Daily Nigerian Hausa

Daily Nigerian Hausa A credible Hausa online newspaper with a head office in Nigeria’s capital, Abuja.
(2)

Mai horas da Manchester United ya ce ko Fafaroma bai isa ya sanya ta canja salon wasan shi ba. Ruben Amorim na shan s**a...
20/09/2025

Mai horas da Manchester United ya ce ko Fafaroma bai isa ya sanya ta canja salon wasan shi ba.

Ruben Amorim na shan s**a akan salon wasan shi, wanda ya saɓa da al'adar salon taka ledar ƙungiyar tun tale-tale.

Taliban sun saki ma'aurata ƴan Birtaniya, Peter da Barbie Reynolds, bayan sun shafe fiye da watanni bakwai a tsare a han...
20/09/2025

Taliban sun saki ma'aurata ƴan Birtaniya, Peter da Barbie Reynolds, bayan sun shafe fiye da watanni bakwai a tsare a hannun su.

Peter mai shekaru 80 da kuma Barbie mai shekaru 75, waɗanda s**a shafe shekaru 18 suna zaune a Afghanistan suna tafiyar da cibiyar ilimi a Bamiyan, an k**a su bisa wasu tuhume-tuhume da ba a bayyana ba.

Ƴan uwansu sun zargi cewa an azabtar da su yayin tsarewar, wanda Taliban ta musanta.

Jami’an Birtaniya sun yi maraba da sakin nasu, suna cewa Birtaniya ta yi aiki tukuru kan lamarin tare da muhimmiyar goyon baya daga Qatar.

An mika ma’auratan ga wakilin Birtaniya da ke Kabul. Sakin nasu yana ɗaya daga cikin matakan Taliban na neman samun karɓuwa a duniya duk da damuwar da ake da ita game da tsarin mulkin ta.

Tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan ya faɗi haka ne a wajen taron tattaunawa na 2025 da Gidauniyar Goodluck Jo...
20/09/2025

Tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan ya faɗi haka ne a wajen taron tattaunawa na 2025 da Gidauniyar Goodluck Jonathan (GJF) ta gudanar a Accra, Ghana.

Ya ce idan har ba a ɗauki matakin gaggawa na maguɗin zaɓe ba, to dimokuraɗiyya na hanyar durkushewa a Afirka.

Ƙungiyar MPD na gudanar da duba marasa lafiya kyauta a Kano Ƙungiyar Musulmai mau zuwa Da'awa, 'Muslim Professionals in ...
20/09/2025

Ƙungiyar MPD na gudanar da duba marasa lafiya kyauta a Kano

Ƙungiyar Musulmai mau zuwa Da'awa, 'Muslim Professionals in Da'awa' ta shirya gangamin duba marasa lafiya da ba su magani kyauta.

An shirya wannan gagarimin aikin a yau Asabar, 20/09/2025 a Masallacin Juma'a na garin Gundutse, Karfi 'Yan Masara, a titin Zaria.

Haka kuma za a tantance masu larurar ido, wadanda za a sanar da lokacin da za a yi musu aiki kyauta nan gaba.

An fara wannan aiki da safe a kuma kammala da la'asar.

Allah ya ba da ikon zuwa. Amin.

Sanarwa: Nasiru Yusuf Ibrahim,
PRO, Muslim Professionals in Da'awa,
Kano State Chapter.

20/09/2025

BIDIYO: Ziyarar shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ga iyalin marigayi shugaba Muhammadu Buhari a Kaduna.

Shugaba Tinubu ya je Kaduna ne a jiya Juma'a domin halartar ɗaurin auren ɗan gidan tsohon gwamnan Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari.

A yayin ziyarar, shugaba Tinubu ya jaddada cewa Nijeriya ba za ta taɓa mantawa da Buhari ba, musamman a wajen mulkin sa da kokarin da na son ci gaban ƙasar.

Ya ce Buhari ya tafi, amma ruhin sa na son ƙasa da kyawawan halaye na nan tare da ƴan ƙasar, kuma za a ci gaba da tuna shi a matsayin shugaba na gari abin koyi.

📸 NTA

Ƴansanda sun hallaka ƙasurguman masu garkuwa da mutane su uku a Abuja Rundunar ‘Yan Sandan Babban Birnin Tarayya (FCT) t...
20/09/2025

Ƴansanda sun hallaka ƙasurguman masu garkuwa da mutane su uku a Abuja

Rundunar ‘Yan Sandan Babban Birnin Tarayya (FCT) ta kashe wasu shugabannin gungun masu garkuwa da mutane uku a wani musayar wuta, inda ta ceto wasu da s**a shiga hannun ‘yan ta’addan.

Kwamishinan Yansanda na FCT, CP Ajao Adewale ne ya bayyana hakan yayin da ya ke zantawa da manema labarai a jiya Juma’a a shelkwatar rundunar.

Adewale ya bayyana wadannan ayyuka a matsayin shaida na jajircewar ‘yansanda, kwakkwaran hadin kai da sauran hukumomin tsaro da kuma goyon bayan al’umma.

Ya ce jami’an rundunar sun kai farmaki maboyar ‘yan bindigar a dajin Zinda, kusa da Gidajen Sojojin Najeriya na Kurudu, a ranar 18 ga Satumba, inda s**a gwabza musayar wuta da su.

Ya ce an kashe Shugaban gungun, Abdullahi Umar (wanda aka fi sani da Duna), da mukarrabansa Buba Ahmadi (wanda ake kira Killer) da Habi Sule (Mai-Kudi) a fafatawar.

Abubuwan da aka kwato sun hada da bindigogi biyu kirar AK-49, gidan saka harsasai guda bakwai, katunan ATM, wayoyin salula, kayan tsafi da kuma kudi har naira 10,000.

Bincike ya nuna cewa gungun na da hannu a garkuwa da mutane da dama a yankunan Guzape, Karu, Kurudu da wasu sassan jihar Nasarawa.

Har ila yau, farmakin ya hana su aiwatar da wani yunkuri na sace wani mazaunin unguwar Federal Housing Estate da ke Karu

Ba za mu rufe kantinan mu na Najeriya ba, muna wasu sauye-sauye ne – ShopRiteKamfanin Retail Supermarkets Nigeria Limite...
19/09/2025

Ba za mu rufe kantinan mu na Najeriya ba, muna wasu sauye-sauye ne – ShopRite

Kamfanin Retail Supermarkets Nigeria Limited (RSNL), mamallakin ShopRite a Najeriya, ya tabbatar da cewa zai ci gaba da gudanar da kasuwanci a ƙasar, duk da jita-jitar da ke yawo cewa zai iya rufewa.

Rahoton Daily Trust ya nuna yadda shagunan s**a fara yin fanko, abin da ya sa ake ganin suna dab da fita daga kasuwa.

Sai dai kamfanin, wanda sabbin masu zuba jari s**a karfafa, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa yana aiwatar da sabon tsarin kasuwanci domin dacewa da halin tattalin arzikin Najeriya.

Sanarwar ta ce: “Tsarin kasuwancin da muka gada lokacin sayen kamfanin ya dogara ne da manyan shaguna, shigo da kaya daga ƙasashen waje, da kuma tsadar kula da harkoki. Amma wannan tsarin bai dace da halin tattalin arzikin Najeriya na yanzu ba, inda ake fama da sauyin kudin canji, tashin farashin kaya da ƙarancin kuɗi.”

Kamfanin ya bayyana cewa sabon tsarin zai rage dogaro da shigo da kaya daga waje, inda ya ce sama da kashi 80 cikin 100 na kayayyakin da ake sayarwa yanzu daga cikin gida ake samo su.

Haka kuma ya ce wannan sabon tsarin zai taimaka wajen daidaita harkoki da kuma sake farfado da kasuwancin domin ci gaba a dogon lokaci.

Shugabar dabarun kasuwancin kamfanin, Bunmi Adeleye, ta bayyana wannan mataki a matsayin sabon ginin da zai maida ShopRite ya zama na cikin gida sosai.

Rikicin ƙarin kuɗin makaranta: Prime College za ta maka gwamnatin Kano a kotu kan umarnin rufe makarantarMakaranta mai z...
19/09/2025

Rikicin ƙarin kuɗin makaranta: Prime College za ta maka gwamnatin Kano a kotu kan umarnin rufe makarantar

Makaranta mai zaman kan ta, Prime College Kano ta bayyana ƙin amincewarta kan matakin da Hukumar Kula da Makarantun Masu Zaman Kansu (PVIB), na ƙoƙarin rufe makarantar sak**akon sabani kan karin kuɗin makaranta.

A cikin wata sanarwa da lauyoyin makarantar, ƙarƙashin Aliant Qais Conrad Laureate su ka fitar a yau Juma’a, makarantar ta ce dole ne ta bayyana matsayinta bayan da aka kai mata umarnin kotu daga Wata Kotun Majistare a Kano, wacce ta umarrci ta janye karin kuɗin makarantar na shekarar karatu ta 2025/26.

A watan Yuli 2025, Prime College ta sanar da karin kuɗin makaranta na shekarar karatu mai zuwa, tana mai cewa hauhawar farashi da buƙatar kiyaye ingancin koyarwa da gine-gine ne s**a sa hakan.

Hukumar makarantar ta bayyana cewa, sun ba da sassaucin biyan kuɗi ga iyaye, tare da tabbatar da cewa babu ɗalibin da za a hana karatu saboda kasa biyan kuɗin makaranta

A cewar makarantar, fiye da kashi 94% na iyaye sun biya sabon farashin, amma ƙasa da iyaye 20 ne s**a ƙi, inda su ka kai ƙara ga PVIB don ta shiga tsakani.

Sanarwar ta ce Shugaban hukumar ta PVIB, Malam Baba Abubakar Umar, ya kai ziyara makarantar tare da su waɗannan iyaye da su ka yi tutsu, inda ya kafa wani kwamitin gaggawa na iyaye daga cikin mambobin PTA da ya ƙunshi iyaye 8 da malamai 5.

Sanarwar ta kara da cewa kwamitin ya kada ƙuri'a a goyon bayan karin kuɗin, amma daga bisani PVIB ta ce zaman bai yi daidai ba, sannan ta bayar da umarnin a gaggauta janye karin kuɗin.

Hukumar makarantar ta yi zargin cewa ƙoƙarin tuntubar shugabannin PVIB ya gamu da "cin mutunci da kuma kunyatr wasu a bainar jama’a."

A ranar Laraba, 17 ga Satumba, makarantar ta samu umarnin kotu daga wata Kotun Majistare a Kano, wanda ke hana ta aiwatar da sabon karin kuɗin da kuma dakatar da ayyukan makarantar.

Prime College ta ce tana nazarin daukar matakin doka domin samun adalci a kotu, inda ta sake jaddada cewa tana aiki bisa ka’ida, tana mai gargadi cewa dakatar da ilimin yaran da ba su da laifi zalunci ne.

“Bai dace ba a dakatar da karatun yaran da ba su da laifi, ko da na rana guda ne — b***e na makonni — ba tare da sauraron ɓangarenmu na magana ba,” sanarwar ta ƙara da cewa.

Gwamnatin Kano ta rufe wasu makarantun masu zaman kansuHukumar kula da makarantu masu zaman kansu da na sa kai ta Jihar ...
19/09/2025

Gwamnatin Kano ta rufe wasu makarantun masu zaman kansu

Hukumar kula da makarantu masu zaman kansu da na sa kai ta Jihar Kano (KSPVIB) ta dauki matakin rufe wasu makarantu guda takwas da ke aiki a fadin jihar, bisa dalilai na karya dokoki da kuma sabawa ƙa’idojin gudanarwar hukumar.

A yayinda yake ganawa da manema labarai, Shugaban hukumar Kwamared Baba Umar ya ce rufe makarantun ya zama wajibi saboda karya dokokin kara kuɗin makaranta da rashin yin takardun na izinin gudanarwa.

Wadannan makarantu sun hada da:

1. Prime College Kano – Alu Avenue, Kano

2. Darul Ulum – Hotoro (Ahmad Musa Road)

3. Gwani Dan Zarga College – (Kofar Waika)

4. Awwal Academy – Rimi (Sumaila)

5. Dano Memorial College – (Sumaila)

6. Unity Academy – Wudil

7. Nurul Islam School

8. As-Saif College.

A makon da ya gabata ne shugaban hukumar Baba Umar ya bada wa’adin mako biyu a kai korafin duk wata makaranta mai zaman kanta da ta kara kuɗin makaranta,Inda yace mutane sun bada hadin mai kuma su sun dauki matakin da ya dace na rufe irin wadannan makarantu tare da gurfanar da su gaban kotu.

Shugaban yace a bisa umarnin Kotu,an dakatar da ayyuka a wadannan makarantun har sai abinda alkali ya yanke hukunci akai.

Yace wasu sun ƙara kuɗin makaranta ba tare da amincewar gwamnati ba.

Baba Umar ya kuma ce sun gano matsalar tsaro da rashin isasshen tsari a cikin gine-ginen wasu daga cikin makarantun.

Sai kuma rashin ingantattun kayan aiki da guraben koyarwa da ya dace da ƙa’idar karatun zamani.

Hukumar ta bayyana cewa wannan mataki ya zama dole ne domin tabbatar da cewa yara na samun ilimi mai inganci, tare da kare iyaye daga karɓar nauyin kuɗaɗen da aka ɗora musu ba bisa ƙa’ida ba.

Ta kuma yi gargadi ga sauran makarantu masu zaman kansu a jihar da su kiyaye doka da ƙa’idojin gwamnati, inda ta ce duk wanda ya ci gaba da karya dokoki, ba za a yi masa rangwame ba.

Daga karshe ya nemi jama’a su cigaba da kai Rahoton duk makarantar da ta saba doka yana mai cewa ba’a kafa hukumar sa domin kuntatawa makarantun masu zaman kansu ba saidai domin dawo da su kan hanya idan sun kauce.

19/09/2025

Abinda Kwankwaso ya faɗa akan sauya sheƙa zuwa APC.

An ga gawar Kwamandan NDLEA a Otal a jihar Cross RiverHukumar Yaki da Sha da fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta...
19/09/2025

An ga gawar Kwamandan NDLEA a Otal a jihar Cross River

Hukumar Yaki da Sha da fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta sanar da mutuwar kwamandan ta na jihar Cross River, CN Ogbonna Maurice Uzoma, wanda aka tsinci gawarsa a dakin otal da yake zaune.

Wani jawabi da kakakin hukumar, Femi Babafemi, ya fitar ya ce rahoton rasuwar ya kai ga shugaban hukumar, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), a Maiduguri, jihar Borno, inda yake halartar taron shugabannin hukumomi da ma’aikatar shari’a ta tarayya ta shirya.

Babafemi ya bayyana cewa marigayin kwamanda kwanan nan aka nada shi ya jagoranci ofishin NDLEA na jihar Cross River, inda ya fara aiki a ranar 18 ga watan Agusta, 2025. Ya zauna a wani otal a Calabar na dan lokaci kafin ya samu masauki na dindindin.

A cewarsa, Ogbonna ya shiga aikinsa da himma sosai, kuma an shirya zai jagoranci jami’ansa a wasu ayyuka a safiyar Alhamis, 18 ga Satumba, 2025. Amma tun da misalin karfe 9 na safe ba a samu jin duriyarsa ba, hakan ya sa jami’ansa tare da ma’aikatan otal s**a nufi dakinsa. Duk bugun kofa da kiran wayarsa bai amsa ba.

An ce ma’aikatan otal sun kasa bude kofar daga waje, sai wani daga cikinsu ya shiga ta saman rufin dakin ya bude daga ciki, inda aka tarar da shi ya riga mu gidan gaskiya.

Nan take aka sanar da rundunar ‘yansandan jihar, kuma kwamishinan ‘yansanda da kansa ya ziyarci wurin. Hakan na zuwa a daidai lokacin da ake ci gaba da binciken musabbabin mutuwar.

Domin taimaka wa bincike, shugaban NDLEA ya umarci kwamandan yankin, ACGN Mathew Ewah, da ya koma Calabar domin kula da lamarin.

Yayin da yake jajanta wa iyalan marigayin, Marwa ya ce hukumar tana tare da su a wannan mawuyacin lokaci, tare da addu’ar Allah Ya jikan mamacin.

YANZU-YANZU: Gwamna Fubara ya dawo Jihar Rivers bayan watanni 6 na dokar-ta-ɓaci Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara...
19/09/2025

YANZU-YANZU: Gwamna Fubara ya dawo Jihar Rivers bayan watanni 6 na dokar-ta-ɓaci

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya dawo Fatakwal ranar Juma’a bayan watanni shida da aka dakatar da mulkinsa sak**akon dokar ta-baci da Shugaba Bola Tinubu ya ayyana a ranar 18 ga Maris 2025.

Fubara ya sauka a filin jirgin saman kasa da kasa na Fatakwal da misalin ƙarfe 11:50 na safe, inda dubban magoya baya s**a taru domin tarbar sa.

Sai dai bai bayyana a gidan gwamnati ba duk da taron jama’a da s**a jira shi.

Tun bayan hawan sa mulki a 2023, Fubara ya samu sabani da wanda ya gada, Ministan Abuja Nyesom Wike, rikicin da ya raba majalisar dokokin jihar gida biyu. Lamarin ya sa Tinubu ya nada tsohon hafsan rundunar sojin ruwa, Admiral Ibok-Ete Ibas (rtd.), a matsayin mai rikon gwamnati.

Ibas ya mika mulki ranar Laraba, inda ya bukaci ’yan siyasar jihar da su rungumi tattaunawa da mutunta juna.

Address

Plot 111B Chinyeaka Ohaa Crescent
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily Nigerian Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily Nigerian Hausa:

Share