VOA Hausa Reporters

VOA Hausa Reporters Kafar yada labaru ta musamman don samun sahihan labaru da shirye-shirye

SAUDIYYA MUSANTA HARI KAN FILIN JIRGIN SAMA NA YARIMA SULTANSaudiyya ta musanta wani rahoton hari kan filin jiragen sama...
09/06/2026

SAUDIYYA MUSANTA HARI KAN FILIN JIRGIN SAMA NA YARIMA SULTAN

Saudiyya ta musanta wani rahoton hari kan filin jiragen sama na Yarima Sultan bin Abdul'aziz a yankin Alkharj.
Kakakin rundunar sojan Saudiyya Janar Turki Almaliki ya ce bayanan kai harin ba gaskiya ba ne.
An dai kunna jiniyar ankarar da mutane yiwuwar hatsari don harbo makami da a ka yi daga cikin Yaman amma makamin ya tsaya a hanya kuma harin bai yiwu yadda a ka tsara ba.
Hakika an daina samun hare-hare daga 'yan houthi a Yaman zuwa Saudiyya tun sulhun da a ka samu tsakanin Saudiyya da Iran zamanin shugabacin marigayi shugaban Iran Ebrahim Raisi da marigayi ministan wajen Iran Amir Hossein Abdollahian ya yi ta kai kawo har a ka dawo da dangantakar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu.
Kasar Sin ta taka rawa wajen sulhunta Iran da Saudiyya amma hare-hare na Amurka da Isra'ila kan Iran sun sa mayar da hannun agogo baya.

ISRA’ILA DA IRAN SUN SHIGA SABON DAUKI BA DADIIsra'ila da Iran sun shiga sabon dauki ba dadi da juna da hakan ke barazan...
09/06/2026

ISRA’ILA DA IRAN SUN SHIGA SABON DAUKI BA DADI

Isra'ila da Iran sun shiga sabon dauki ba dadi da juna da hakan ke barazana ga wanzuwar shirin tsagaita wuta na Amurka.
Hare-hare da Isra’ila ke kai wa kan Lebanon da zummar gamawa da duk 'yan Hezbollah da Iran ke marawa baya ya haddasa daukar matakai daga Iran din.
An yi musayar hare-hare tsakanin kasashen biyu kuma an ga wajejen da Isra'ila ta kai wa farmaki a Tehran, Tabriz da Isfahan
Iran na bukatar a shigar da Lebanon a cikin yarjejeniyar tsagaita wuta ta na mai zargin Amurka da Isra’ila da keta yarjejeniyar.
Ba ma abun da ya fi zama damuwa irin hare-hare kan yankin Dahiyeh na kudancin Lebanon da kuma sassan tasoshin ruwa na Iran.
A nan alamu na nuna sai an samu jajircewa daga mai shiga tsakani wato Pakistan don wanzar da yarjejeniyar tsagaita wuta a yakin da Amurka da Isra’ila ke yi da Iran.

GHANA TA DAWO DA 'YAN KASARTA 1000 DAGA AFURKA TA KUDU Kasar Ghana ta yi nasarar dauko 'yan kasarta kimanin 1000 daga Af...
09/06/2026

GHANA TA DAWO DA 'YAN KASARTA 1000 DAGA AFURKA TA KUDU

Kasar Ghana ta yi nasarar dauko 'yan kasarta kimanin 1000 daga Afurka ta kudu inda a ke fama da kin jinin baki.
'Yan Afurka bakar fata na fama da hare-hare daga 'yan Afurka ta kudu kuma har hakan kan yi sanadiyyar mutuwa ko kisan gilla da asarar dukiya.
Ministan harkokin wajen Ghana Samuel Ablakwa ya fitar da sanarwar dawo da mutanen zuwa gida don kare su daga fitinar Afurka ta kudu.
An tanadi tsari na maraba da wadanda a ka dawo da su ta hanyar alkawuran sama mu su aiki kuma an raba mu su layukan waya da damar hawa yanar gizo don samun sadarwa da dangi da sauran abokan hulda.
Mutanen sun yabawa shugaban Ghana John Dramani Mahama don daukin da ya yi mu su.
Najeriya ma ta dau matakai ciki har da magana da hukumomin Afurka ta kudu su hukunta masu hannu wajen hare-haren kin jinin baki don ya zama matakin dakile mummunar dabi’ar.

GWAMNATIN OYO TA RUGUJE GIDAN BOYE WADANDA A KA SACE A BADUNGwamnatin jihar Oyo a kudu maso yammacin Najeriya ta ruguje ...
09/06/2026

GWAMNATIN OYO TA RUGUJE GIDAN BOYE WADANDA A KA SACE A BADUN

Gwamnatin jihar Oyo a kudu maso yammacin Najeriya ta ruguje wani gida da barayin mutane ke adana wadanda su ka sace a babban birnin jihar Badun.
Wannan ya biyo bayan gano 'yar uwar tsohon ministar lantarki Adelabu da barayin su ka sace ranar 3 ga watan nan su ka ajiye su a gidan.
Akasin ya faro ne da sace Busayo John Paul a lokacin da ta ke kai 'ya'yanta tagwaye Peter da Paul makaranta a nan Badun din.
Ruguje ginin ya zo 'yan sa'o'i bayan kwamishinan 'yan sanda na jihar CP Abimbola Olugbenga ya zaga da manema labaru don duba ginin.
Kwamishina Olugbenga ya ce akwai mamaki yadda gidan da ke tsakiyar jama’a kuma mutane na ganin wadanda a ke satowa a kawo amma ba tare da kai rahoto ga hukuma ba.
Wadanda a ka sacen na cewa su na jin hada-hadar makwabtan gidan amma ba su iya fitowa ba.
Olugbenga ya bukaci jama’a su rika kai rahoton satar mutane ko wasu laifuka don daukar matakan da su ka dace.

09/06/2026

NEPU KANKAT-Alhaji Hussaini Gariko ya ce da alamun wadanda a ka tsinta a kan kw@lta ne ke aib@ta Sardauna kuma ba don albarkacin Sardauna ba da yau ‘yan lakada-kawas din nan b@yi ne. Ga shi yau su na hura h@nci su na tinkaho a Arewa da Sardauna ya gina ya kuma sadaukar da ransa👇👇👇👇👇👇👇

07/06/2026

GWAMNATIN JIHAR KATSINA A NAJERIYA TA FARA AIKIN TANTANCE BURTALI KO LABI DOMIN MAGANCE MATSALAR RIKICIN MANOMA DA MAKIYAYA A JIHAR.

Shugaban karamar Hukumar Batsari Alh.Mannir Mu'azu Ruma da ya kaddamar da aikin Fidda labin a karamar Hukumarsa jiya Asabar yace Umurni ne daga Gwamnatin Jihar Katsina a kokarin Gwamnatin na maido da zaman lafiya.
Karamar Hukumar ta Batsari dai na daya daga cikin yankunan da aka samu saukin hare haren yanbindigar tun bayan wani sulhun da akayi a Shekarar bara.
Shugaban karamar hukumar ta Batsari yace aikin samar da burtalin shanun yana da matukar Muhimmanci wajan maido da cikakken zaman lafiya,
Kamar yadda yayi Karin bayani a cikin zantawarmu ta wayar salula👇👇👇.

07/06/2026

GWAMNAN JIHAR BAUCHI SANATA BALA MUHAMMAD KAURAN BAUCHI, YACE RASHIN HUKUNCI NE YASA AYYUKAN TA'ADDANCI KE KARA YAWA A NAJERIYA.

Gwamnan Jihar ta Bauchi Wanda yake jawabi a garin lanzai ta Jihar Bauchin yace izgilanci da raina hukuma ne yasa masu Ayyukan ta,addanci ke cin karensu babu babbaka,
Gwamnan dai yaje garin na lanzai ne domin yin jaje akan ta,addancin kisan Jama,a da kona gidaje a sakamakon Wani tashin hankali,kamar yadda zakuji Karin bayani a cikin rahoton Abdulwahabu Muhammad Daga Bauchi 👇👇👇.

06/06/2026

BABU DAN MAJALISAR DA ZAI IYA FADAWA GWAMNA BAGO GASKIYA A JIHAR NEJA,,
''INJI BARISTA REGE''
Kashi na biyu na zantawa da masanin shari,a Barista Ibrahim Ahmadu Rege yayi bayani akan halin da yankin Arewacin Jihar Neja ke ciki na rashin samar da ababen more rayuwa ga Al,ummar yankin👇👇👇.

06/06/2026

MASU KOKARIN RABA HAUSAWA DA FULANI SUN KARBO KWANGILAR TARWATSA AREWACIN NIGERIA NE,,,
'''BARISTA IBRAHIM REGE'''
Wani masanin dokar Kasa a Nigeria lauya mai zaman kansa a Jihar Neja Barista Ibrahim Ahmadu Rege yayi bayani akan matsalar rashin tsaro dake ci gaba da addabar Yankin Arewacin Nigeria,
Ya Amince da cewa kwangila ce wasu s**a karbo daga makiya Domin tarwatsa Arewacin kasar,
Sannan ya goyi bayan kalaman Sarkin Kebbin Argungu na cewa kowa ya nemi Makamin kare kanshi a hukumance,
Kamar yadda zakuji acikin zantawar kashi na farko,
zamu kawo maku kashi na biyu nan gaba Insha Allahu👇👇👇.

06/06/2026

NEPU- Yadda Malam Aminu Kano ya takawa jama’arsa birki a lokacin da su ka zo da murnar kisan gilla ga Sardauna. Malam Aminu maimakon dariya ya ce barkewa da kuka ya dace a yi don ba wani jigo da Arewa ke da shi fiye da Sardauna. Babban mukarrabin Malam Aminu wato shugaban rundunar adalci Alhaji Abdulkarim Dayyabu ya zayyana labarin dalla-dalla👇👇👇👇👇👇

Address

No 32 Dennis Osadebey Apo Legislative Quarters
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when VOA Hausa Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share