Zuma Times Hausa

Zuma Times Hausa Burin mu sanar da ku 'yancin ku.
(4)

Ko Kun San An Saki Wannan Mata, Matsafiya Da Aka K**a Ta A Jiya Saboda An Same Ta Da Yaran Hausawa A Matsafanta A Suleja...
08/06/2026

Ko Kun San An Saki Wannan Mata, Matsafiya Da Aka K**a Ta A Jiya Saboda An Same Ta Da Yaran Hausawa A Matsafanta A Suleja?

Shugaban Kungiyar Inganta rayuwar Mazauna Suleja, watau Suleja Ina Muka Dosa ya sanar wa Zuma Times Hausa cewa suna kan binciken gano wadanda s**a sa hukumar tsaro s**a sake ta.

Tunda farko 'ya'yan kungiyar sun nuna fargabarsu na yin adalci akan wannan matar ganin yadda ake zargin cewa manyan mutane da dama ke zuwa wajenta neman taimako da daddare.

Suleja na daya daga cikin garuruwan Arewa da kananan yara ke yawan salwanta.

CBN ya umarci bankuna su riƙa bibiyar dalilin yadda kwastomomi ke tura kuɗaɗe daga asusun kuɗaɗen wajen su, ko su fuskan...
08/06/2026

CBN ya umarci bankuna su riƙa bibiyar dalilin yadda kwastomomi ke tura kuɗaɗe daga asusun kuɗaɗen wajen su, ko su fuskanci tarar naira miliyan 100

Daga Ashafa Murnai Barkiya

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya umarci bankuna da su ci gaba da sa-ido tare da rubuta dalilin duk wata mu’amalar taransifa ko canja kuɗaɗen ƙasashen waje daga asusun da kowane kwastoman su ke ajiye kuɗaɗen waje.

Sannan kuma CBN na mai gargaɗin cewa rashin bin wannan umarni na iya jawo hukuncin tarar har naira miliyan 100 kan bankin da ya yi sakaci wajen ƙin bibiyar.

Wannan ƙarin haske ya biyo bayan matakin CBN na soke buƙatar masu asusun ajiyar kuɗaɗen waje na yau da kullum, tare da umarnin su cike 'Form A' kafin su tura kuɗaɗen ƙasashen waje daga asusun su.

A cikin ƙa’idojin da ke cikin bugu na huɗu na Kundin Dokokin Kasuwancin Musayar Kuɗaɗen Ƙasashen Waje, wanda a Turance ake kira 'Foreign Exchange Manual', CBN ya bayyana cewa masu asusun kuɗaɗen waje na yau da kullum suna da ’yancin amfani da kuɗaɗen da ke cikin asusun su domin halastattun mu’amaloli, ba tare da buƙatar 'Form A ba'.

Sai dai kuma, bankin ya jaddada cewa dole ne bankuna su rubuta dalilin kowace mu’amala tare da sanya ta a madaidaicin rukuni a ƙarƙashin Kundin Lambobin Tsarin Gudanar da Musayar Kuɗaɗen Ƙasashen Waje, wato 'Foreign Exchange Management System' (FEMS Code Book).

Ana sa ran wannan mataki zai sauƙaƙa wa kwastomomi canja kuɗaɗen ƙasashen waje daga asusun su na ajiyar kuɗaɗen waje, tare da tabbatar da cewa masu sa-ido kan harkokin kuɗi za su ci gaba da bibiyar yadda kuɗaɗen ƙasashen waje ke gudana a cikin tsarin dokokin Nijeriya.

A ƙarƙashin waɗannan ƙa’idoji, masu asusun za su iya cire kuɗi ko biyan kuɗaɗe ta hanyar tsabar kuɗi, canjin kuɗi ta waya da sauran hanyoyin da aka amince da su.

Haka nan CBN ya kuma amince wa kwastomomi su yi amfani da tsabar kuɗin su na ƙasashen waje da ke cikin asusun su, har zuwa adadin dala 10,000 a rana, ko makamancin sa a wasu kuɗaɗen ƙasashen waje, domin yin canjin kuɗi ta waya, matuƙar bankuna sun gabatar da rahotannin da ke bayyana dalilin waɗannan mu’amaloli.

Babban bankin ya kuma bayyana cewa mutanen da ke buɗe ko sanya kuɗaɗe a asusun ajiyar kuɗaɗen wajen su, ba lallai ne su bayyana tushen kuɗaɗen ƙasashen wajen da s**a ajiye ba. Duk da haka, dole ne dukkan mu’amalolin su kasance cikin bin dokokin yaƙi da halatta kuɗaɗen haram da kuma hana ɗaukar nauyin ayyukan ta’addanci.

Wannan sabon ƙarfafa matakin tattara bayanai wani ɓangare ne na ƙoƙarin CBN na ƙara ƙarfafa sa-ido kan kasuwar musayar kuɗaɗen ƙasashen waje ta Nijeriya tare da inganta bin doka da oda a tsakanin cibiyoyin kuɗi.

Bisa ga ƙa’idojin, duk wani bankin da aka ba izinin gudanar da harkokin musayar kuɗaɗen ƙasashen waje da ya aiwatar da wata mu’amala ba tare da cikakkun takardun shaida ba, zai iya fuskantar hukunci mai tsauri.

Kundin dokokin ya tanadi tarar naira miliyan 100 saboda gazawar samar da takardun da ake buƙata, baya ga tarar naira miliyan 10 kan kowace mu’amala da aka gano ta karya ƙa’idojin.

Masu fitar da kaya zuwa ƙasashen waje za su ci gaba da samun cikakkiyar damar amfani da kuɗaɗen da ke cikin asusun ajiyar kuɗaɗen wajen su, domin halattattun mu’amaloli. Sai dai idan aka canja kuɗaɗen zuwa wani mutum ko kamfani na uku, dole ne bankuna su tabbatar da cewa an rubuta dalilin mu’amalar yadda ya kamata tare da sanya ta ƙarƙashin lambar amfani da ta dace.

Masana harkokin kuɗi sun bayyana cewa wannan sabon umarni na nuna ƙoƙarin CBN wajen daidaita tsakanin sauƙaƙa samun damar amfani da kuɗaɗen ƙasashen waje da kuma tabbatar da gaskiya da bayyana gaskiya a kasuwar musayar kuɗi.

08/06/2026

Alhamdullillah ! Karshen 'Yan t@'adda da masu taimakawa masu ya zo karshe a Najeriya In Shaa Allah !

Kasaurara zuwa karshen video nan kuji abunda Sheikh Imam Habibi Assufiyyu ya bayyana, wanda shine Shugaban Kungiyar Malamai Masana ilimin Taurari na Najeriya.

Ku yada wannan sako domin kowa ya ji matakin da za'a dauka.

Dan Allah kuma dan Muhammadur Rasulullah (SAW), ku yada wannan sako .

Allah Ya sa mudace.

Labari Cikin Hoto:Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) kuma Gwam...
07/06/2026

Labari Cikin Hoto:

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima; Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) kuma Gwamnan Jihar Kwara, Malam AbdulRahman AbdulRazaq; Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris; tsohon Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Umar Ganduje, da Ministan Noma da Samar da Abinci, Sanata Abubakar Kyari, tare da sauran manyan baƙi suna daga cikin fitattun mutanen da s**a halarci sallar Juma’a ta musamman da aka gudanar domin bikin Ranar Dimokiraɗiyya ta bana. An gudanar da wannan zaman addu’a ne a ranar Juma’a, 5 ga Yuni, 2026, a Masallacin Ƙasa da ke Abuja.

"Abin da ke bani mamaki kullum Abubakar Rimi ke shiga kafafen yada labarai yana s**a ta, amma kuma kullum da safe shi ke...
07/06/2026

"Abin da ke bani mamaki kullum Abubakar Rimi ke shiga kafafen yada labarai yana s**a ta, amma kuma kullum da safe shi ke kira na ya fara gaishe ni, har ma na saba idan naga kira da safe nasan shi ne" - Shehu Shagari

Ummi Ibro Ta Yi AureUmmi Ibro Allah Ya sanya alkairi.An sha raɗe-raɗin cewa ƴar gidan marigayi Rabilu Musa Ibro ce, amma...
07/06/2026

Ummi Ibro Ta Yi Aure

Ummi Ibro Allah Ya sanya alkairi.
An sha raɗe-raɗin cewa ƴar gidan marigayi Rabilu Musa Ibro ce, amma a zahiri ba haka ba ne. Alaƙar aiki ce ta hada ta da shi, kuma yayi mata halacci, shiyasa a lokacin da ake kiranta da Ummin Ibro, ba ta hana ba ko don shi ya ji dadi. Har Allah Ya dauki ransa.
Duk da cewa Ni ne mutum na farko da na fara ba ta gudunmawar zama jaruma saboda na fahimci ta na da son Addini, har tsokanar ta na ke yi in ce mata "Mayyar Sallah" saboda Allah ne shaida ban taba ganin Ummi ta yi Sallah ba a kan lokaci ba. Kuma ta san halacci, shi ya sa na ke ce mata 'Yar halak ɗina. Ta jima ta na son yin aure, amma saboda jinyar mahaifiyarta, auren ya na ba ta barazana har kuma Allah Ya ɗauki ran Mahaifiyar, sai yanzu Allah Ya kawo lokaci.

Muna yi mata addu'ar Allah Ya sa albarka a aurenta.

Ali Rabiu Ali Daddy

Rahma Sa'idu Ta Fito Da Sabbin Hotuna Masu Ɗaukar Hankali
07/06/2026

Rahma Sa'idu Ta Fito Da Sabbin Hotuna Masu Ɗaukar Hankali

An K**a Wata Matsafiya Da Yaran Hausawa A Garin SulejaWadannan yara guda uku dukkannin su yaran Musulmi ne kuma suna jin...
07/06/2026

An K**a Wata Matsafiya Da Yaran Hausawa A Garin Suleja

Wadannan yara guda uku dukkannin su yaran Musulmi ne kuma suna jin Hausa amma wata da ake zargin matsafiya ce ta canza masu sunaye.

Alhamdulillah a yanzun haka tana hannun Hukuma.

Majiyarmu ta Suleja Ina Muka Dosa ta ce, wannan mata tana zaune ne a gidan ta da ke kallon Asibitin Dr Hussaini DHA Hospital Suleja.

Sun yi rokon Allah Ya kara tona asirin ire-iren su tare da bai wa Hukuma ikon yin adalci.

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN:Allah Ya yi wa Hajiya Salma Hassan rasuwa, ƴa ga ɗan majalissar tarayya na Birniwa/G...
07/06/2026

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN:
Allah Ya yi wa Hajiya Salma Hassan rasuwa, ƴa ga ɗan majalissar tarayya na Birniwa/Guri/Kirikasamma, da ke Jihar Jigawa, Abubakar Hassan Fulata.

Ta rasu a daren ranar Asabar, inda ta bar mijinta, Salim, da kuma ƴarsu guda ɗaya.

A cewar sanarwar da iyalanta s**a fitar, an gudanar da sallar jana’izarta da misalin ƙarfe 1:30 na rana a yau Lahadi, a Uthman Bin Affan Mosque, da ke kusa da Banex Plaza a kan titin Aminu Kano Crescent, Wuse 2, Abuja.

Arewa Mu Farka‎Bari ku ji abinda ya faru a Jihar Oyo. Gwamnan jihar Oyo wato Seyi Makinde ya tura tawagar sa zuwa wurin ...
07/06/2026

Arewa Mu Farka

‎Bari ku ji abinda ya faru a Jihar Oyo. Gwamnan jihar Oyo wato Seyi Makinde ya tura tawagar sa zuwa wurin iyayen yaran nan da aka sace don su jajanta musu sannan su kwantar musu da hankali a hukumance daga gidan gwamnati.

A lokacin da s**a je communityn da iyayen yaran nan suke, bayan sun gama bayanin abinda gwamnan ya turo su sai s**a fara sauƙe buhuhunan shinkafa daga mota da kuma tsabar kuɗi s**a ce Seyi Makinde ne ya ce a basu sannan su yi haƙuri kafin a karɓo musu yaran su.

Abinda zai ba ka mamaki, na rantse da Allah mutanen nan ƙin karɓa s**a yi. Yadda s**a zo da kayansu haka s**a koma da shi ko sisi ba wanda ya karɓa kaf cikin su. Ita kanta shinkafar da s**a sauƙe da kansu s**a sake ɗora ta a mota kamar yadda s**a zo da ita.

‎ Abinda kawai shugabansu ɗin ya ce, shine "kawai a dawo musu da yaransu gida ba sa buƙatar komai daga wurin gwamnati baya wannan."

Ba ku ganin da a Arewa ne wannan abun ya faru akwai tabbacin 100% sai al'ummar mu san karɓi wannan kayan.

Ba wani Hakimi, Bulama ko Mai unguwa da ya isa ya danne kwaɗayin sa ballantana ma yace a mayarwa da gwamnati kayanta.

Su kansu iyayen yaran sai ka samu wasunsu da har godiya ma sai sun yi kafin su karɓa saboda tsabar rashin sanin zafin kai da kishin kai.

‎Salisu Yakubu RN RNT

Address

Number 17B Sidi Plaza Behind Old NEPA Off Sulemanu Barau Road Suleja
Abuja
910101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zuma Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zuma Times Hausa:

Share