Zuma Times Hausa

  • Home
  • Zuma Times Hausa

Zuma Times Hausa Burin mu sanar da ku 'yancin ku.

Hamshakin Dan Kasuwa kuma Attajiri Abdulsamad Rabi'u, BUA Shima Yabi Sahun Sauran masoya masu tururuwar Zuwa Ta'aziya a ...
20/07/2025

Hamshakin Dan Kasuwa kuma Attajiri Abdulsamad Rabi'u, BUA Shima Yabi Sahun Sauran masoya masu tururuwar Zuwa Ta'aziya a Jihar Katsina.

Mai Kamfanin BUA, Ya Ziyarci Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Radda Domin Yi mashi Ta'aziyyar Marigayi tsohon Shugaban kasar Nigeria Muhammad Buhari Yau Lahadi A Gidan Gwamnatin Jihar Katsina

Salwa radio and television online media services Katsina.

Shugaba Tinubu ya sa an saki Abba Kyari tare da umurni ya koma bakin aikinsa na Ɗansanda.Menene ra'ayinku?
20/07/2025

Shugaba Tinubu ya sa an saki Abba Kyari tare da umurni ya koma bakin aikinsa na Ɗansanda.
Menene ra'ayinku?

"Idan na gaza ba ku wutar lantarki ta awa 24, ka da ku sake zabe na."ADC ta tunawa Shugaba Bola Tinubu alkawarin da ya d...
20/07/2025

"Idan na gaza ba ku wutar lantarki ta awa 24, ka da ku sake zabe na."

ADC ta tunawa Shugaba Bola Tinubu alkawarin da ya daukarwa 'yan Najeriya a 2023.

Jam'iyyar ADC ta ce ya kyautu Tinubu ya fadi zabe a 2027 don ya gaza cika alkawarinsa.

Da Ɗumi-Ɗumi Fitacciyar ƴar kasuwar nan kuma mai amfani da kafafen sada zumunta Layla Ali Othman ta buɗe katafaren gidan...
20/07/2025

Da Ɗumi-Ɗumi

Fitacciyar ƴar kasuwar nan kuma mai amfani da kafafen sada zumunta Layla Ali Othman ta buɗe katafaren gidan marayu a Abuja wanda za a riƙa kula da yaran da aka tsinta da ma waɗanda su ka rasa dukkan iyayensu a duniya.

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Je Ta'aziyyar Buhari.Fitaccen malamin addinin Musulunci na nahiyar Afrika, Sheikh Dahiru Usman B...
20/07/2025

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Je Ta'aziyyar Buhari.

Fitaccen malamin addinin Musulunci na nahiyar Afrika, Sheikh Dahiru Usman Bauchi a bisa wakilcin Khadimul Faida, Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi (R.T.A), ya kai ziyara ta musamman zuwa raudar tsohon shugaban ƙasa, marigayi Janar Muhammadu Buhari (rtd), inda ya gudanar da addu'o’i na musamman ga Allah Madaukakin Sarki domin jaddada rahama da gafara a gare shi.

Yayin ziyarar addu'o'in ta miƙa sakon jajanta wa ga iyalan mamacin, tare da bayyana rashin a matsayin babban abun alhini ba wai ga mutanen jihar Katsina ko Arewa ba har da Najeriya da faɗin duniya gaba daya.

Shehin malamin tare da wasu daga cikin manyan almajiransa da malamai sun roƙi Allah ya yafe masa kura-kuransa, ya sa kabarinsa ya kasance dausayin Aljanna, kuma ya cika masa da rahamarSa marar iyaka.

Tun da fari, tawagar ta soma miƙa saƙon ta'aziyya ga Gwamnan jihar Katsina Umar Dikko Radda, yayin wata ganawa da s**a yi a ziyarar, kafin nan s**a kai ziyara ta musamman fadar Sarkin Daura domin jajanta masa.

Muna roƙon Ubangiji Allah Ya jaddada rahama a gare shi, Ya kuma ƙara juriya da imani ga iyalan da ya bari.

Amin.

RAN MAZA YA BACI: Shugaban Ƙaramar Hukumar Rijau Dake Jihar Neja, Honarabul Ɗanladi K. Uganda Ya Shiga Daji Domin Yakar ...
19/07/2025

RAN MAZA YA BACI: Shugaban Ƙaramar Hukumar Rijau Dake Jihar Neja, Honarabul Ɗanladi K. Uganda Ya Shiga Daji Domin Yakar Ƴan Bìndiga Da S**a Addabe Karamar Hukumar

Wace fata za ku yi masa?

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Rajiun Allah Ya yi wa Yarima Alwaleed bin Khalid bin Talal bin Abdulaziz Al Saud rasuwa.Yari...
19/07/2025

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Rajiun

Allah Ya yi wa Yarima Alwaleed bin Khalid bin Talal bin Abdulaziz Al Saud rasuwa.

Yarima wanda ake wa laƙani da Yarima Mai barci ya shafe tsawon shekaru 20 yana some sai yau Allah Ya ƙarɓi abinSa.

An gudanar da jana'izar mutum 9 da ƴan bindiga su ka kashe a garin Jangeɓe waɗanda dukkaninsu manoma ne, inda a yayin ha...
19/07/2025

An gudanar da jana'izar mutum 9 da ƴan bindiga su ka kashe a garin Jangeɓe waɗanda dukkaninsu manoma ne, inda a yayin harin sun sace mutum 9 a wannan gari da ke ƙarkashin Ƙaramar Hukumar Talata-Mafara ta jihar Zamfara. Lamarin ya faru ne a jiya Jumma'a.

Rahotanni Sun Nuna Cewa 'Yàn Sanda A Garin Zaria Sun Saki Matashiyar 'Yar Shi'a Da S**a K**a Bisa Zargin Muzantà Marigay...
19/07/2025

Rahotanni Sun Nuna Cewa 'Yàn Sanda A Garin Zaria Sun Saki Matashiyar 'Yar Shi'a Da S**a K**a Bisa Zargin Muzantà Marigayi Buhari Bayan Rasuwarsa

Majiyar Rariya ta nakalto cewa gwamnatin Kaduna ce ta bada umarnin a saki matashiyar mai suna Fatima Zahra wadda take tsare a komar 'yan sandan tun jiya Juma'a.

Shin Suwa S**a Gina Ƙabarin Shugaba Buhari Daga Muhammad Aminu Kabir MUHAMMAD ALI Ne Ya Gina Ƙabarin Ko A'a?Ga ɗan abind...
19/07/2025

Shin Suwa S**a Gina Ƙabarin Shugaba Buhari

Daga Muhammad Aminu Kabir

MUHAMMAD ALI Ne Ya Gina Ƙabarin Ko A'a?

Ga ɗan abinda na kalato mana bai zama lallai dole kowa sai ya yadda ba.

K**ar yadda wasu bayin Allah s**a bayyana cewa suna bina bashin binciken gaskiyar maganar nan to Alhamdulillah na samo mana bayanai sai dai bai zama wajibi ko dole ba ace kowa ya gasgata bayanan amma dai sune abinda na iya kalatowa waɗanda zan iya faɗi.

Zancen gaskiya ba Malam Muhammad Ali ya gina ƙabarin ba amma dai yaje wurin yayi wani aikin daban dashi da wasu mutane kimanin goma amma dai ba gina ƙabarin ba.

Bisa ga sahihan bayanai da na samu shine shi Malam Ali shi da sauran mutane sunje wurin ne domin gina ƙarafan da aka zagaye wurin da ƙabarin yake da waya kamar yadda za'a ga cewa ga waya nan an zagaye ƙabarin da ita a duba cikin hotuna a ƙasa.

Shi kuma aikin tonawa, haƙar ko gina ƙabarin wasu jami'an Sojoji ne haɗi da ma'aikata yaran gidan marigayi tsohon shugaban ƙasa Buhari sune s**a gina ƙabari, kamar yadda wani bawan Allah Musbahu ya tabbatar mana wanda shi duk abinda ya faru a gaban idon shi komai ya faru.

K**ar yadda wasu suke ganin kamar an tursasa Malam Ali ya ƙarya ta kan shi akan batun haƙar ƙabarin to ba zan ce A'a ba amma dai an nuna mashi kuren shi an kuma sanya shi ya janye kalaman shi na cewa shi ya haƙa ƙabarin, batun ko an biya shi kuɗin aikin shi ko akasin hakan shine dai abin bamu samu tabbaci ba, iya abinda muka iya samu kenan.

Allah yajiƙan shugaban ƙasa Buhari Ya sanyaya makwanci Amin.

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Kotu A Matsayin LauyaDaga Muhammad Kwairi WaziriSanata Dino Melaye, wanda a kwana...
18/07/2025

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Kotu A Matsayin Lauya

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Sanata Dino Melaye, wanda a kwanan nan aka tabbatar da shi a matsayin cikakken lauya, ya yi bayyanarsa ta farko a gaban alƙalin kotu a yau Alhamis.

Tsohon Sanatan na Kogi ya bayyana a gaban alkalin kotu na takwas na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja, yana sanye da kayan lauya kamar yadda doka ta tanada.

Bayyanar Dino a kotu ta zo ne jim kaɗan bayan ya samu shaidar kammala karatunsa na lauya kuma ya shiga jiki-jikin masu kare hakkokin jama’a a cikin tsarin shari’a.

Wannan mataki yana nuna wani sabon babi a rayuwarsa ta siyasa da doka.

Tinubu ya naɗa ɗan Babangida, Aminu-Zariya da wasu mutum takwas shugabannin manyan hukumomin gwamnati
18/07/2025

Tinubu ya naɗa ɗan Babangida, Aminu-Zariya da wasu mutum takwas shugabannin manyan hukumomin gwamnati

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zuma Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zuma Times Hausa:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share