Jakadiya Hausa

  • Home
  • Jakadiya Hausa

Jakadiya Hausa Ku Kasance Da Jaridar "JAKADIYA HAUSA" Domin Samun Ingantattun Labarai.
(423)

Ku Ajiiye Son Zuciya Da Bangarancin Siyasa Ku Faɗawa Shugaban Kasa Ba Za Mu Zaɓe Shi Ba Idan Babu Tsaro A Arewa, Cewar F...
29/07/2025

Ku Ajiiye Son Zuciya Da Bangarancin Siyasa Ku Faɗawa Shugaban Kasa Ba Za Mu Zaɓe Shi Ba Idan Babu Tsaro A Arewa, Cewar Fadila H. Aliyu (GoldenPen).

Me za ku ce?

JA'O'JI YA CANCANCI RIƘE KOWANNE IRIN MUƘAMI:  ~Saƙo Zuwa Ga Shugaban ƙasa......Saƙon Wasu Daga Cikin Matasan Arewa Kena...
25/07/2025

JA'O'JI YA CANCANCI RIƘE KOWANNE IRIN MUƘAMI: ~Saƙo Zuwa Ga Shugaban ƙasa.
.....Saƙon Wasu Daga Cikin Matasan Arewa Kenan Ga shugaban ƙasa Kan Batun Maye Gurbin Kujerar Ministan Walwala da jinƙai Da Nasir Bala Aminu "Ja'oji

Biyo bayan naɗa Nentawe Shugaban Jam'iyyar APC na ƙasa, Da yawa daga cikin dubban matasa dake Kano, dama wasu daga cikin Yankunan Arewa na cigaba da ƙira ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinibu, da cewa ya naɗa Nasir Bala Aminu Ja'oji a Matsayin Ministan Walwala da jinƙai.

A cewar Matasan "Ja'oji mutum ne gwarzo kuma Jajirtacce wanda yayi fice wajen gina al'umma, kawo cigaba Ga al'umma, Musamman a Kano, Arewa, dama ƙasa baki ɗaya.

Yana ɗaya daga cikin ƴan siyasar dakuma Jajirtattun mutanen da suke gina Rayuwar Talakawa, yanada zuciyar Tausayi dakuma dabarun kawo cigaba, yanada gogewa dakuma ilmin gudanar da mulki, Hakan zai taimaka masa wajen riƙe kowacce irin ma'aikata domin ciyar da wannan ƙasa Gaba.

Bawa Ja'oji wannan Matsayin kamar ajiye kwarya a gurbinta ne, domin tabbas zai gabatar da ayyukansa cikin tsari, kuma bazai taɓa watsawa mutane ƙasa a ido ba, yana ɗaya daga cikin waɗanda s**a zama abin kwatance ga al'umma da muke ciki Yanzu.

A.Y SADEEQ
Chairman Nigerian Voice of politics

Har Yanzu Matasa A Jihar Gombe Na Cin Moriyar Ayyukan ICT Na  Professor Isa Ali Pantami Daga Muhammad Kwairi Waziri  A r...
24/07/2025

Har Yanzu Matasa A Jihar Gombe Na Cin Moriyar Ayyukan ICT Na Professor Isa Ali Pantami

Daga Muhammad Kwairi Waziri

A ranar 16 ga Oktoba, 2020, tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Farfesa Isa Ali Pantami, CON, ya kaddamar da manyan ayyukan fasahar sadarwa a Jihar Gombe, wadanda s**a zama ginshikin ci gaban matasa da ilimin zamani.

Cikin ayyukan da aka kaddamar akwai ICT Incubation Park a Jami’ar Jihar Gombe, cibiyar koyon fasahar IT a Tudun Wada, da kuma ofishin yankin hukumar Nigerian Communications Satellite Systems.

A lokacin kaddamarwar, Farfesa Pantami ya bayyana cewa a wannan zamani, ƙwarewa ta fi takardar shaidar kammala karatu muhimmanci. Ya ce, “Matasa masu ƙwarewa su ne ke zama masu samar da aiki, yayin da marasa ƙwarewa ke zama masu neman aiki.”

Shekaru hudu bayan haka, wadannan wurare na ci gaba da kasancewa abin shaida ga hangen nesa na Farfesa Pantami wajen habaka ilimin zamani, ƙarfafa matasa da inganta kirkire-kirkiren ICT a Jihar Gombe.


— *MUD*

Har Yanzu Matasa A Jihar Gombe Na Cin Moriyar Ayyukan ICT Na  Professor Isa Ali Pantami Daga Muhammad Kwairi Waziri A ra...
24/07/2025

Har Yanzu Matasa A Jihar Gombe Na Cin Moriyar Ayyukan ICT Na Professor Isa Ali Pantami

Daga Muhammad Kwairi Waziri

A ranar 16 ga Oktoba, 2020, tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Farfesa Isa Ali Pantami, CON, ya kaddamar da manyan ayyukan fasahar sadarwa a Jihar Gombe, wadanda s**a zama ginshikin ci gaban matasa da ilimin zamani.

Cikin ayyukan da aka kaddamar akwai ICT Incubation Park a Jami’ar Jihar Gombe, cibiyar koyon fasahar IT a Tudun Wada, da kuma ofishin yankin hukumar Nigerian Communications Satellite Systems.

A lokacin kaddamarwar, Farfesa Pantami ya bayyana cewa a wannan zamani, ƙwarewa ta fi takardar shaidar kammala karatu muhimmanci. Ya ce, “Matasa masu ƙwarewa su ne ke zama masu samar da aiki, yayin da marasa ƙwarewa ke zama masu neman aiki.”

Shekaru hudu bayan haka, wadannan wurare na ci gaba da kasancewa abin shaida ga hangen nesa na Farfesa Pantami wajen habaka ilimin zamani, ƙarfafa matasa da inganta kirkire-kirkiren ICT a Jihar Gombe.


— *MUD*

YANZU-YANZU: Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙwace Fasfon Din Sanata Natasha A Filin Jirgin Sama Na AbujaDaga Muhammad Kwairi W...
24/07/2025

YANZU-YANZU: Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙwace Fasfon Din Sanata Natasha A Filin Jirgin Sama Na Abuja

Daga Muhammad Kwairi Waziri

A ranar Laraba 24 ga Yuli, 2025, jami’an hukumar shige da fice na Najeriya sun tsaida Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan a tashar jirgin sama ta Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, inda s**a karɓe fasfon tafiyarta kafin daga bisani aka bar ta ta tashi zuwa Landan.

Sanata Natasha, wacce ke wakiltar mazabar Kogi ta Tsakiya a majalisar dattawa, ta isa filin jirgin tare da mijinta Chief Emmanuel Uduaghan, inda jami’an s**a dakatar da ita bisa zargin tsaro da ba a fayyace ba.

Wani shaidar gani da ido ya bayyana cewa an ja lokaci kafin a bai wa Sanatar damar shiga jirgin British Airways, lamarin da ya janyo tambayoyi daga jama'a game da dalilin wannan mataki da kuma ko yana da nasaba da siyasa.

Sai dai har yanzu babu wani karin bayani daga hukumomin da s**a aiwatar da matakin, kuma Sanatar ba ta fitar da sanarwa kai tsaye ba kan abin da ya faru.

DA ƊUMI-ƊUMI: Sowore Ya Maka Hukumar Ƴan Sanda Kotu Kan Sace Masa GilashiDaga Muhammad Kwari WaziriTsohon ɗan takarar sh...
23/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Sowore Ya Maka Hukumar Ƴan Sanda Kotu Kan Sace Masa Gilashi

Daga Muhammad Kwari Waziri

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa kuma ɗan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan adam, Omoyele Sowore, ya shigar da ƙara a kotu yana zargin wani jami’in ‘yan sanda da sace masa gilashin AI mai ƙayatarwa yayin zanga-zangar da aka gudanar a hedikwatar rundunar ƴan sanda da ke Abuja.

A cewar Sowore, jami’in wanda aka bayyana sunansa da "Victor", yana aiki ne a matsayin mai ɗaukar bidiyo na ƴan sanda a ƙarƙashin CSP Muyiwa Adejobi, ya sace gilashin ne da nufin su fitar da bayanan bidiyo da gilashin ke ɗauka.

Lauyan Sowore ya buƙaci a cafke jami’in tare da dawo da gilashin, yana mai cewa hakan ya nuna cin zarafi da amfani da iko ba bisa ƙa'ida ba.

Sowore ya bayyana cewa gilashin na da fasahar zamani da ke ɗaukar bidiyo da murya, kuma akwai muhimman bayanai da ke ciki dangane da yadda zanga-zangar ta gudana.

Ana ci gaba da sa ido kan yadda shari’ar za ta kaya.

Majalisar Dattawan Nijeriya Za Ta Gudanar Da Zama Na Musamman Domin Girmama Marigayi Shugaba BuhariDaga Muhammad Kwairi ...
22/07/2025

Majalisar Dattawan Nijeriya Za Ta Gudanar Da Zama Na Musamman Domin Girmama Marigayi Shugaba Buhari

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Majalisar Dattawan Najeriya ta shirya gudanar da zamangirmamawa na musamman a ranar Laraba, 23 ga Yuli, 2025, domin tunawa da kuma girmama tsohon Shugaban Ƙasa, Marigayi Janar Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a birnin London ranar 13 ga Yuli, 2025.

Zaman na musamman zai gudana a zauren majalisar dattawa inda za a karanta tarihin rayuwarsa da hidimarsa ga ƙasa, tare da gabatar da jawabai daga manyan 'yan majalisa da sauran jiga-jigan gwamnati.

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana cewa wannan zaman alama ce ta girmamawa ga mutumin da ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidima ga ƙasar Najeriya a lokuta daban-daban, ciki har da lokacin mulkinsa a matsayin shugaban ƙasa daga 2015 zuwa 2023.

Ana sa ran zaman zai jawo halartar shugabanni daga sassa daban-daban na gwamnati da 'yan uwa da abokan arzikin marigayin.

Jagororin Hukumin Gwamnatin Tarayya Sun Kaiwa Professor Isa Ali Pantami  Ta’aziyyar Rasuwar Shugaba BuhariDaga Muhammad ...
22/07/2025

Jagororin Hukumin Gwamnatin Tarayya Sun Kaiwa Professor Isa Ali Pantami Ta’aziyyar Rasuwar Shugaba Buhari

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Wasu daga cikin manyan shugabannin hukumomin Gwamnatin Tarayya da Professor Isa Ali Ibrahim Pantami ya tallafawa samun mukamai, sun jagoranci ziyarar ta’aziyya zuwa gare shi, biyo bayan rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a asibiti da ke London a ranar 13 ga Yuli, 2025.

Ziyarar ta gudana ne ƙarƙashin jagorancin Alhaji Ishaq Ali Kalshingi, inda wakilai daga hukumomi da dama s**a halarta, ciki har da: NCC, GBB, NIMC, NITDA, NFIU, POLICE, NEDC, CBN, da wasu.

A yayin karɓar ta’aziyyar, Prof. Pantami ya bayyana wasu daga cikin kyawawan halayen Marigayi Baba Buhari, ciki har da rikon gaskiya, amana, karamci da girmama na gaba – halaye da ya ce sun cancanci a yi koyi da su.

Ya kuma yi kira da a ci gaba da yi wa Marigayi Shugaba Buhari addu’a, tare da rokon Allah ya gafarta masa, ya sanya shi cikin rahama da Aljanna Firdausi. Ya kuma roki gafara da rahama ga dukkan iyaye da malamai da s**a rigamu.

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun b...
21/07/2025

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba

Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun bazu da wani labari mara tushe a kafafen sada zumunta da ke cewa Muhammad Babangida, ɗan tsohon shugaban kasa Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya ƙi amincewa da nadin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya masa na chairman BOA.

Mun tabbatar da cewa wannan labarin ƙarya ne tsagwaronta, domin ba Muhammad Babangida bane ya fitar da sanarwar da ke yawo ba. Lambar da ke jikin takardar da aka yaɗa da kuma sa hannun da ke cikinta duk ba nasa ba ne.

Wannan wata makirci ce ta ɓatanci da ƙoƙarin jefa shakku a tsakanin shugaban ƙasa da manyan 'yan Najeriya, musamman waɗanda ke da sunaye da martaba a cikin al'umma.

Muhammad Babangida bai fito ya musanta nadin ba, kuma babu wata cikakkiyar shaida daga gare shi ko daga hannunsa da ke nuna ya ƙi karɓar kujerar. Wannan yana nuni da cewa an ƙirƙiri wannan labari ne domin yaudarar jama'a da haddasa ruɗani.

Muna kira ga 'yan Najeriya da su yi hattara da labaran ƙarya da ake yawan yaɗawa, su nemi gaskiya daga ingantattun majiyoyi kafin yarda da kowace irin sanarwa.

Allah ya ƙara haɗin kanmu da cigaban ƙasar nan.

21/07/2025

YANZU-YANZU: An Fara Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Karin Albashi Da Fanshon 'Yan Sanda Masu Aiki Da Masu Ritaya

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Yayin wata gagarumar zanga-zanga da aka gudanar a yau, Omoyele Sowore, ɗan gwagwarmaya kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, ya jagoranci gungun masu zanga-zanga domin neman a inganta rayuwar jami’an ‘yan sanda a Najeriya.

Masu zanga-zangar sun bukaci gwamnati ta duba halin kuncin da ‘yan sanda ke fuskanta, musamman yadda albashinsu ke ƙasa da kima, tare da rashin kula da ‘yan sanda da s**a yi ritaya. Sun ce lokaci ya yi da za a mutunta waɗanda ke bayar da rayukansu don kare lafiyar jama’a da dukiyarsu.

Sowore ya bayyana cewa, "Yan sanda su ne ginshiƙin tsaro a ƙasa, amma ana wulaƙanta su da iyalansu. Ba za mu ci gaba da shiru ba alhali suna rayuwa cikin talauci bayan shekaru da dama na hidima.”

Masu zanga-zangar sun rike kwalaye masu ɗauke da rubuce-rubuce kamar:

“A biyan ‘yan sanda albashi mai kyau yanzu!”

“Rayuwa mai kyau ga masu ritaya!”

“’Yan sanda ma mutane ne!”

Zanga-zangar ta gudana cikin lumana, tare da jami’an tsaro da s**a tabbatar da zaman lafiya a wajen.

Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Matasan Arewa Sun Gargadi Atiku da El-RufaiKun...
19/07/2025

Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Matasan Arewa Sun Gargadi Atiku da El-Rufai

Kungiyar Matasa Ta Arewa (Northern Youth Frontiers) ta bayyana damuwarsu kan yadda wasu 'yan siyasa ke ƙoƙarin amfani da rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari domin yaudarar mutane da neman samun goyon bayansu.

A cewar kungiyar, Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai sun nuna kamar su abokai ne na Buhari domin su karɓi ƙaunar jama'a, alhali sun shafe shekaru suna adawa da akidu da manufofin Buhari tun yana raye.

Wannan abin da suke yi ruɗi ne, karya ce, kuma cin fuska ne ga marigayin shugaban da ya sadaukar da rayuwarsa ga ƙasar nan.

Kungiyar ta ce waɗannan 'yan siyasa ba su taɓa goyon bayan Buhari ba, kuma yanzu suna ƙoƙarin nuna soyayya ta bogi domin su karɓi ra'ayin mutanen Arewa — musamman bayan mutuwar sa.

“Matasan Arewa ba za su bari a ci zarafin Buhari ba.”

Matasan sun ce ba za su yarda a yi amfani da mutuwar Buhari a matsayin hanyar da za a fake domin yaudarar al’umma ba. Sun kuma roƙi jama’ar Arewa da su yi hankali da siyasar ruɗu da wasu ke ƙoƙarin kawowa a cikin lokaci mai muhimmanci na jimami da girmamawa.

Mutuwar Buhari ba siyasa bace. Lokaci ne na tunani da haɗin kai, ba na neman karɓuwa da nuna ƙarya ba.”

Kungiyar ta ƙara da cewa Atiku da El-Rufai su dakata da wannan salon siyasa, su girmama Buhari, su kuma bar mutanen Arewa su zaɓi gaskiya da amintattu, ba masu nuna soyayya ta ɗan lokaci ba.

Ku dakata da fakewa da mutuwar Buhari. Mutumin da kuka ƙi a raye, ba ku da ikon fakewa da shi bayan ya rasu.

✍️ Northern Youth Frontiers
Sakon Gargaɗi daga Matasan Arewa

18/07/2025

Daga Karshe Shiekh Sani Yahaya Jingir Ya Janye Kalaman Sa Da Ya Yiwa Shiekh Sambo Yayin Da Ya Karrama Peter Obi A Jihar Kaduna

Address

Maitama

005

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jakadiya Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jakadiya Hausa:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share