Zuma Times Hausa

Zuma Times Hausa Burin mu sanar da ku 'yancin ku.

Yanzu Yanzu: Shugaba Tinubu ya Zauna don tattaunawa da Majalisar Koli ta ƘasaShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a halin y...
09/10/2025

Yanzu Yanzu: Shugaba Tinubu ya Zauna don tattaunawa da Majalisar Koli ta Ƙasa

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a halin yanzu yana jagorantar zaman Majalisar Koli ta Ƙasa (Council of State) a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda ake sa ran zai gabatar da sunayen waɗanda zasu maye gurbin kujerar shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC). Zaman, wanda aka fara da misalin ƙarfe 1:29 na rana a yau Alhamis, ya zo ne kwana biyu bayan kammala wa’adin shekaru 10 na Farfesa Mahmood Yakubu a matsayin shugaban INEC, wanda ya ja ragamar shugabancin hukumar a ƙarƙashin gwamnatoci biyu tare da gudanar da manyan zaɓuɓɓuka uku.

Bisa ga jerin ajanda da aka gani kafin zaman ya koma na sirri, Shugaba Tinubu ya gabatar da sunayen mutane uku domin a tantance su, Farfesa Joash Amupitan, Mai Shari’a Abdullahi Mohammed Liman, da kuma Farfesa Lai Olurede. Waɗannan duka masana ne a fannin shari’a da ilimi, kuma za a zaɓi ɗayan su a matsayin wanda zai gaji Mahmood Yakubu domin shugabantar hukumar INEC.

Tsoffin Shugabannin Ƙasa, Janar Abdulsalami Abubakar (mai ritaya) da Janar Ibrahim Badamasi Babangida (mai ritaya), sun halarci zaman ta kafar bidiyo, yayin da ake jiran dakon shigowar tsofaffin shugabannin ƙasa, Olusegun Obasanjo da Goodluck Jonathan.

A cikin wadanda s**a halarci zaman a zahiri akwai Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima; Sakataren Gwamnatin Ƙasa, George Akume; Mai Ba da Shawara na Musamman kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu; Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN); da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila. Haka zalika, Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio; Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas; da gwamnonin jihohi da dama ko mataimakansu sun halarci taron. Ana sa ran Shugaba Tinubu zai yi jawabi kan tattalin arziki, tsaro da sauran al’amuran ƙasa kafin a mika sunayen da aka zaɓa ga Majalisar Dattawa domin tabbatarwa.

Labari a Hoto: Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, Ya Karɓi Baƙuncin Jakadan Ƙasar Argentina a Najeri...
09/10/2025

Labari a Hoto: Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, Ya Karɓi Baƙuncin Jakadan Ƙasar Argentina a Najeriya, Nicholas Perrazo Nao, a Ziyarar Ban-girma a Ofishinsa da Ke Abuja, a Jiya Laraba, Inda S**a Tattauna Kan Ƙarfafa Haɗin Gwiwar Ƙasashen Biyu Ta Hanyar Musayar Bayanai, Haɗin Gwiwar Kafofin Yaɗa Labarai da Al’adu

Gwamnatin Nijeriya Ta Ƙaryata Sanatan Amurkan Da Ya Yi Zargin Ana Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare DangiGwamnatin Tarayya ta s...
09/10/2025

Gwamnatin Nijeriya Ta Ƙaryata Sanatan Amurkan Da Ya Yi Zargin Ana Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Gwamnatin Tarayya ta sake ƙaryata zargin da wani Sanatan ƙasar Amurka wai shi Ted Cruz ya yi cewa wai ana yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Nijeriya.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya ƙaryata zargin a cikin wata hira ta musamman da Fox News Digital da ke Amurka ta wallafa a ranar Talata.

Ministan ya ce: “Gwamnatin Nijeriya ta ƙi amincewa da wannan zargi. Wannan ba gaskiya ba ne kwata-kwata.”

Yayin da yake mayar da martani kan alƙaluman da Sanata Cruz ya bayar, Idris ya ce: “Ba gaskiya ba ne. Wannan ba shi ne abin da ke faruwa ba. Ina nufin ba gaskiya ba ne a ce an ƙone fiye da coci 20,000. Kuma ƙarya ce a ce an kashe Kiristoci 52,000. Daga ina ya samo waɗannan alƙaluma? Ba shi da wata hujja ko shaidar da ya dogara da ita. Gwamnatin Nijeriya ta ƙi amincewa da wannan zargi.”

Ya kuma jaddada cewa babu wani jami’in gwamnati ko wata hukuma a Nijeriya da ke mara wa ‘yan ta’adda baya ko yin aiki tare da su don kai hari ga mabiya wani addini.

A cewar sa: “Babu wani jami’in gwamnati a Nijeriya da zai goyi bayan masu tayar da ƙayar baya don su kai hari ga mabiyan wani addini. Wannan zargi ƙarya ne ɗari bisa ɗari.”

Ministan ya sake tabbatar da cewa Nijeriya ƙasa ce mai yawan addinai da kuma zaman lafiya da juna, inda ya ce: “Nijeriya ƙasa ce da ke da mabiya addinai daban-daban. Muna da Kiristoci, muna da Musulmai, har da waɗanda ba sa bin waɗannan addinai biyu. Nijeriya ƙasa ce mai yarda da bambancin addinai. Gwamnatin Nijeriya ta ƙudiri aniyar tabbatar da cewa ana da ‘yancin yin addini a ƙasar nan.”

Ya ƙara da cewa matsalar ta’addanci ta shafi kowa, ba tare da la’akari da addini ba. Ya ce: “Abin baƙin ciki ne cewa waɗannan ‘yan ta’adda suna kashe Kiristoci da Musulmai a wurare daban-daban da suke samun goyon baya. Don haka, ba gaskiya ba ne. Gaba ɗaya ƙarya ce a ce wai ana da wani shiri ko ƙudiri na gangan don hallaka wata ƙungiyar addini; wannan ba daidai ba ne, abin takaici ne ƙwarai.”

Idris ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya tana da cikakken ƙudirin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa, inda ya jaddada cewa hukumomin tsaro na ƙasar nan ba su yi ƙasa a gwiwa ba a yaƙi da ta’addanci da fashi da makami a kowane salo.

ACF Ta Cimma Matsaya Kan Siyasa Da Watsa LabaraiHukumar Amintattu (BOT) ta Arewa Consultative Forum (ACF) a ranar Talata...
08/10/2025

ACF Ta Cimma Matsaya Kan Siyasa Da Watsa Labarai

Hukumar Amintattu (BOT) ta Arewa Consultative Forum (ACF) a ranar Talata, 7 ga Oktoba, 2025 ta cimma matsaya kan gabatar da sahihan ƙa’idojin sadarwa ga jami’anta domin ka ƙauce wa maganganun da ke cin karo da juna a bainar jama’a, tare da tabbatar da haɗin kai da manufa ɗaya a cikin ƙungiyar.

Shugaban hukumar, Alhaji Bashir M. Dalhatu, Wazirin Dutse, ne ya sanar da wannan mataki a wajen taron da aka gudanar a hedikwatar ACF da ke Kaduna.

Dalhatu ya bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne saboda wasu lamurra da s**a faru kwanan nan inda wasu jami’an ACF s**a yi maganganu masu karo da juna ga ‘yan jarida. Ya ƙara da cewa akwai takardar tsare-tsare da sakateriyar ƙungiyar ta shirya domin daidaita harkar sadarwa tsakanin mambobi.

Ya kuma sanar da cewa shirye-shirye suna kan gaba sosai domin bikin cika shekara 25 (Silver Jubilee) na ACF da za a gudanar daga 20 zuwa 22 ga watan Nuwamba, 2025.

Bikin zai haɗa da taron tara kuɗi domin gina sabon hedikwatar ƙasa, ƙaddamar da Asusun Tallafi (Endowment Fund) don bunƙasa harkokin zamantakewa da tattalin arziki, da kuma ƙaddamar da littafi da s**a ƙunshi tarihin ACF da nasarorinta.

Dalhatu ya sake jaddada cewa ACF za ta ci gaba da kasancewa wacce ba ta da ra’ayin siyasa, musamman yayin da ake shirye-shiryen zaɓen 2027.

Ya ƙara da cewa kodayake mambobi na iya shiga jam’iyyun siyasar da ya dace da ra'ayinsu, amma ACF za ta ci gaba da kasancewa ƙungiya mai ra’ayin zamantakewa da al’adu, ba ta siyasa ba.

Ya yi gargaɗi kan kafa ƙungiyoyi masu k**a da ACF a Arewa, yana mai cewa irin waɗannan rarrabuwar kai na rage ƙarfi da murya ɗaya ta yankin.

Ya roƙi waɗanda s**a kafa ƙungiyoyin rassa da su komawa cikin ACF domin ci gaba da aiki tare.

Dalhatu ya kuma yaba wa Sojojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro bisa jajircewarsu wajen yaƙi da ta’addanci da ‘yan fashi da makami, tare da yin addu’ar rahama ga waɗanda s**a rasa rayukansu yayin hidima.

Haka kuma ya yi tir da zargin yi wa Masana’antar Dangote (Dangote Refinery) zagon ƙasa, yana mai kiran hakan a matsayin aikin da ya sabawa muradin ƙasa, tare da kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki mataki cikin gaggawa domin kare ƙadarorin tattalin arzikin ƙasa.

Taron ya samu halartar mambobin BOT, shugabanni da sakatarorin jihohi, da kuma wakilan ƙungiyar Arewa 100% Focus Group.

CBN ya gindaya sabbin ƙa'idoji da sharuɗɗan amfani da P.O.SAshafa Murnai BarkiyaBabban Bankin Nijeriya (CBN) gindaya sab...
08/10/2025

CBN ya gindaya sabbin ƙa'idoji da sharuɗɗan amfani da P.O.S

Ashafa Murnai Barkiya

Babban Bankin Nijeriya (CBN) gindaya sabbin sharuɗɗa da ƙa'idojin amfani da P.O.S a hada-hadar kuɗaɗe ta yau da kullum.

Daga cikin sabbin ƙa'idojin, an gindaya cewa ba a yarda ejan masu tiransifa da P.O.S su zarce tiransifa ta sama da Naira miliyan 1 da dubu 200 ba (N1.2m) a duk P.O.S ɗaya a kowace rana.

Cikin wata sanarwa da CBN ya fitar a ranar Talata, ya ce an fito da sabbin sharuɗɗan domin tabbatar da sa-ido da kuma inganta tsarin hada-hadar kuɗaɗe.

Sanarwar wadda Daraktan Kula da Tsare-tsaren Biyan Kuɗaɗe, Musa Jimoh ya sa wa hannu, ya ce hakan zai sa tsarin hada-hadar kuɗaɗe na zamani ya kare kwastomomi sosai daga faɗawa tsilla-tsillar matsalolin yau da kullum da suke fuskanta a tsarin tiransifa ta P.O.S.

Ya ce kuma wajibi ne dukkan bankuna su riƙa bada rahotonannin hada-hadar kuɗaɗen da ejan-ejan ɗin su s**a yi da P.O.S, domin ƙarƙafa sa-ido a tsarin hada-hadar tare da inganta shi.

Yayin da sanarwar ta fara aiki nan take, ta kuma ƙara da cewa daga 1 ga Afrilu, 2026 za a tabbatar ana bada bayanan daidai wurin da kowane mai P.O.S ke zaune.

"Dukkan bankuna da masu ruwa da tsaki na cibiyoyin hada-hadar kuɗaɗe su tabbatar da cewa ana bin waɗannan sabbin sharuɗɗa waɗanda CBN ya gindaya."

A ƙarƙashin wannan sabon tsari, tilas ejan ya riƙa hada-hadar kuɗaɗe da P.O.S ta hanyar amfani da asusun banki da ya ware musamman domin hada-hadar ko kuma 'Asusun Tafi da Gidan Ka' na 'wallet' daga wata cibiyar hada-hadar kuɗaɗe ta zamani, domin tabbatar da samun sauƙin sa-ido da bibiyar abin da ke gudana.

CBN ya yi gargaɗin cewa wanda ya yi amfani da asusun da ba shi aka tantance masa ba, to shi wannan ejan ɗin ya karya ƙa'idar da tilas sai an hukunta shi.

Duk ejan ɗin da aka samu da laifin zamba, rashin bin ƙa'ida, ko wasu laifukan da dokar hada-hadar kuɗi ta haramta, to za a sa-ido a kan sa, kuma a soke yarjejeniyar da aka ƙulla da shi.

An kuma umarci cibiyoyin hada-hadar kuɗaɗe su buga sunayen dukkan ejan-ejan ɗin su a shafin su na intanet, tare da rubuta sunayen dukkan rassan da ejan-ejan ɗin ke ƙarƙashi.

Manyan ejan-ejan, wato 'Super Ejan' tilas ya kasance akwai aƙalla ejan guda 50 a ƙarƙashin kowane 'Babban Ejan', a faɗin shiyyoyin ƙasar nan shida. Yin hakan zai tabbatar da kowane lungu ya samu damar yin hada-hadar kuɗaɗe ta zamani kuma a sauƙaƙe.

Wasu daga cikin sharuɗɗan kuma sun haɗa da cewa: "An hana ejan mai amfani da na'urar P.O.S sauya wurin zama, matsawa nesa ya yi tirasifa ko rufe wurin hada-hadar sa ba tare da neman izni daga Babban Ejan ba.

"Duk ejan ɗin da zai canja wurin zama, tilas ya manna sanarwar yin haka a wurin da yake hada-hada, tun kwanaki 30 kafin zuwan ranar da zai canja wuri.

An kuma buƙaci cibiyoyi ko kamfanonin hada-hadar kuɗaɗe su fito da wani tsarin amfani da na'urorin da za su riƙa maida wa kwastoma kuɗaɗen sa, nan take idan aka cire, amma ba su je inda aka tura ba, bayan an rigaya an cire masa.

Tilas a riƙa ajiye rasiɗin aikawa ko cirar kuɗi mai ɗauke da sunan ejan ɗin da shiyyar da yake, har tsawon shekaru biyar.

CBN ya ce an fito da sabbin sharuɗɗan domin inganta tsarin hada-hadar kuɗaɗe, sa-ido tare da tabbatar da jama'a da dama na samun yin hada-hada cikin sauƙi a kowane lungu suke.

Kotu Za Ta Yanke Hukunci A Kan Kisan Hanifa Wata kotun ɗaukaka ƙara dake zamanta a sakatariyar Audu Bako a Kano, ta ce z...
07/10/2025

Kotu Za Ta Yanke Hukunci A Kan Kisan Hanifa

Wata kotun ɗaukaka ƙara dake zamanta a sakatariyar Audu Bako a Kano, ta ce za ta sanar da ranar da za ta yanke hukunci kan neman soke hukuncin kisa da aka yankewa Abdulmalik Tanko da Hashim Isiyaku.

Masu ƙara sun roƙi kotun da ta soke hukuncin kisa da Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke musu ta hanyar rataya, tare da sallamar su daga tuhumar.

Lauyan masu ƙara, Barista Attorney Eze Wike, ya nemi kotun da ta rushe hukuncin ƙasa gaba ɗaya tare da sallamar waɗanda ake ƙara.

Sai dai lauyan gwamnatin Jihar Kano, waɗanda ake ƙara, Barista Lamido Abba Sorondinki, ya yi s**a ga wannan buƙata, inda ya roƙi kotun da ta tabbatar da hukuncin kisa da babbar kotun Kano ta yanke.

Alkalan kotun uku da s**a saurari ƙarar – Justice Moses Ugo, Justice O. O. Goodluck, da Justice A. R. Mohammed – kuma sun bayyana cewa zasu sanar da ranar yanke hukunci a nan gaba.

Tun a shekarar 2022 Babbar Kotun Jihar Kano mai lamba 5 ta yanke musu hukuncin kisa bayan ta same su da laifin kashe Hanifa Abubakar, da ke unguwar Dakata a ƙaramar hukumar Nassarawa.

Mata Ku Rinƙa Kwanciya A Gefen MazajenkuDaga Mairo Muhammad MudiA ‘yan watannin da s**a gabata, wasu abubuwa masu ban ta...
07/10/2025

Mata Ku Rinƙa Kwanciya A Gefen Mazajenku

Daga Mairo Muhammad Mudi

A ‘yan watannin da s**a gabata, wasu abubuwa masu ban tausayi sun tilasta ni daukar alkalami domin yin magana da mata, musamman masu aure.

Mun rasa wasu mazaje nagari iyaye masu kauna, mazaje masu aiki tuƙuru, kuma ginshiƙan gidajensu. Amma abin da ya fi damuna shi ne yadda wasu daga cikinsu s**a rasu su ka mutu cikin kaɗaita, babu kowa a gefensu.

Labarinsu ya kan zama iri ɗaya. Namiji zai yi hira da abokai cikin farin ciki da dariya, daga bisani ya annashuwa, ya yi sallama ya koma gida ya kwanta. Da safe, idan bai bayyana a masallaci don sallar asuba ba, mutane sai su fara tambaya. In an tafi gidansa, an buga ƙofa, shiru. Sai matarsa ta shiga, ta tarar da shi ya riga mu gidan gaskiya a yayin da ya ke barci shi kaɗai.

Saleh ɗaya ne daga cikin irin waɗannan mazajen. Namiji ne mai son iyalinsa, mai sauke nauyin gidansa, kuma abin koyi ga maza. Ba wanda ya zaci yana da wata matsananciyar larura, sai ɗan ƙorafin ciwon olsa da yake yi lokaci zuwa lokaci. A daren da abin ya faru, ya gaya wa matansa cewa kirjin sa yana masa ciwo, ya ce zai kwanta. Bayan ya yi musu sallama, ya shiga ɗakinsa. Da safe, matar da ke da gurki amma tuni ta ƙaurace zuwa turakarsa ta je ta tashe shi don sallah, sai ta tarar da Saleh ya riga mu gidan gaskiya.

Wannan irin labari yana yawaita, kuma yana ɗaukar hankali.

Me yasa wasu mata ke fara nesanta kansu daga mazajensu da zarar shekaru sun ja? Me yasa suke zaɓar kwana daban, ɗaki daban, har rayuwa daban a gida ɗaya? Shin ba su gane cewa da zarar shekaru sun ja, shine lokacin da miji ya fi buƙatar kasancewarsu kusa da shi ba?

Iyayenmu mata da kakanni na iya yin shigowa da fita cikin sirri a lokacin da, amma yau zamani ya sauya. Mazajenmu suna fama da damuwa, kaɗaici, da cututtukan da ba a iya gani da ido. A irin wannan lokaci, kasancewar ki a kusa da shi tana zama magani.

Ya k**ata mu koya wa ‘ya’yanmu mata cewa kwanciya tare da miji ba alamar rauni ba ce, kuma ba son kai ba ne, alamar soyayya da haɗin kai ce. Ya k**ata mu gyara tunanin da wasu ke da shi cewa duk lokacin da aka ga mace a ɗakin mijinta, sai an ɗauka ta je yin wani abu ne da ake jin kunya.

Ku bari ‘ya’yanku su tashi suna ganin kauna da haɗin kai a tsakaninku. Wannan tunanin na iya gyara rayuwar su gaba ɗaya.

Mata, kada ku bar mazajenku su kwanta cikin kaɗaici. Ku zauna kusa da su. Ku saurare su. Ko da ba ku yi magana ba, kasancewarku tana nufin komai. Wani lokaci, kasancewar ki kusa da shi ce ke iya hana abin da ba a zata ba.

Soyayya ba sai da hayaniya ba wani lokaci cikin shiru, k**ar numfashin da k**e ji daga wanda kika yi alkawarin rayuwa tare da shi ka iya ba shi kwanciyar hankali da natsuwa.

Shugaba Tinubu ya ba da umarnin a rage kudin kujerar aikin Hajji na 2026Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarni ...
06/10/2025

Shugaba Tinubu ya ba da umarnin a rage kudin kujerar aikin Hajji na 2026

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarni ga hukumar kula da aikin Hajji ta ƙasa (NAHCON) da ta sake duba kudin kujerar aikin Hajji na shekara ta 2026 tare da rage shi, bisa ga ingantuwar darajar Naira a kasuwar musayar kudi.

A sak**akon wannan umarni, Mataimakin Shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya bai wa hukumar NAHCON wa’adin kwanaki biyu don fitar da sabon tsarin kudin kujerar aikin Hajji da zai dace da yanayin tattalin arzikin ƙasar.

Shettima ya bayyana hakan ne a fadar shugaban ƙasa, yayin taron da ya jagoranta tare da shugabannin NAHCON da wasu jami’an gwamnati, inda ya jaddada muhimmancin haɗin kai tsakanin jami’an jihohi da gwamnoni wajen tabbatar da sabon tsarin da ya dace.

Ya kuma bukaci hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta biyan kuɗaɗen da s**a wajaba da aika su ga Babban Bankin Najeriya (CBN) domin gudanar da aikin Hajji cikin nasara da tsari.

Da yake bayani ga manema labarai bayan taron, Mataimakin Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban ƙasa, Sanata Ibrahim Hadeija, ya ce manufar taron ita ce kammala shirye-shiryen aikin Hajji na 2026, musamman batun kudin kujeru.

Ya ce, “Tun da darajar Naira ta samu ƙaruwa a kasuwa saboda gyare-gyaren tattalin arzikin da gwamnatin Tinubu ke yi, dole ne hakan ya bayyana a cikin kudin aikin Hajji. Idan masu aikin Hajji sun biya Naira Miliyan 8.5 zuwa Naira Miliyan 8.6 a bara saboda raguwar darajar Naira, yanzu da ta inganta, dole ne su amfana da saukin kudin.”

Shi ma Sakataren NAHCON, Dr. Mustapha Mohammad, ya ce umarnin shugaban ƙasa zai ƙara yawan masu niyyar zuwa Hajji a bana.

A nasa bangaren, Shugaban Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi, kuma Mataimakin Shugaban Kungiyar Shugabannin Hukumar Alhazai ta Jihohi da birnin tarayya, Alhaji Faruk Aliyu Yaro, ya bayyana farin cikinsa da wannan mataki.

Ya ce, “Muna murna sosai da wannan mataki da shugaban ƙasa da mataimakinsa s**a ɗauka. Mun yi imanin hakan zai rage farashin kujerar Hajji kuma ya sauƙaƙa wa musulmi.”

Kotun majistare mai lanba 7 karkashin jagorancin mai shari'a Halima Wali, ta aike da dan Tiktok din nan Ashiru Mai wushi...
06/10/2025

Kotun majistare mai lanba 7 karkashin jagorancin mai shari'a Halima Wali, ta aike da dan Tiktok din nan Ashiru Mai wushirya zuwa Gidan gyaran hali bisa zarginsa da wallafa bidiyo da hotunan fitsara tare da Wadar da s**ai aikin.

SHUGABA TINUBU YA DAWO ABUJA BAYAN KAMMALA ZIYARAR AIKI A LAGOSShugaba Bola Ahmed Tinubu, ya dawo Abuja yau bayan shafe ...
06/10/2025

SHUGABA TINUBU YA DAWO ABUJA BAYAN KAMMALA ZIYARAR AIKI A LAGOS

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya dawo Abuja yau bayan shafe kwanaki goma na ziyarar aiki a jihar Lagos.

Shugaba Tinubu ya je Lagos a ranar Juma’a, 26 ga Satumba, bayan halartar bikin nadin sabon Olubadan na Ibadan, Mai Martaba Oba Rashidi Adewolu Ladoja. A yayin da yake Lagos, Shugaban Ƙasa ya gana da manyan ’yan kasuwa da masu zuba jari, ciki har da Shugaban Kamfanin Global Infrastructure Partners, Bayo Ogunlesi, da tsohon shugaban UBA da Etisalat, Keem Belo-Osagie, wanda yanzu ke shugabantar Metis Capital Partners.

Shugaba Tinubu ya kuma karɓi bakuncin Sakatare-Janar na Hukumar Kula da Harkokin Ruwa ta Duniya (IMO), Mista Arsenio Dominguez, tare da Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arzikin Ruwa, Adegboyega Oyetola, da shugabannin hukumomin da ke karkashin ma’aikatar. A yayin tattaunawar, Shugaban Ƙasa ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta harkokin ruwa a matsayin hanyar dena dogaro da man fetur.

A daren bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai, Shugaban Ƙasa ya ziyarci Jihar Imo, inda ya kaddamar da wasu ayyukan da Gwamna Hope Uzodimma ya aiwatar. Haka kuma, ya halarci taron kaddamar da littafin da Gwamnan ya rubuta kan tarihin shekaru goma na mulkin jam’iyyar APC a Najeriya.

A ranar bikin ’yancin kai, Shugaban Ƙasa ya gabatar da jawabin ƙasa kai tsaye daga fadar gwamnati ta Dodan Barracks. Daga bisani kuma, ya kaddamar da sabunta Gidan wasa na ƙasa (National Theatre), wanda yanzu aka sake masa suna zuwa Wole Soyinka Centre for Culture and the Creative Arts, inda ya yi kira ga ’yan ƙasa da su rika yin fata mai kyau game da Najeriya.

A ranar Asabar, 4 ga Oktoba, Shugaban Ƙasa ya ziyarci garin Jos, Jihar Filato, domin halartar jana’izar Mahaifiyar Farfesa Nantawe Yilwatda, Shugaban Jam’iyyar APC. A wajen jana’izar, Shugaba Tinubu ya yaba da rayuwa da jajircewar Marigayiya Mama Lydia Yilwatda, tare da tabbatar wa al’ummomin Kiristoci na Arewa cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tabbatar da adalci da daidaito tsakanin mabiya mabanbantan addinai a fadin ƙasa.

Wani Tsòhòñ Dañ Bøķõ Hàřªm Yà Kàshè Shi A Jihar Borno Saboda Ya Kì Ba Su Naira Dubu Daya Bayan Sun Tare Su A HanyaLamari...
06/10/2025

Wani Tsòhòñ Dañ Bøķõ Hàřªm Yà Kàshè Shi A Jihar Borno Saboda Ya Kì Ba Su Naira Dubu Daya Bayan Sun Tare Su A Hanya

Lamarin ya auke ne a hanyar Mafa a lokacin da marigayi Jidda suke dawowa daga yankin Gamborou Ngala.

Tuni dai tubabben dan tà'àďdañ ya shiga hannu, wanda shine a tube cikin wadannan hotunan.

Aliko Dangote ya fara gina kamfanin taki a habasha bayan na siminti.Ya kaddamar da gina kamfanin takin zamani na sama da...
06/10/2025

Aliko Dangote ya fara gina kamfanin taki a habasha bayan na siminti.

Ya kaddamar da gina kamfanin takin zamani na sama da Naira tiriliyan 3.

Address

Number 17B Sidi Plaza Behind Old NEPA Off Sulemanu Barau Road Suleja
Abuja
910101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zuma Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zuma Times Hausa:

Share