goma,  Hisbah ta sake daƙile yunƙurin safarar ƴan mata a Kano Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta sake dakile yunk...
28/10/2025

A karo na goma, Hisbah ta sake daƙile yunƙurin safarar ƴan mata a Kano

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta sake dakile yunkurin safar 'yan mata daga jihar zuwa wasu garuruwan da ƙasashe domin aikata badala da abubuwan da basu dace ba.

Mataimakin Babban Kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano Dakta Mujahideen Aminudeen ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya aiko Daily Nigerian Hausa inda ya ce a wannan karon sun k**a wani mai suna Umar Bala da ya yi yunkurin safarar mata 3.

Acewar Mujahideen, wannan ne karo na 10 da hukumar ke dakile safarar 'yan mata.

"Waɗanda muka k**a, sun kai su Guda 3, na hudun shi ne mai safarar su, mai suna Umar Bala mai shekaru 40"

Malamin ya bayyana cewa matan sun fito ne daga jihohin Yobe da Borno da Katsina.

Hukumar ta bayyana cewa bayan bincike tuni ta mika su zuwa ga hukumar NAPTIP.

Sannan ya yi kira ga iyaye da su rike amanar 'ya'yansu ta hanyar kula dasu ba tare da barinsu suna gararanba ba.

Zaben Anambra: INEC ta yi alkawarin gyara matsalar na'urar sadarwa kafin zabeHukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC)...
28/10/2025

Zaben Anambra: INEC ta yi alkawarin gyara matsalar na'urar sadarwa kafin zabe

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce tana ɗaukar matakan gaggawa domin gyara matsalolin sadarwa da aka samu yayin gwajin tantance masu kada kuri’a a Jihar Anambra kafin babban zaben gwamna da za a gudanar ranar 8 ga Nuwamba, 2025.

Shugaban hukumar, Farfesa Joash Amupitan, SAN, wanda ya bayyana hakan a taron kwamitin haɗin gwiwar tsaro na zaɓe (ICCES) a Abuja, ya tabbatar da cewa INEC ta shirya tsaf don gudanar da zaɓe mai sahihanci da gaskiya.

Amupitan ya ce hukumar za ta tura ma’aikata 24,000 a rumfunan zabe 5,718, yayin da za a tattara sak**ako daga matakai uku — mazabu, kananan hukumomi, da cibiyar tattara sak**ako ta jiha a Awka.

Ya kuma bayyana cewa hukumar ta tsawaita lokacin karɓar katin PVC daga 29 ga Oktoba zuwa 2 ga Nuwamba domin ba kowane mai rajista damar karɓar katinsa.

Shugaban INEC ya yaba da gudunmawar jami’an tsaro da ƙungiyoyin sufuri wajen tabbatar da gudanar da zabe cikin lumana, tare da gargadin cewa duk wani yunkuri na sayen kuri’a zai fuskanci hukunci.

INEC ta ce kimanin masu kada kuri’a miliyan 2.8 ne ake sa ran za su shiga zaben, yayin da shirye-shiryen karshe s**a hada da ƙare yakin neman zabe ranar 6 ga Nuwamba kafin gudanar da zaben ranar 8 ga Nuwamba, 2025.

Zargin badaƙalar kuɗaɗe: An samu tsaiko a fara sauraren shari'ar da gwamnatin Kano ta shigar akan Ganduje Sauraron shari...
27/10/2025

Zargin badaƙalar kuɗaɗe: An samu tsaiko a fara sauraren shari'ar da gwamnatin Kano ta shigar akan Ganduje

Sauraron shari’ar tsohon Gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da wasu mutum bakwai, kan zargin cin hanci da almundahana, ya samu tsaiko a Babbar Kotun Jihar Kano a ranar Litinin.

An dakatar da zaman ne bayan wadanda ake tuhuma s**a kasa mika takardunsu na bukatun su da ake bukata kafin ci gaba da shari’ar.

Gwamnatin Jihar Kano ce ta shigar da karar mai kunshe da tuhuma 11 da s**a hada da cin hanci da hada baki, da karkatar da kudaden gwamnati.

Cikin wadanda ake tuhuma tare da Ganduje akwai matarsa Hafsat da dansa Umar, da wasu kamfanoni da mutane hudu.

Mai shari’a Amina Adamu Aliyu ta umurci dukkan bangarorin da su kammala shigar da takardunsu kafin zaman gaba, sannan ta dage shari’ar zuwa 26 ga Nuwamba, 2025.

Gwamnatin Kano ta ƙaryata labarin ɗaukar malamai 3,917Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sa...
27/10/2025

Gwamnatin Kano ta ƙaryata labarin ɗaukar malamai 3,917

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke cewa tana shirin daukar malamai 3,917 a karkashin shirin “Kano State Government Basic Education Teachers Mapping and Recruitment Plan (2025–2028)”.

A wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin a Kano ta hannun Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi, Balarabe Abdullahi, an bayyana rahoton a matsayin “karya ne kuma mara tushe.”

Abdullahi ya ce ma’aikatar ba ta taba fitar da wata sanarwa ko umarni na hukuma dangane da daukar malamai ba, don haka ya shawarci jama’a su yi watsi da bayanan da ke yawo a kafafen sada zumunta.

"Ma’aikatar na son ta sanar da jama’a cewa ba ta taba yin wata sanarwa ta hukuma kan daukar malamai ba,” in ji shi.

Ya kuma bukaci al’umma da su rika tabbatar da sahihancin duk wata sanarwa daga hanyoyin hukuma kafin su yarda da ita, musamman idan ta shafi batutuwan daukar aiki ko ayyukan gwamnati.

"Ana gargadin jama’a da kada su dogara da bayanan da ba a tabbatar da su ba, musamman a kan batutuwan da s**a shafi daukar malamai,” in ji Abdullahi.

Address

Plot 111B Chinyeaka Ohaa Crescent
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily Nigerian Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily Nigerian Hausa:

Share