VOA Hausa Reporters

VOA Hausa Reporters Kafar yada labaru ta musamman don samun sahihan labaru da shirye-shirye

23/08/2025

GWAMNONIN JAM,IYYAR PDP A NIGERIA CIKIN SHIGAR GARGAJIYA A GUSAU FADAR GWAMNATIN JIHAR ZAMFARA.

DAGA ABDURRAZAK BELLO KAURA A GUSAU.

GWAMNAN JIHAR ZAMFARA A NIGERIA DAUDA LAWAL DARE YA GANA DA GWAMNONIN PDP.RAHOTON ABDRAZZAK BELLO KAURA DAGA GUSAU.Gwamn...
23/08/2025

GWAMNAN JIHAR ZAMFARA A NIGERIA DAUDA LAWAL DARE YA GANA DA GWAMNONIN PDP.

RAHOTON ABDRAZZAK BELLO KAURA DAGA GUSAU.

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, yanzu haka yana karbar bakuncin takwarorinsa Gwamnonin na jam’iyyar PDP a Gusau a yau Asabar, 23 ga watan Agusta, 2025, domin gudanar da wata muhimmiyar tattaunawa da nufin daidaita alkiblar jam’iyyar gabanin babban taronta na kasa.

Gwamnonin sun isa Gusau Babban Birnin Jihar Zamfara ne da yammacin jiya Juma’a domin gudanar da zaman sirri da suke yi a yau.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar, an bayyana taron a matsayin wani muhimmin taro na tattaunawa kan muhimman dabarun siyasa da kuma samar da hadin kai a cikin jam’iyyar.

"Gwamnonin sun hallara ne domin wani muhimmin zama na kungiyar gwamnonin PDP. Gwamna Lawal ya shirya liyafar cin abincin dare a daren jiya, gabanin taron dabarun." in ji sanarwar

Sanarwar ta ci gaba da cewa taron zai ba da dama ga shugabannin jam’iyyar don magance matsalolin siyasa, da karfafa hadin kan cikin gida, da hada kai kan ayyukan ci gaba a jihohinsu.

Bugu da kari, gwamnonin a halin yanzu suna tattaunawa kan shirye-shiryen babban taron kasa mai zuwa wanda kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP na kasa ya shirya gudanarwa a birnin Ibadan na jihar Oyo a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.

Al’ummar Fulani sun yi Allah-wadai da kisan sojoji, sun bukaci a kasance masu gaskiya wajen samar da zaman lafiya a Kari...
23/08/2025

Al’ummar Fulani sun yi Allah-wadai da kisan sojoji, sun bukaci a kasance masu gaskiya wajen samar da zaman lafiya a Karim

Fassarar lado Salisu M Garba daga Jalingo

Daga Sa’idu Adamu, Jalingo

Al’ummar Fulani a karamar hukumar Karim Lamido ta jihar Taraba sun yi Allah-wadai da kisan sojoji biyu da aka tura yin aikin sulhu a yankin.

Sakataren kungiyar, Alhaji Ahmed Isa Karim, wanda ya bayyana hakan yayin tattaunawa da ’yan jarida a Jalingo ranar Asabar, ya ce lamarin abin takaici ne matuka kuma bai k**ata ya faru ba tun da farko.

Yayin da yake bayyana yadda abin ya faru, Ahmed ya ce, ko da yake bai goyi bayan harin kan jami’an tsaro ba, Fulani sun tilasta su kare kansu ne lokacin da sojoji s**a tsaya tare da ’yan kungiyar Bandawa suna kashe Fulani da shanunsu.

Ya kara da cewa ya k**ata sojoji su tsaya ne a tsakani don raba fada, kuma a ga suna nuna adalci maimakon goyon bayan kowane bangare.

“Kisan sojoji biyu abin bakin ciki ne matuka, kuma bai k**ata ya faru ba kwata-kwata. Duk da haka, yana da matukar muhimmanci a fayyace gaskiya. Sojoji sun tsaya tare da ’yan kungiyar Bandawa wadanda s**a kai hari kan makiyaya tun da safe, s**a kuma sha mamaki.

“Daga bisani, ’yan Bandawa s**a dawo da sojoji s**a ci gaba da kashe shanunmu da mutanenmu, har sai da mutanenmu s**a daina gudu s**a dauki fansa, wanda ya kai ga mutuwar sojojin biyu.

“A halin yanzu, sojoji suna tsare Fulani a yankin ba tare da bambanci ba, suna kuma kwace shanu suna kaisu idan s**a gani. Wannan ba daidai ba ne. Ba dukkan Fulani ne ’yan ta’adda ba ko kuma s**a yi hannun wajen kisan sojojin. Don haka wannan nuna wariya da ake yi wa al’ummarmu a yankin ba daidai ba ne ko kadan.

“Haka kuma, sun kwace shanu fiye da dubu guda da suke a harabar sakatariyar karamar hukumar yanzu. Ya k**ata a mika su ga mamallakinsu. Jiya ma sun je masallaci lokacin sallar Juma’a s**a k**a mutane. Me ya sa rundunar sojin Najeriya za ta sauka matakin da zai sa ta shiga wuraren ibada tana k**a mutane? Wannan abin kunya ne, kuma dole a yi tir da shi daga dukkan mai hankali.

“Muna kira ga hukumomin da abin ya shafa su gaggauta shiga tsakani don samar da mafita mai adalci, tare da mayar da shanu ga mamallakinsu. Daukar bangare a rikici ba zai kawo sulhu ba, sai dai kara dagula lamarin. Don haka muna sake kira ga sojin Najeriya da su kasance masu gaskiya wajen gudanar da aikin da yak**ata ya kasance na ’yan sanda da Civil Defence, wanda yanzu s**a karba kansu.”

Da yake tabbatar da lamarin a ranar Juma’a, mai magana da yawun ’yan sanda, James Leshen, ya ce an tura jami’an tsaro zuwa yankin don dawo da doka da oda.

“An aika jami’an tsaro zuwa yankin don shawo kan halin da ake ciki da kuma hana karin asarar rayuka,” in ji Leshen, yana mai cewa ana ci gaba da tantance adadin mutanen da abin ya shafa.

Shima Musa Garba, shugaban matasa a Karim-Lamido, ya bayyana kisan sojojin a matsayin “abin bakin cikin da ya nuna bukatar gwamnati ta dauki tsauraran matakai.”

“Mutanenmu sun gaji da yin gudu daga gidajensu. Muna bukatar mafita ta dindindin ga wannan kisan da babu ma’ana,” in ji shi.

Rikicin manoma da makiyaya ya ci gaba da zama babbar barazana ta tsaro a jihar Taraba, musamman a yankuna irin su Karim-Lamido, Lau, Wukari, Bali, da Gassol. Sabani kan amfani da kasa, wuraren kiwo, da samun ruwa na daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa rikicin.

Sai dai har yanzu rundunar sojin Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa ba kan lamarin, kodayake Laftanar Umar Mohamed, mai rikon kwarya na mai magana da yawun rundunar 6 Brigade, ya tabbatar da faruwar lamarin.

SOJOJIN ISRA’ILA SUN TAKARKARE GA RUWAN WUTA KAN GAZA GARISojojin Isra’ila sun matsa kaimi ga rowan wuta kan Gaza Gari g...
22/08/2025

SOJOJIN ISRA’ILA SUN TAKARKARE GA RUWAN WUTA KAN GAZA GARI

Sojojin Isra’ila sun matsa kaimi ga rowan wuta kan Gaza Gari gabanin shirin mamaye garin gaba daya.

Wannan sabon babin na farmakin da Isra’ila ke yi kan Hamas a Gaza tsawon wata 23 na da zummar wargaza abun da Isra’ila ke dauka tungar karshe ta Hamas.

Cikin shirin akwai gaiyato sojoji 60,000 da ke jiran kota-kwana don cimma wannan burin na gwamnatin firaminista Benjamin Netanyahu.

Jagoran sojojin na Isra’ila Eyal Zamir ya ce sojojin su na aiki a wajen Gaza gari kuma za a tura wasu sojojin ma su tarar da wadanda ke farmakin.

Ba mamaki Isra’ila na ganin za ta kwato sauran k**ammun Isra’ilawa da ke hannun Hamas da hakan zai ba da dammar mamaye dukkan Gaza.

Abu ne mawuyaci Hamas ta daina wannan yakin matukar akwai ko da gomman mayakan ta ne da su ka saura a Gaza ko wajen Zirin.

SHUGABA TINUBU YA NUFI BURAZIL DAGA JAPANShugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nufi kasar Burazil bayan kammala taruka ...
22/08/2025

SHUGABA TINUBU YA NUFI BURAZIL DAGA JAPAN

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nufi kasar Burazil bayan kammala taruka da halartar babban taron Tokyo na 9 na lamuran tattalin arzikin Afurka.

Kakakin shugaban Bayo Onanuga ya baiyana cewa shugaba Tinubu ya gudanar da zama na hulda tsakanin Japan da Najeriya kafin k**a hanyar Burazil inda zai dan dakata a Los Angeles din Amurka.

Shugaba Tinubu zai sauka a Brasilia babban birnin kasar Burazil a Amurka ta kudu don fara ziyarar aiki daga ranar 24 ga watan nan na Agusta.

Shugaban a wannan doguwar tafita na tare da tawaga da ta hada da ministan harkokin waje Yusuf Tuggar.

NAHCON TA BUKACI MASU YAYATA LABARU DA JAMA’A SU RIKA TAKATSANTSANHukumar alhazan Najeriya NAHCON ta bukaci masu yayata ...
22/08/2025

NAHCON TA BUKACI MASU YAYATA LABARU DA JAMA’A SU RIKA TAKATSANTSAN

Hukumar alhazan Najeriya NAHCON ta bukaci masu yayata labaru da sauran jama’ar kasa su rika takatsantsan da labarun da ba a tantance ba.

A ‘yan kwanakin nan mutane musamman a yanar gizo na yada labaru da ke nuna gudanar da bincike a hukumar daga hukumar yaki da cin hanci EFCC.

A nan NAHCON ta sanarwa daga jami’ar labarun hukumar Fatima Sanda Usara ta ce NAHCON a matsayin ta na hukumar gwamnati ta na aiki tare da dukkan hukumomin gwamnati ciki har da na yaki da cin hanci.

NAHCON kan maida hankali wajen tabbatar da kula da kare muradun maniyyata aikin hajji wajen gudanar da aikin cikin walwala da nasara.

Don haka NAHCON na ganin adalci shi ne a rika tabbatar da sahihancin labari da kuma fahimtar nauyin da ya rataya kan hukumar shi ne na kula da kare hakkokin maniyyata; kuma ba abun da za ta boye da ya shafi wani bincike don kofar ta a bude ta ke ga duk mai son karin haske kan wani labari.

21/08/2025

"Janar Buhari bai sake daukar waya ta ba tun ranar da Jonathan ya taya shi murnar lashe zabe a 2015" Inji Dr.Umar Ardo wanda ya yi ruwa da tsaki don tabbatar da marigayin ya sake takara a 2015 da ba da shawarar hada CPC da ACN. Ga zantawar sa da Hassan Maina Kaina a shirin KUKAN KURCIYA👇

20/08/2025

*MASU RUWA DA TSAKI NA CI GABA DA MAIDA MARTANI AKAN GAYYATAR WASU JAMI,AI NA HUKUMAR ALHAZAN NIGERIA DA HUKUMAR EFCC TAYI.*

Yanzu haka dai Hukumar yaki da Al,mundahana da dukiyar kasa a Nigeria ta gayyaci Wasu Manyan Jami,ai a Hukumar aikin hajji ta Nigeria wato NAHCON,domin suyi bayani akan Wasu Milyoyin Naira da tace an kashe ba,akan ka,ida ba.

Hukumar ta EFCC dai ta gayyaci wadan nan Jami,ai akan wadan nan kudade kimanin Naira Milyan 50 da tace an kashe su ba,a akan ka,ida ba.

Injiya Mustapha Imam Sitti Shine Babban Darakta na kungiyar Agaji JIBWIS a Nigeria Yace suna goyon bayan gudanar da Binciken Amma Kuma suna janyo hankali Hukumar ta EFCC da ta sanya Adakci acikin Binciken k**ar yadda yayi Karin bayani👇

Gwamnan Taraba ya mika dokoki uku na zartarwa ga Majalisar JihaGwamnan Jihar Taraba, Dokta Agbu Kefas, ya mika dokoki uk...
20/08/2025

Gwamnan Taraba ya mika dokoki uku na zartarwa ga Majalisar Jiha

Gwamnan Jihar Taraba, Dokta Agbu Kefas, ya mika dokoki uku na zartarwa ga Majalisar Dokokin Jihar domin a amince da su su zama doka.

Yayin da ya gabatar da dokokin a zaman majalisar, Kakakin majalisar, John Kizito Bonzena, ya jera su k**ar haka:

1. Dokar sake kafa Jami’ar Taraba, Jalingo, 2025

2. Dokar sake kafa Kwalejin Koyon Kimiyyar Nas, Jalingo, 2025

3. Dokar soke da sake kafa Hukumar Iyakokin Taraba, 2025

A cikin wasikar da ya aike wa majalisar, Gwamna Kefas ya jaddada cewa daya daga cikin manyan abubuwan da gwamnatinsa ta sa gaba shi ne farfado da hukumomi da tsare-tsaren gwamnati domin ingantacciyar ayyuka ga jama’a. Ya ce wannan na bukatar tushe na doka mai karfi wadda za ta zama ginshiki ga shirinsa na sauyi a jihar.

Gwamnan ya bayyana cewa yayin da wasu dokokin zartarwa aka tsara su domin gyara ko sake kafa tsofaffin dokoki, wasu kuma sabbin dokoki ne gaba ɗaya da za su zama jagora ga ayyukan gwamnati. Ya kara da cewa dokoki biyu na ilimi sun shafi ci gaba da gyare-gyaren da ake yi a bangaren manyan makarantu, yayin da dokar Hukumar Iyakoki za ta tabbatar da aiki bisa ka’idojin kasa da kasa.

Magatakardar majalisar, Salmuna Amos Sani, ya karanta dokokin karo na farko, inda daga bisani Kakakin ya tura su zuwa Kwamitin Ka’idoji da Hanyoyin Ayyuka domin ci gaba da nazari.

A halin da ake ciki, majalisar ta karɓi rahoton Kwamitin dindindin na Walwala, Matasa da Wasanni, bayan jin ra’ayoyin jama’a kan dokoki guda biyu: Dokar Hukumar Wasannin Taraba, 2025, da kuma Dokar Hukumar Ci gaban Matasa ta Taraba, 2025.

Yayin da ya gabatar da rahoton, Shugaban kwamitin, Hon. Anas Shaibu, ya ba da shawarar cewa ya k**ata majalisar gudanarwa ta hukumar wasanni ta kunshi sarakunan gargajiya da shugabannin addini. Haka kuma ya bada shawarar a rika koyar da darussa na musamman kan miyagun kwayoyi da haramun don kauce wa amfani da su a tsakanin matasan ‘yan wasa.

Kan Hukumar Ci gaban Matasa, Shaibu ya bayyana cewa an tsara ta ne domin hada-hadar shirye-shirye da manufofi da za su taimaka wajen bunkasa zamantakewa, tattalin arziki da ci gaban kai na matasa a fadin jihar.

Bayan tattaunawa a matsayin kwamitin gaba daya, majalisar ta amince baki ɗaya da rahoton kwamitin. Daga nan sai Kakakin ya tura shi zuwa Kwamitin Ka’idoji da Hanyoyin Ayyuka domin saka ranar da za a ci gaba da tattaunawa a kai.

20/08/2025

*WADANDA AMBALIYAR RUWA TA KWASHEMA GIDAJE A MOKWA SUNCE ANYI MASU WALA WALA WAJEN RABON KUDADEN TALLAFIN DA S**A SAMU.*

_Rahoton Mustapha Nasiru Batsari Daga Minna._

Yanzu haka dai Al,ummomin da Ambaliyar Ruwa ta sharewa Gidaje a Garin Mokwa ta Jihar Nejan Nigeria na ci gaba da kokawa akan rabon kudaden tallafin da S**a Samu Daga bangarori daban daban na kasar.

Rahotanni dai sun nuna cewa Babu wani magidanci da aka baiwa sama da Naira Milyan Daya a rabon kudaden duk da cewa kudaden da aka Samu sun haura Naira Bilyan Uku,Kuma Gidaje dari biyu da tamanin ne Ambaliyar ta kwashe.

Wani Magidanci da ya rasa gidansa a wannan Ambaliya ya tabbatar da cewa Naira Milyan Daya aka bashi Kuma akwai wadanda Naira Dubu Dari Biyar aka Basu...

Alokacin da na tuntubi Shugaban karamar Hukumar ta Mokwa Hon.Jibrin Muregi Yace bashi da wani cikakken bayani akan rabon kudaden domin kuwa bada Agaji Gaggawa ta Jihar Neja ce Tayi aikin rabon kudaden.

Akan haka na tuntubi Jami,in Hulda da Jama,a na Hukumar bada Agaji a Jihar Neja Alh.Husaini Ibrahim ga kuma bayanishi akan wannan Matsalar....

To acikin bayanin na Husaini ya Ambato mataimakin Gwamnan Neja Kwamred Yakubu Garba akan haka nayi kokarin samunshi Amma Labarin ya faskara.

20/08/2025

*ANA ZARGIN RUNDUNAR SOJIN RUWAN NIGERIA DA KIN DAUKAR MUSULMI A SABBIN SOJOJIN RUWA DA AKA DAUKA DAGA JIHAR KADUNA.*

_Rahoton Lamido Abubukar Sokoto daga Kaduna._

A jahar Kaduna masana na ci gaba da korafin yadda s**ace an nuna bangaranci na addini karara wajen daukar sababbin dalibai da zasu samu horo don zama sojan ruwa,

wanda s**ace hakan kuma ya sabawa ka,ida da kundin tsarin mulkin kasa inda s**a bukaci Mahukunta su duba lamarin.

k**ar dai yadda zakuji karin bayani daga bakin Lamido Abubakar Sokoto👇.

SHUGABAN KASA YA CIRE HARAJI KAN WAYAR SADARWARahoton Medina Dauda Nadabo Daga Abuja.Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinub...
20/08/2025

SHUGABAN KASA YA CIRE HARAJI KAN WAYAR SADARWA

Rahoton Medina Dauda Nadabo Daga Abuja.

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da soke harajin da aka dora wa ayyukan sadarwa ta wayar salula na kashi biyar cikin ɗari (5%) a cikin sabon tsarin haraji na ƙasar.

Wannan mataki na shugaban ƙasa, a cewar masu sharhi, na da nufin rage wa ‘yan Najeriya nauyin kuɗaɗen da suke biya wajen amfani da wayar salula da kuma intanet.

Harajin, wanda aka ƙaddamar a baya, ya janyo ƙorafi daga masana harkar sadarwa da kuma ƙungiyoyin kare muradun masu amfani da wayar hannu, inda s**a ce ya ƙara tsananta matsin tattalin arziƙi a kan jama’a.

Shugaba Tinubu ya ce gwamnatin sa ba za ta ɗora wa ‘yan ƙasa karin haraji da zai ƙara musu raɗaɗin rayuwa ba, musamman a wannan lokaci da ake ƙoƙarin gyara tattalin arziƙi da kuma rage hauhawar farashin kayayyaki.

Masu amfani da layukan wayar hannu da intanet a Najeriya na sa ran matakin zai kawo sauƙi a kuɗin kira da amfani da bayanai ta intanet wato data.

Address

No 32 Dennis Osadebey Apo Legislative Quarters
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when VOA Hausa Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share