FUA MEDIA

FUA MEDIA Your trusted source for unbiased political analysis, news, and discussions.

Join our community to stay updated on the latest political developments and engage with fellow citizens who share your passion for democracy

26/07/2025

Fassarar Jawabin Sanata Henry Seriake Dickson A Zaman Majalisar Dattawa Na Musamman Kan Jimamin Rasuwar Buhari

Suna na Sanata Henry Seriake Dickson daga Bayelsa ta Yamma. Ina godiya ga Shugaban Majalisar Dattawa kan wannan damar da ka bani ta cewa abu daya ko biyu kan tsohon Shugaban Kasa marigayi Muhammadu Buhari.

Idan na duba a wannan zauren majalisar ni kadai ne Gwamnan da ke a jam'iyyar adawa a lokacin da aka zabi Buhari a matsayin Shugaban Kasa a 2015 don haka daidai ne wannan damar da ka bani ta magana a kan sa.

A madadin al'ummar Bayelsa ta Yamma mun shiga cikin shugabannin majalisa da Shugaban Kasa, al'ummar masarautar Daura da al'ummar Nijeriya bakidaya wajen jajantawar wannan babban rashin maras misaltuwa da muka yi. Zan je masarautar Daura wadda nake neman sarauta domin jajantawa mai girma Sarki.

'Yan Nijeriya kalilan ne ubangiji ya baiwa irin dama da sukunin da Buhari ya samu, na farko a matsayin shugaban mulkin soji da karancin shekaru na biyu a matsayin zababben shugaban kasa a wa'adin mulki biyu, kuma ya kammala ya yi ritaya a gida.

Kasar mu ta na cikin jimami, ina son in shiga cikin wannan majalisar da al'ummar kasa wajen yabawa Shugaban Kasa wanda ya jagoranci Gwamnatin Tarayya wajen shirya jana'izar musamman ta gwamnati wadda irinta ya kamata a rika yi wa shugabannin mu.

Na bayyana hakan ne domin tsohon Shugaban Kasa, Shehu Shagari bai samu irin wannan karramawar ba don haka na yadda da abin da Tinubu ya yi abin yabawa ne wanda ya kamata a bayyana a matsayin abin da ya kamata a yi wa shugabannin mu da s**a yi kokari wajen bautawa kasa.

Za mu iya kin yadda da manufofinsu da ma siyasarsu saboda bambancin ra'ayin siyasa amma mu mutunta jagorancin da s**a yi, don haka Tinubu ya yi abin da ya kamata ya zama abin koyi.

Shugaban Majalisa, ba shakka Buhari ya gudanar da rayuwar hidimtawa kasa, za mu iya kin yadda da manufofinsa domin ni kaina ban yadda da yawa daga cikin manufofinsa ba.

A yayin da aka cire babban mai shari'a na kasa Walter Onnoghen a wani yanayi, na tara Gwamnonin Kudu- Maso- Kudu muka dauki matsaya daya kuma Buhari bai dauki wani mataki kan mu ba ko ni kaina da na jagorance su.

Ban yadda da Buhari ba kan batun da ya gabatar na kashi uku na al'ummar da ke da albarkarun mai maimakon kashi biyar da muka bukata.

Haka ma ban yadda da matakinsa ba lokacin da shi da Gwamnan Babban Bankin Kasa, Godwin Emefele s**a yi abin da s**a yi wajen canza kudade.

Bugu da kari ban kuma goyi bayyansa ba a bisa kasa shirya taron canza fasalin kasa amma duk da haka Buhari a dukkanin tarukan mu yana nuna dabi'a tagari duk da girman matsayinsa da bambancin shekaru amma yana girmama dukkanin mu Gwamnonin jam'iyyar adawa tare da mutunta mu.

Baya ga wannan a kodayaushe yana yi mana uzuri, zan bada misali da lokacin da ya karbi mulkin kasa a 2015 kuma tattalin arzikin kasa ya tabarbare zai iya yin siyasa da yanayin ta hanyar bayar da tallafi ga Gwamnonin jihohin da jam'iyyarsa ta APC kawai ke mulki kamar yadda aka matsa masa amma bai yi hakan ba sai ya bayar da tallafin ga dukkanin Gwamnoni bakidaya.

Ina ganin dayan Gwamnan da ke nan a lokacin shine Adams Oshomhole, Buhari ya tabbatar dukkanin Gwamnonin jihohi abin da ya kamata a baiwa jihohi an ba su, bai nuna bambancin wannan jihar ta PDP ce ko ta APC mai mulki ba.

Da yawa 'yan Nijeriya ba su san irin matsin tattalin arziki da kasa ta shiga ba a 2015 har zuwa 2020 lokacin da abubuwa s**a daidaita ba, a lokacin Buhari da mataimakinsa Osinbajo da tawagar da yake jagoranta ta masana tattalin arziki s**a fito da hanyoyin samun kudi da goyon bayan majalisar dokoki ta kasa domin tallafawa jihohi wanda ba don hakan ba da kasa ta tabarbare, don haka ya zama wajibi mu gode masa.

Haka ma a yayin da na nemi wa'adin mulki na biyu a 2015, Buhari ya kira ni ya ce mani Dickson kar ka damu na kira hukumar zabe da shugaban sojoji da shugaban jami'an tsaron farin kaya na DSS na ba su umurnin su fadawa jami'ansu su yi abin da ya kamata, ya kuma sake kira na ya ce sako ya isa, ka je ka fara yekuwar neman zabe.

Buhari ya ce mani ya fuskanci magudin zabe a kasar nan don haka a matsayinsa na shugaban kasa ba zai yadda ya hanawa al'umma abin da s**a zaba ba, na yi masa godiya.

Zabe na shine zabe mafi zafi da aka yi a kasar nan wanda ban tunanin an taba yin irinsa, duk da ba su yi biyayya ba, ina da tabbacin shugaban kasa ta, ya bada umurnin duk da yake ba su bi umurninsa ba amma an yi zabe na kuma yi nasara.

A lokacin da muke a kotun koli a 2020 bayan kammala wa'adina, Buhari wanda mutanensa suke a Bayelsa domin rantsar da dan takarar APC wanda aka bayyana ya samu nasara a zaben, amma bai kira kotun koli domin a yi watsi da karar mu ba har kasa da awanni 24 a inda kotun ta yanke hukuncin dan takarar su bai cancanta ba amma Buhari ya karbi hukuncin.

A lokacin da ya hadu da Gwamnan, sai cikin barkwanci ya ce masa wato kai da maigidan ka ku ke da fannin shari'a (s**a yi dariya) wannan dabi'ar mutanen kwarai ce.

Daga karshe muna yabawa iyalansa kan samun shi da muka yi a wannan kasa, muna rokon Allah ya gafarta masa ya yafe masa kura- kuransa.

Jamilu Abubakar.
Mataimaki na musamman kan yada labarai ga Sanata Henry Seriake Dickson.
26/07/2025.

26/07/2025
19/07/2025

Sanata Henry Seriake Dickson yace; A jiya na bi sahun takwarorina wajen halartar wani taron bita na kwamitocin hadin gwiwa na Majalisar Dokoki kan Ilimi, inda muka tattauna kan kalubalen da ke tattare da ilimin firamare, musamman kan batun gyara da aka yi wa dokar karatun UBE.

Kamar yadda kowa ya sani, na sha bayyana ra’ayi na a zauren majalisar dattijai so da dama kan bukatar karfafa ilimin boko da rage adadin yaran da ba sa zuwa makaranta a kasar nan.

Har ila yau, na jaddada bukatar tattaunawa kan hanyoyin karfafawa da bunkasa iyawa ta fuskar neman ilimin harsuna, al'adu, da wayewar da ke da muhimmanci wajen fadada tunanin 'yan Nijeriya.

Saboda haka, na yi magana ne na goyon bayan ilimin Larabci ko Addinin Musulunci ga Musulmi, wadanda su ne babban tushen albarkatun kasa, da kuma ilimin Faransanci, a matsayinsa na guda daga cikin harsunan da ake koyarwa a kasa, ya kamata a karfafa, inganta su kamar yadda ake yiwa karatun Boko.

Zai kasance cikin maslahar ƙasarmu mu wadata yaran ƙasar nan da ilimin harsuna, al'adu, da wayewa gwargwadon iko don shirya su don yin gogayya da takwarorinsu na duniya.

Kamar yadda nake fada a kowane dandali, saka hannun jari a fannin ilimi ya kamata ya zama babban fifiko ga kowa a cikin gwamnati - shugaban kasa ko gwamna, kamar yadda na yi a matsayin Gwamna na tsawon shekaru takwas, ko da a lokacin koma bayan tattalin arziki, ba'a dakatar da tsare-tsaren ilimi, fannin ilimi yana bukatar a kara karfafa shi, tare da mai da hankali kan inganta cibiyoyi da tsari mai kyau na ilmantar da malamai, da kuma samar da manufofi masu kyau wajen zuba kudade domin tallafawa ilimin.

19/07/2025
15/07/2025
13/07/2025

Gobe Litinin 14 ga watan Julayen 2025 da misalin karfe sha biyu 12pm na rana Sanata Henry Seriake Dickson zai halarci Taro a Barcelona Hotel, Wuse 2, Abuja dazai yi jawabi a Taron karawa juna sani da hukumar Civil Society’s Alliance for Democratic Change (NCSADC). Ta shirya

taron zai kasance Kai tsaye a Wadan nan kafafen sadarwa na zamani

Facebook: @ https://www.facebook.com/share/198Qc7jkzE/?mibextid=wwXIfr

YouTube: @ https://youtube.com/?si=8a0JvM1TLOx9XmWp

Idan muka hada hannu zamu iya karfafa Dumukuradiyaya domin dorewar ta.

Kuyi Mana Karin Bayani akan wan nan Matashiyar Farfesar
13/07/2025

Kuyi Mana Karin Bayani akan wan nan Matashiyar Farfesar

13/07/2025

Jiki magayi! Gaskiya Bata Neman ado!!

11/07/2025

Mu nemi Jaridar Leadership Hausa ta yau Juma'a a shafi na 11 zakuga Jawabin Senata Henry Seriake Dickson akan Batun Hana karbar kudi kafin zaben Shugaba ko Dan takara!!

09/07/2025

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when FUA MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share