23/08/2025
Al’ummar Fulani sun yi Allah-wadai da kisan sojoji, sun bukaci a kasance masu gaskiya wajen samar da zaman lafiya a Karim
Fassarar lado Salisu M Garba daga Jalingo
Daga Sa’idu Adamu, Jalingo
Al’ummar Fulani a karamar hukumar Karim Lamido ta jihar Taraba sun yi Allah-wadai da kisan sojoji biyu da aka tura yin aikin sulhu a yankin.
Sakataren kungiyar, Alhaji Ahmed Isa Karim, wanda ya bayyana hakan yayin tattaunawa da ’yan jarida a Jalingo ranar Asabar, ya ce lamarin abin takaici ne matuka kuma bai k**ata ya faru ba tun da farko.
Yayin da yake bayyana yadda abin ya faru, Ahmed ya ce, ko da yake bai goyi bayan harin kan jami’an tsaro ba, Fulani sun tilasta su kare kansu ne lokacin da sojoji s**a tsaya tare da ’yan kungiyar Bandawa suna kashe Fulani da shanunsu.
Ya kara da cewa ya k**ata sojoji su tsaya ne a tsakani don raba fada, kuma a ga suna nuna adalci maimakon goyon bayan kowane bangare.
“Kisan sojoji biyu abin bakin ciki ne matuka, kuma bai k**ata ya faru ba kwata-kwata. Duk da haka, yana da matukar muhimmanci a fayyace gaskiya. Sojoji sun tsaya tare da ’yan kungiyar Bandawa wadanda s**a kai hari kan makiyaya tun da safe, s**a kuma sha mamaki.
“Daga bisani, ’yan Bandawa s**a dawo da sojoji s**a ci gaba da kashe shanunmu da mutanenmu, har sai da mutanenmu s**a daina gudu s**a dauki fansa, wanda ya kai ga mutuwar sojojin biyu.
“A halin yanzu, sojoji suna tsare Fulani a yankin ba tare da bambanci ba, suna kuma kwace shanu suna kaisu idan s**a gani. Wannan ba daidai ba ne. Ba dukkan Fulani ne ’yan ta’adda ba ko kuma s**a yi hannun wajen kisan sojojin. Don haka wannan nuna wariya da ake yi wa al’ummarmu a yankin ba daidai ba ne ko kadan.
“Haka kuma, sun kwace shanu fiye da dubu guda da suke a harabar sakatariyar karamar hukumar yanzu. Ya k**ata a mika su ga mamallakinsu. Jiya ma sun je masallaci lokacin sallar Juma’a s**a k**a mutane. Me ya sa rundunar sojin Najeriya za ta sauka matakin da zai sa ta shiga wuraren ibada tana k**a mutane? Wannan abin kunya ne, kuma dole a yi tir da shi daga dukkan mai hankali.
“Muna kira ga hukumomin da abin ya shafa su gaggauta shiga tsakani don samar da mafita mai adalci, tare da mayar da shanu ga mamallakinsu. Daukar bangare a rikici ba zai kawo sulhu ba, sai dai kara dagula lamarin. Don haka muna sake kira ga sojin Najeriya da su kasance masu gaskiya wajen gudanar da aikin da yak**ata ya kasance na ’yan sanda da Civil Defence, wanda yanzu s**a karba kansu.”
Da yake tabbatar da lamarin a ranar Juma’a, mai magana da yawun ’yan sanda, James Leshen, ya ce an tura jami’an tsaro zuwa yankin don dawo da doka da oda.
“An aika jami’an tsaro zuwa yankin don shawo kan halin da ake ciki da kuma hana karin asarar rayuka,” in ji Leshen, yana mai cewa ana ci gaba da tantance adadin mutanen da abin ya shafa.
Shima Musa Garba, shugaban matasa a Karim-Lamido, ya bayyana kisan sojojin a matsayin “abin bakin cikin da ya nuna bukatar gwamnati ta dauki tsauraran matakai.”
“Mutanenmu sun gaji da yin gudu daga gidajensu. Muna bukatar mafita ta dindindin ga wannan kisan da babu ma’ana,” in ji shi.
Rikicin manoma da makiyaya ya ci gaba da zama babbar barazana ta tsaro a jihar Taraba, musamman a yankuna irin su Karim-Lamido, Lau, Wukari, Bali, da Gassol. Sabani kan amfani da kasa, wuraren kiwo, da samun ruwa na daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa rikicin.
Sai dai har yanzu rundunar sojin Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa ba kan lamarin, kodayake Laftanar Umar Mohamed, mai rikon kwarya na mai magana da yawun rundunar 6 Brigade, ya tabbatar da faruwar lamarin.