Daily Nigerian Hausa

Daily Nigerian Hausa A credible Hausa online newspaper with a head office in Nigeria’s capital, Abuja.
(1)

Kamfanin mai na ƙasa, NNPCL ya bada gudummawar motocin bas masu amfani da iskar gas (CNG) guda 35.
08/07/2025

Kamfanin mai na ƙasa, NNPCL ya bada gudummawar motocin bas masu amfani da iskar gas (CNG) guda 35.

A wani saƙo da ya wallafa a shafin sa na facebook, Aminu Dahiru, hadimi na musamman ga tsohon shugaban jam'iyyar APC na ...
08/07/2025

A wani saƙo da ya wallafa a shafin sa na facebook, Aminu Dahiru, hadimi na musamman ga tsohon shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce:

"Duka Yau duka Gobe shike sa bakin Ba'auzini tawaye.

"Yan APCn Kano Kano Tinubu ya mana rauni sau Daya sau Biyu har sau Uku. Allah ya kai mu ranar ramuwa ranar da zasu gane Ganduje ne rufin Asirinsu."

Ƴan bindiga sun kashe ƴan bijilant 70 a jihar Plateau Aƙalla ƴan bijilant 70 ne aka ruwaito sun mutu a wani rikici da ƴa...
08/07/2025

Ƴan bindiga sun kashe ƴan bijilant 70 a jihar Plateau

Aƙalla ƴan bijilant 70 ne aka ruwaito sun mutu a wani rikici da ƴan bindiga da ya faru a kusa da kauyukan Kukawa da Bunyun da ke karamar hukumar Kanam, Jihar Plateau.

Jaridar Leadership ta rawaito cewa mazauna yankin sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 2 na rana a jiya Litinin, lokacin da daruruwan ƴan bijilant daga karamar hukumar Wase ke kan hanyarsu ta zuwa maboyar ƴan bindiga, amma sai aka yi musu kwanton bauna kuma aka kashe da dama daga cikinsu.

Shugaban kungiyar ƴan bijilant na Kukawa, Aliyu Baffa, ya shaida wa wakilin Leadership cewa “fiye da ’yan bijilant 70 aka kashe” a harin na kwanton bauna, yana mai cewa akwai yiwuwar a sake gano karin gawarwaki a cikin jeji.

A cewar Baffa, harin ya auku ne kusan kilo mita daya daga garin Kukawa, lokacin da 'yan bindigar s**a yi wa 'yan bijilant kwanton bauna yayin da su ke hanyarsu zuwa wata maboya da ke cikin gandun dajin gwamnati da ake kira Madam Forest, wanda ke iyaka da wasu al’ummomin jihohin Bauchi da Taraba.

Rashin gwamnati a hannu ne ya sanya ya sanya ƴan adawa su ka shiga ADC - Radda Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar ...
08/07/2025

Rashin gwamnati a hannu ne ya sanya ya sanya ƴan adawa su ka shiga ADC - Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi watsi da sabuwar haɗakar ƴan hammayar ƙasar, waɗanda ya bayyana da masu haushin rashin gwamnati a hannunsu.

BBC ta rawaito cewa yayin da ya ke jawabi a gidan talbijin na Channels ta cikin shirin Sunrise Daily, Gwamnan ya ce shirin haɗakar ADC ba wani abu ne face tsantsar yaudara.

“Ya k**ata mu faɗa wa kanmu gaskiya, lokacin yaudarar mutanen Najeriya fa ya ƙare'', in ji shi.

A makon da ya gabata ne gamayyar wasu ƴan hamayya daga jam'iyyu daban-daban s**a haɗe kai ƙarƙashin inuwar jam'iyyar ADC da nufin ƙalubalantar gwamnatin APC a 2027.

Ƴan hamayyar sun zargi gwamnatin APC da lalata Najeriya da kuma yunƙurin mayar da ƙasar mai bin tafarkin jam'iyya guda.

To sai dai Gwamnan na Katsina ya ƙalubalanci masu haɗakar da cewa me s**a yi wa Najeriya a lokacin da suke riƙe da madafun iko.

“Wane ne a cikinsu ba ya cikin gwamnatin da ta gabata? Waye a cikinsu bai taɓa shiga gwamnati ba? Muna sane da irin abubuwan da kowanensu ya yi,” in ji Gwamnan na Katsina.

“Mun san irin abubuwan da s**a yi lokacin da suke gwamnati, sai yanzu za su zo suna ɓaɓatu saboda ba sa cikin gwamnati.” a cewar Gwamna Radda.

Gwamnatin Taraiya ta ƙayyade shekarun shiga jami’a zuwa  shekara16Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana cewa Gw...
08/07/2025

Gwamnatin Taraiya ta ƙayyade shekarun shiga jami’a zuwa shekara16

Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta ƙayyade mafi ƙarancin shekaru da ɗalibai za su iya samun gurbin karatu a manyan makarantu zuwa shekara 16.

Alausa ya yi wannan bayani ne a Abuja a yau Talata yayin taron tattaunawa kan manufofi da dokoki da hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandare, JAMB, na 2025 ta shirya.

“Wannan matakin manufofi zai kawo daidaito tsakanin shekarun balaga da kuma girman jiki na shiga jami'a. Mun ƙayyade shekara 16 kuma babu canji daga haka,” in ji shi.

Ya gargadi makarantu da kada su nemi kauce wa wannan doka ta hanyar canza shekarun ɗalibai, yana mai jaddada cewa duk wani yunƙuri na irin haka zai fuskanci hukunci

Mambobin ADC sun shigar da ƙara akan sabbin shugabannin riƙo na jam'iyyar Mambobi uku na jam’iyyar ADC sun shigar da kar...
08/07/2025

Mambobin ADC sun shigar da ƙara akan sabbin shugabannin riƙo na jam'iyyar

Mambobi uku na jam’iyyar ADC sun shigar da kara a gaban kotun tarayya da ke Abuja, suna kalubalantar shugabancin riƙon ƙwarya na jam’iyyar wanda tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, ke jagoranta.

A ranar 2 ga Yuni ne dai ƴan adawa su ka bayyana jam’iyyar ADC a matsayin wacce za su yi amfani da ita wajen hada kuri’u domin kau da Shugaba Bola Tinubu daga kan mulki a zaben 2027.

Ralph Nwosu, tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, ya ce shugabannin jam’iyyar a karkashin jagorancinsa sun yanke shawarar yin murabus tare da goyon bayan sabon shugabancin rikon kwarya.

Sabon shugabancin ya haɗa da David Mark da Rauf Aregbesola, tsohon gwamnan jihar Osun, a matsayin shugaban riko na kasa da kuma sakataren riko, sai kuma Bolaji Abdullahi, tsohon ministan wasanni, da aka nada shi a matsayin kakakin jam’iyyar.

Sai dai a cikin ƙarar da su ka shigar, mai lamba FHC/ABJ/CS/1328/2025 a ranar 4 ga Yuli, wadanda s**a shigar da karar — Adeyemi Emmanuel, Ayodeji Victor Tolu, da Haruna Ismaila — suna neman kotu ta tantance sahihancin shugabancin riƙon na ADC.

Sun bayyana cewa Ralph Nwosu ba shi da hurumin kiran zaman kwamitin ƙoli na ƙasa (NWC), ko kwamitin zartarwa na kasa (NEC) na jam'iyyar, ko wani zama, tun da wa’adinsa a matsayin kakakin ta na ƙasa ya ƙare.

Masu ƙarar sun kuma bayyana cewa shugabannin riko “ba za su iya ba kuma bai k**ata su kasance a matsayin shugabanni ba,” suna mai cewa an naɗa su ne ta hanyar wani taro da tsohon shugaban jam’iyyar ya shirya ba bisa ka’ida ba.

Wasu majiyoyi na kusa sun baiyana cewa Victor Osimhen ya shaidawa Napoli cewa ba zai ci gaba da taka leda a nan ba, illa...
07/07/2025

Wasu majiyoyi na kusa sun baiyana cewa Victor Osimhen ya shaidawa Napoli cewa ba zai ci gaba da taka leda a nan ba, illa iyaka zai ci gaba da zama a Galatasaray, inda ya kammala kakar da ta gabata a can a matsayin aro.

Da ya ke jawabi a taron kasashen da s**a shiga tsarin BRICS, a birnin  Rio de Janeiro na Brazil, Tinubu ya bukaci a kara...
07/07/2025

Da ya ke jawabi a taron kasashen da s**a shiga tsarin BRICS, a birnin Rio de Janeiro na Brazil, Tinubu ya bukaci a kara zuba kudade a fannin kiwon lafiya a duniya.

CNG: Gwamnatin Kaduna ta fara ɗaukar ma’aikata da ɗalibai kyauta a motoci masu amfani da gasShirin Tallafin Sufuri na Ka...
07/07/2025

CNG: Gwamnatin Kaduna ta fara ɗaukar ma’aikata da ɗalibai kyauta a motoci masu amfani da gas

Shirin Tallafin Sufuri na Kaduna (KSTS) ya sanar da fara ɗaukar ma’aikatan gwamnati, tsofaffin ma’aikata da ɗalibai kyauta a motoci bas masu amfani da iskar gas.

Daraktan Hukumar Kula da Shirye-shiryen Gwamnati ta Jihar Kaduna (KADSTRA), Inuwa Ibrahim, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a jiya Lahadi, inda ya ce za a fara wannan sufuri daga yau Litinin, 7 ga wata.

Ya bayyana cewa masu cin gajiyar shirin za su samu damar shiga motocin kyauta na tsawon watanni shida na farko.

A tuna cewa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ne ya kaddamar da sabbin motoci 100 masu amfani da iskar gas (CNG) a filin Murtala Mohammed Square yayin ziyarar aiki da ya kai jihar a ranar 19 ga watan Yuni.

Ibrahim ya bayyana cewa ɗaliban makarantun gwamnati da masu zaman kansu – daga matakin firamare har zuwa jami'a – za su amfana da wannan shiri.

Ya ƙara da cewa daga baya, za a fara biyan kuɗin motar akan ragin kashi 60% ga al’umma baki ɗaya.

Bayan shafe shekaru 40 a kan mulki, shugaban Uganda mai shekaru 80, Museveni zai sake tsayawa takara Jam'iyyar NRM mai m...
07/07/2025

Bayan shafe shekaru 40 a kan mulki, shugaban Uganda mai shekaru 80, Museveni zai sake tsayawa takara

Jam'iyyar NRM mai mulki a Uganda ta ayyana shugaban ƙasar, Yoweri Museveni a matsayin wanda zai yi mata takara a zaɓe mai zuwa.

Matakin zai bai wa shugaban ƙasar - wanda ya fi kowa jimawa kan mulkin ƙasar - damar tsawaita kusan shekara 40 da ya shafe yana jagorantar ƙasar.

A jawabin amincewa da takarar da ya yi, Mista Museveni ya ce idan ya yi nasara a zaɓen zai samu damar cimma muradinsa na mayar da ƙasar ''cikin jerin ƙasashen masu masu tasowa''.

Masu s**ar shugaban, sun zarge shi da mulkin k**a karya tun bayan da ya ƙwace mulkin ƙasar a matsayin jagoran ƴantawaye a 1986.

Tun daga lokacin ne ya riƙa lashe duka zaɓukan ƙasar da aka gudanar, yayin da aka yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar kwaskwarima har sau biyu, domin cire ka'idar shekaru da wa'adi domin ba shi damar ci gaba da zama a kan karagar mulki.

BBC

An saki matashi ɗan Birtaniya da aka ɗaure bisa kwanciya da ƴar shekara 17 a Dubai Wani matashi ɗan Birtaniya da aka ɗau...
07/07/2025

An saki matashi ɗan Birtaniya da aka ɗaure bisa kwanciya da ƴar shekara 17 a Dubai

Wani matashi ɗan Birtaniya da aka ɗaure a Dubai saboda yin jima’i da wata yarinya ƴar shekara 17 ya shaƙi iskar ƴanci kuma tuni yabya koma ƙasar sa ta gado.

An yanke wa Marcus Fakana, wanda yanzu yana da shekaru 19, hukuncin shekara ɗaya a gidan yari a watan Disambar 2024, bayan tarawa da yarinyar, wacce ita ma ƴar Birtaniya ce, yayin da su ke hutu a Ƙasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), wacce ta hana yin jima'i ga ƴan ƙasa da shekara 18.

Uwar yarinyar ce ta kai ƙarar Fakana ga hukumomi a UAE bayan ta ga saƙonnin da s**a tura wa juna ta waya bayan ta koma Birtaniya.

Fakana, wanda ya fito daga Tottenham a arewacin birnin London, ya samu afuwar masarauta daga Mai mulkin Dubai, Sheikh Mohammed bin Rashid Al Maktoum, k**ar yadda ƙungiyar “Detained in Dubai” ta bayyana.

Radha Stirling daga ƙungiyar, wadda ke samun magana da mahaifan Fakana, ta shaida wa BBC Newsbeat cewa: “Yana cikin matuƙar farin ciki. Abu ne mai wuya sosai a sako mutum kwatsam bayan watanni shida a gidan yari.

“Ga shi matashi kuma yaro ne fa a idanu na... Da wuya mutane su fahimci tsawon lokacin da ake buƙata don murmurewa daga irin wannan hali.

“Tabbas yana cikin tsananin fargaba, iyalinsa ma haka. Amma idan aka ce maka ‘sayi tikitin jirgi’, nan da nan jin daɗi sai ya bayyana. Mahaifan sa ma suna cikin farin ciki ƙwarai da gaske da dawowarsa da wuri," in ji Stirling.

Asibitin Best Choice zai fara tiyatar manyan cututtuka akan ragin farashi na kashi 50 Asibitin Kwararru na Best Choice y...
07/07/2025

Asibitin Best Choice zai fara tiyatar manyan cututtuka akan ragin farashi na kashi 50

Asibitin Kwararru na Best Choice ya sake bijiro da wasu ayyukan farantawa al'umma bayan bude fayil kyauta da rage kaso 50% cikin ayyukansu da s**a fara a satin da ya gabata.

Yanzu haka asibitin ya sake tanadar kwararrun likitoci masu yin wadannan Tiyatar

( Urology) Aikin Mafitsara

(Hynea) Ƙabar ciki

(Orthopaedic) Aikin ƙashi,

(ENT) Aikin Hanci , Makogaro da Kunne

(Dental) Haƙori

(Fibroid) Ƙarin mahaifa,

Asibitin ya zakulo zakakuran likitoci domin gudanar da wannan ayyukan daga yau Litinin 8, ga watan Yuli 2025, ga duk masu bukatar wannan ayyukan, akan farashin kaso 50% cikin 100 shima za a biya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanar da shugaban asibitin Alh Auwal Muhammad Lawal ya bayyanawa jaridar Alfijir Labarai a safiyar Litinin.

Lawal yace sun yanke wannan hukuncin ne sak**akon buƙatar da al'umma suke da ita a wannan bangarorin ga kuma yawan da mutane s**a yiwa gwamnati shi yasa hukumar gudanarwar Asibitin Kwararru na Best Choice itama taga da cewar bada tata gudummawar domin kara karfafar gwamnati a wannan fannin.

Ya kuma bayyana jin dadinsa ganin yadda al'umma suke ta cin gajiyar bude fiyil kyauta da rage kaso 50% ganin likita tare da manya da kananan ayyukan asibitin da yayi a satin da ya gabata.

Dukkannin waɗannan ayyuka za a fara gudanar da sune a yau Litinin, don haka ga masu irin wadannan matsaloli za su iya zuwa domin a tantancesu.

Address

Plot 111B Chinyeaka Ohaa Crescent
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily Nigerian Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily Nigerian Hausa:

Share