ATS Hausa

ATS Hausa ATS Hausa (Advanced Telecommunications System) Sahihiyar Kafar yada labarai ta zamani.

Muna kawo muku labarai da dumi-duminsu da bidiyo da shirye shiryen sauti daga ko'ina a fadin Duniya.

Jami'an tsaron Turkiyya sun cafke mutum 209 da ake zargi da alaƙa da ƙungiyar ISIS da kuma wasu ƙungiyoyin masu ra'ayin ...
23/06/2026

Jami'an tsaron Turkiyya sun cafke mutum 209 da ake zargi da alaƙa da ƙungiyar ISIS da kuma wasu ƙungiyoyin masu ra'ayin ƙin jari-hujja na tsattsauran ra'ayi a jerin samame da aka kai a birnin Ankara, gabanin taron ƙasashen NATO da za a gudanar a watan Yuli.

A cewar hukumomi, an bayar da umarnin cafke mutane 241, yayin da jami'an tsaro s**a samu nasarar k**a 209 daga cikinsu, sannan ake ci gaba da neman sauran da ba a k**a ba.

Gwamnatin Recep Tayyip Erdoğan ta ƙara tsaurara matakan tsaro domin taron NATO da za a yi a Ankara a ranakun 7 zuwa 8 ga watan Yuli, inda ake sa ran shugabannin ƙasashe 32 mambobin ƙungiyar za su halarta.

Matakan tsaron sun haɗa da hana wasu taruka, takaita zirga-zirgar ababen hawa a wasu yankuna da kuma ƙara yawan jami'an tsaro a wuraren da za a gudanar da taron.

Turkiyya na ci gaba da gudanar da hare-haren tsaro kan ISIS tun bayan jerin hare-haren ta'addanci da ƙungiyar ta kai a ƙasar cikin shekaru da s**a gabata, ciki har da harin da aka kai a wani gidan rawa a birnin Istanbul a shekarar 2017 wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 39.

Wasu sakonnin da ake yadawa a shafukan sada zumunta sun ce an k**a "fiye da mutum 200 masu alaƙa da ISIS". Wannan ba cikakken bayani ba ne, domin hukumomi sun ce wasu daga cikin waɗanda aka k**a ana zarginsu da alaƙa da ƙungiyoyin masu ra'ayin tsattsauran ra'ayi na hagu, ba ISIS kaɗai ba.

ATS Hausa

Mutanen da s**a kamu da Ebola sun haura 1,000 a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo, yayin da adadin waɗanda s**a mutu ya ka...
23/06/2026

Mutanen da s**a kamu da Ebola sun haura 1,000 a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo, yayin da adadin waɗanda s**a mutu ya kai 267.

Adadin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ya haura 1,000, yayin da adadin mace-macen ya kai 267, a cewar hukumomin lafiya na ƙasar.

Ma'aikatar Lafiya ta ƙasar ta ce tun bayan ayyana barkewar cutar a ranar 15 ga Mayu, an tabbatar da kamuwa da cutar ga mutum 1,003, yayin da mutum 100 s**a warke, sannan akalla mutum 365 ke kwance a asibiti ko kuma a cibiyoyin killace marasa lafiya.

An bayyana cewa barkewar cutar ta samo asali ne daga nau'in kwayar cutar Ebola mai suna Bundibugyo, wanda har yanzu babu ingantaccen rigakafi ko tak**aiman maganin da aka amince da shi.

Hukumomi sun ce babban ƙalubalen da suke fuskanta shi ne gano da bibiyar mutanen da s**a yi hulɗa da masu ɗauke da cutar, inda s**a samu nasarar bibiyar kusan kashi 55% kacal na waɗanda ake zargin sun yi mu'amala da marasa lafiyar.

Rikice-rikicen tsaro da hare-haren mayaƙan Allied Democratic Forces a yankin Ituri sun kuma hana jami'an lafiya isa wasu ƙauyuka, lamarin da ke ƙara wahalar daƙile yaɗuwar cutar.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce barkewar cutar na faruwa ne a yanayi mai cike da ƙalubale, ciki har da rashin tsaro, yawan ƙaura da cunkoson jama'a, kuma tana ci gaba da tallafa wa ƙasashen Kongo da Uganda wajen sa ido, gano masu ɗauke da cutar da kuma wayar da kan al'umma.

Sabuntawa: Rahoton da aka fitar ranar Litinin ya nuna cewa adadin ya ƙaru zuwa mutum 1,048 da aka tabbatar sun kamu, yayin da adadin mace-mace ya kai 267.

ATS Hausa

Sojojin Myanmar sun kashe fiye da fararen hulla 700 a cikin wata shidda - In ji MDDMajalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta ce s...
23/06/2026

Sojojin Myanmar sun kashe fiye da fararen hulla 700 a cikin wata shidda - In ji MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta ce sojojin Myanmar ne ke da alhakin mutuwar fararen hula sama da 700 a cikin watanni shida da s**a gabata yayin gudanar da zaɓen ƙasar.

Wani sabon rahoto da ofishin kare haƙƙin ɗan Adam na MDD ya fitar ya nuna cewa daga watan Agustan shekarar da ta gabata, lokacin da gwamnatin sojin ƙasar ta sanar da shirin gudanar da zaɓe, zuwa ƙarshen watan Janairu, an tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 702.

Rahoton ya ce daga cikin waɗanda aka kashe, mata 224 ne, yayin da yara 153 s**a rasa rayukansu. Haka kuma, hare-haren sama ne s**a kasance babban abin da ya janyo asarar rayuka da lalacewar dukiyoyi.

MDD ta bayyana cewa aƙalla fararen hula 505 ne aka kashe ta hanyar hare-haren jiragen yaƙi, jiragen marasa matuƙa, da wasu ƙananan jiragen sama da sojoji ke amfani da su.

Mai magana da yawun ofishin kare haƙƙin ɗan Adam na MDD, Ravina Shamdasani, ta ce dukkan mutanen 702 da aka tabbatar da mutuwarsu an danganta su da ayyukan sojojin Myanmar, duk da cewa akwai yiwuwar wasu ƙungiyoyin masu ɗauke da mak**ai ma sun haddasa asarar rayuka.

Rikicin yaƙin basasa ya ƙara tsananta a Myanmar tun bayan juyin mulkin da sojoji s**a yi a shekarar 2021, wanda ya hambarar da gwamnatin farar hula ta Aung San Suu Kyi.

MDD ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya da su dakatar da samar wa Myanmar mak**ai, man jiragen sama da sauran kayayyakin da za su iya taimaka wa sojojin ƙasar wajen cigaba da take haƙƙin ɗan Adam.

ATS Hausa

Jami’an tsaron Najeriya sun k**a wasu mak**ai da ake shirin kai wa Ƴan Ta’adda a KogiATS Hausa
23/06/2026

Jami’an tsaron Najeriya sun k**a wasu mak**ai da ake shirin kai wa Ƴan Ta’adda a Kogi

ATS Hausa

"Yara manyan gobe" in ji Malan Bahaushe, sai dai wata ziyara a Sansanonin ‘Yan Gudun Hijira ta nuna akasin hakan:Ku biyo...
23/06/2026

"Yara manyan gobe" in ji Malan Bahaushe, sai dai wata ziyara a Sansanonin ‘Yan Gudun Hijira ta nuna akasin hakan:

Ku biyomu ku ji dalili!

Ilimi da Rawar da Al’umma Za Ta Taka ga rayuwar Yara 'ƴan gudun hijira dake Gararamba a Birnin Sokoto - Daga Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Sokoto, Usman Mohammed Binji

A yayin da na kai ziyarar aiki da dama a matsayina na ɗan jarida zuwa sansanonin ‘yan gudun hijira (IDPs) da ke cikin birnin Sokoto, musamman sansanonin Ramin Kura da Guiwa Eka, na lura da wani yanayi mai matuƙar tayar da hankali da raɗaɗi.

Duk da irin tallafin jin ƙai da ake bayarwa a waɗannan sansanoni, akwai wata babbar matsala da ba'a cika lura da ita ba, wadda ke shafar yara kanana da rikice-rikice s**a rutsa da su.

Abin da ya fi tayar min da hankali shi ne yadda na tarar da ɗimbin yara maza da mata masu shekarun zuwa makaranta amma ba sa halartar kowace irin makaranta.

Wasu ba sa zuwa makarantun boko, haka kuma ba sa samun ilimin addinin Musulunci. Saboda rashin tsari na ilimi, waɗannan yara suna zaman banza a cikin sansanonin, suna gararamba ba tare da wata manufa ko alkibla ba, ba samun kulawa ko abin da zai amfane su.

Abin da ya fi ɗaga hankali kuma shi ne ganin wasu daga cikin waɗannan ƙananan yara suna yawo a tituna da unguwannin da ke kewaye da sansanonin suna neman abinci ta hanyar barace barace.

Yaran da ya k**ata ace suna cikin ajujuwa suna karatu, ko wasanni da kuma shiryawa makomarsu dake tafe, a maimakon haka suna shafe kwanakin su suna bara domin kawai su rayu.

Ganin waɗannan yara marasa laifi suna miƙa hannayensu domin neman sadaka abu ne mai matuƙar raɗaɗi da bakin ciki. Wannan ba wai kawai yana nuna irin wahalhalun da s**a fuskanta ba ne, har ma yana nuna yadda suke rasa ƙuruciyarsu da mutuncinsu da kuma gurinsu na rayuwa.

Yayin da nake zagayawa a sansanonin tare da tattaunawa da mazauna wuraren, na kasa daina tunanin irin makomar da ke jiran waɗannan yara idan ba'a ɗauki matakin gaggawa ba. Kowace rana da yaro ya shafe ba tare da zuwa makaranta ba, rana ce da ta salwanta ko zata iya haifar da cigabansa.

Duk yaron da aka bari ba tare da kulawa da jagoranci ba, zai fi kasancewa cikin haɗarin faɗawa tarkon cin zarafi, ko cikin yaran bata gari da zasu koya masa munanan dabi'u da zasu yi tasiri a rayuwarsa.

Bisa ga abin da na gani, wannan matsala ta wuce batun rashin abinci ko matsuguni ko wasu buƙatu na yau da kullum. Matsalar tana nuna akwai babban gibi a tsarin ilimi da tarbiyya a cikin sansanonin Ramin Kura da Guiwa.

Duk da cewa ana cigaba da samar da agajin gaggawa to makomar ilimin waɗannan yara da s**a rasa muhallansu na cikin rashin tabbas.

Rashin kula da iliminsu tabbas zai jefa su cikin wani hali, saboda tasirin rikice-rikice s**a haifar da kuma wasu matsalolin zamantakewa da ka iya haifar da mummunan tasiri na dogon lokaci.

Saboda haka, na yi imanin cewa ƙungiyoyin al’umma, musamman ƙungiyoyin addinin Musulunci, suna da muhimmiyar gudummawa da zasu bada wajen taimakawa da cike gibin da ke akwai tare da gwamnati, maimakon jiran gwamnati kaɗai ta magance wannan ƙalubale.

Matsalar ta wuce misali kuma ta yi girman da ta wuce a bar ta a hannun hukumomin gwamnati kaɗai.

Addinin Musulunci ya ba da muhimmanci matuƙa ga neman ilimi, tausayi da kula da marasa ƙarfi, musamman yara, don haka bai k**ata waɗannan ƙa’idoji su tsaya a matsayin magana kawai ba, dole ne a gansu a aikace.

Ƙungiyoyin Musulunci da Malamai da ƙungiyoyin agaji za su iya taimakawa wajen kafa cibiyoyin koyo a cikin sansanonin ‘yan gudun hijira, inda yara za su samu ilimin boko na asali tare da ilimin addini da tarbiyya.

Haka kuma, Malamai masu aikin sa kai da masu ilimantar da al’umma za su iya koyar da karatu da rubutu, ilimin Alƙur’ani, ba da shawarwari da kuma sauya tunani da zamantakewa domin dawo da hankali yaran tare da ƙara musu ƙwarin gwiwa ko.

Al’umma baki ɗaya ma tana da babban nauyi a kanta. Attajirai, masu hannu da shuni, ƙungiyoyin ƙwararru da shugabannin al’umma za su iya tallafa wa shirye-shiryen ilimi ta hanyar bayar da gudummawa, kayan koyarwa, tallafin karatu da kuma ayyukan sa kai. Komi ƙanƙantar gudummawa tana da tasiri, tana iya kawo babban sauyi a rayuwar waɗannan yara.

Daga abin da na gani a sansanonin Ramin Kura da Guiwa Eka, waɗannan yara ba wai sun rasa matsugunansu kawai ba ne, da dama daga cikinsu suna tafiyar da rayuwarsu ba tare da tsari, jagoranci ko kariya ba. Wannan yanayi ya k**ata ya dami kowane ɗan Najeriya.

Idan muka kasa ɗaukar mataki a yau, muna cikin haɗarin samar da wata al’umma da aka hana ilimi da damar da za ta taimaka musu su zama ‘yan ƙasa masu amfani ga al’umma.

Saboda haka, ya zama wajibi ga ƙungiyoyin al’umma, ƙungiyoyin addinin Musulunci da duk masu kishin ƙasa su ɗauki matakin farko, su yi aiki tare da gwamnati da hukumomin agaji domin magance wannan ƙalubale.

Ta haka ne za a iya dawo da mutunci da kyakkyawar makoma ga rayuwar yaran da rikice-rikice s**a shafa a jihar Sokoto.

Waɗannan yara ba su cancanci rayuwa ta tsira da rai kawai ba. Sun cancanci ilimi. Sun cancanci kariya. Fiye da komai, sun cancanci makoma mai cike da damarmaki da manufa da kuma fata nagari.

ATS Hausa na tunatar da sakkwatawa cewa, "Kukan kurciya ma jawabi ne" mu tabbatar mu hada hannu mun samarwa yaran nan makoma ta gari kafin dare yayi mana hausawa s**a ce idan kunne yaji gangar jiki ta tsira.

An yi jana'izar Sojojin Najeriya 3 da s**a rasa rayukansu bayan motarsu da taka Nakiya a yankin Isa dake Gabascin Sokoto...
22/06/2026

An yi jana'izar Sojojin Najeriya 3 da s**a rasa rayukansu bayan motarsu da taka Nakiya a yankin Isa dake Gabascin Sokoto

Mataimakin Gwamnan jihar Sokoto Alhaji Idris Mohammed Gobir ne ya wakilci Gwamna Ahmed Aliyu wajen jana'izar da aka gudanar da yammacin ranar Litinin 22 Yunin 2026.

ATS Hausa

22/06/2026

Labarun Yamma Tare da Amamatu Abubakar Daga AST Hausa 22-06-2026

Ɗaukar tsauraran Matakai akan Matsalar Tsaro ne mafita ga inganta tattalin arzikin Najeriya – Orji Uzor KaluTsohon gwamn...
22/06/2026

Ɗaukar tsauraran Matakai akan Matsalar Tsaro ne mafita ga inganta tattalin arzikin Najeriya – Orji Uzor Kalu

Tsohon gwamnan jihar Abia kuma Sanata, Orji Uzor Kalu, ya ce ɗaukar matakan da zasu inganta harkokin tsaro shi ne babban ginshiƙin da zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin Najeriya.

Kalu ya bayyana hakan ne yayin da yake bankwana da Gwamna Ahmed Aliyu Sokoto, bayan kammala wata ziyarar ƙaddamar ayukka da ya kawo a jihar Sokoto, a wani bangare na cikar Gwamnatin APC shekaru 3.

A ziyarar ta Sanata Orji ya ƙaddamar da tituna guda 10 da gwamnatin Sokoto ta shinfida a Arkilla dake ƙaramar Hukumar Wamakko.

Ya ce matsalar rashin tsaro da ake fuskanta a sassa daban-daban na ƙasar Najeriya na cigaba da zama babban ƙalubale ga ƙoƙarin da ake yi na gina tattalin arziki mai ƙarfi wanda zai inganta rayuwar al'umma.

Sanatan ya yi kira da a ɗauki tsauraran matakai domin magance matsalolin tsaro, yana mai cewa hakan ne zai samar da cigaba mai ɗorewa a fannin tattalin arziki.

Kalu ya kuma yabawa Bola Ahmed Tinubu kan matakan da gwamnatinsa ke ɗauka wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar, yana mai cewa ana samun cigaba a matakin manyan manufofin tattalin arziki.

ATS Hausa

22/06/2026

Rahotanni sun tabbatar da cewa sama da jama'an lafiya 70 sun harbu da cutar Ebola a Congo yayin da 17 daga cikinsu s**a rigamu gidan gaskiya.

22/06/2026

Rashin Shugabanci Nagari a Najeriya ne Yasa Matsalolin Tsaro s**a ta'azzara — Malam Murtala Bello Da'a

Malam Murtala Bello Da'a ya bayyana cewa rashin shugabanci nagari da gazawar hukumomi wajen aiwatar da manufofin cigaba ne s**a kasance manyan abubuwan da s**a janyo tabarbarewar matsalar tsaro a Najeriya.

Ya zargi Gwamnatin tarayya da Tinubu ke jagoranta da Gwamnonin Najeriya da kasawa karara.

ATS Hausa

Address

Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ATS Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share