Zuma Times Hausa

Zuma Times Hausa Burin mu sanar da ku 'yancin ku.

HIKIMAR SHIGO DA ABINCI DAGA WAJE: Yadda Tinubu ya magance tsadar abinci, ba tare da samun cikas ga Shirin Farfaɗo da No...
04/11/2025

HIKIMAR SHIGO DA ABINCI DAGA WAJE: Yadda Tinubu ya magance tsadar abinci, ba tare da samun cikas ga Shirin Farfaɗo da Noma a Nijeriya ba

Daga Tanimu Yakubu

Jaridar Daily Trust ta ranar 6 ga Oktoba 2025, tana ɗauke da ra'ayin ta mai nuni da cewa "Shirin Shigo da Abinci da Gwamnatin Tinubu ke yi yana Gurgunta Harkokin Noma a Arewa." Ra'ayin jaridar ya nuna damuwa kan makomar manoman Arewa da halin da za su tsinci kan su a ciki.

Ra'ayin na gidan jaridar ya yi nuni da matsi da takurar da manoman karkara ke fuskanta, k**a daga tsadar noma, barazanar sauyin yanayi, matsalar tsaro da kuma fargabar gogayyar farashi da kayan abincin da ake shigo da su daga waje. Lallai kuwa akwai waɗannan ƙalubale, to amma duk Gwamantin Tarayya na sane da su, kuma tana taka-tsantsan da su.

Sai dai kuma cewa wai shigo da kayan abinci da gwamnati ke yi yana "gurgunta" harkokin noma a Arewa, jaridar ba ta gabatar da wasu hujjoji ba, ba ta kuma yi duba da la'akari da tsare-tsaren gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na game-garin faɗin ƙasar nan ba.

Gaskiyar shi wannan tsari dai an bijiro da shi ne hususan domin gaggauta samar wa jama'a sauƙin rayuwa a yayin da gwamnati ke aiwatar da tsare-tsaren farfaɗo da arzikin ƙasa mai dogon-zango.

Tilas Ta Sa Tinubu Gaggata Shigo da Abinci, Ba Watsi da Manoma Ya Yi Ba:

Nijeriya ta fuskanci matsanancin ƙarancin abinci a daidai tsakiyar 2025. Malejin tsadar abinci ya cilla sama, har sai da ya ƙaru da kashi 40 bisa 100. Sannan kuma nauyin aljihun jama'a ya ragu sosai, ba su iya sayen abincin da zai wadace su. Miliyoyin jama'a s**a riƙa gaganiya da tsadar abinci a manyan biranen ƙasar nan da dama. Duk a lokacin, aka kuma fuskanci annobar ambaliya a Arewa-maso-gabas. Ga kuma fari ya addabi Arewa-maso-Yamma, sai kuma matsalar rashin tsaro da ta baibaye yankin Tsakiyar Nijeriya. Waɗannan matsaloli sun haifar da raguwar yawan amfanin gonar da manoma ke nomawa.

Dalilin waɗannan matsaloli ne Shugaban Ƙasa ya amince da jingine dokar karɓar kuɗaɗen haraji daga kayan abincin da ake shigowa da su, irin su masara, shinkafa, alk**a, dawa da kuma gero. Amma hakan ba kaucewa aka yi kan shirin inganta harkokin noma ba. An dai shigo da kayan abinci ne domin kauce wa ɓarkewar yunwa, saisaita farashin kayan abinci daidai aljihun talakawa, sannan kuma a dawo wa jama'a da yaƙinin kyakkyawar fatan da suke da shi kan gwamnati.

Da Tinubu bai gaggauta bayar da umarnin cire harajin shigo da waɗannan kayan abinci ba, to tabbas sai gwamnati ta riƙa kamfatar maƙudan kuɗaɗe tana biyan tallafin kayan abinci, ko a gaggauta shigo da kayan abinci da kuɗaɗen da ba su cikin kasafin kuɗaɗe. Da an yi hakan kuwa, to lallai sai an fuskanci mummunan tsadar kayayyaki, sannan kuma a haifar da wawakeken giɓin kasafin kuɗaɗe. Saboda haka abin da aka yi hanya ce mai kyau da aka sauƙaƙa wa magidanta tsadar rayuwa, ba tare da haifar da tangarɗa kan tattalin arzikin ƙasa ba.

Yadda Gwamnati Ke Farfaɗo da Harkar Noma Yayin da Take Sassauta Farashin Abinci:

Tunanin bijiro da ɗaukin gaggawa wajen shigo da abinci domin sauƙaƙa farashi, ya zo ne tare matakan bunƙasa yawan abincin da ake nomawa:

1. Shirin Samar da Kayan Aikin Noma, wato Agricultural Inputs Support Window (AISW): Samar da Naira biliyan 150 ta Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya tare da Babban Bankin Nijeriya (CBN), domin rage farashin takin zamani da magungunan ƙwari zuwa sauƙin kashi 22 na farashin su. Sai kuma tallafa wa ƙungiyoyi da sassaucin kuɗin safarar kayayyaki.

2. Faɗaɗa Filayen Noma:
Ma'aikatar Samar Ruwa ta Tarayya ta fara aikin faɗaɗa filayen noma har faɗin eka 400,000 a Haɗejia, Bakolori da Daɗin Kowa. waɗannan ayyuka ana ci gaba da gaggauta yin su domin a bunƙasa noman rani a 2026.

3. Rumbunan Tanadin Abinci da Sassauta Farashi: Ana samar da manyan rumbunan adana abinci har zuwa tan 750,000, waɗanda za a fitar da su kasuwanni a lokacin rani, ta yadda za a daidaita farashin kayan gona, ba tare da an dagula darajar amfanin gona ba.

4. Tsarin Bayar Da Lamuni da Raba Asara a ƙarƙashin ACGSF a yanzu zai yi fa'ida sosai ga ƙananan manoma, tare da samun tabbacin sa'ida daga Gwamnatin Tarayya a yayin da aka fuskanci asara sak**akon matsalar tsaro ko ambaliya.

5. Shirin Dawo da Harajin Shigo da Kayan Abinci: Dakatar harajin kayan abinci abu ne mai taƙaitaccen lokaci, nan da watan Disamba 2025. Cikin watanni ukun farkon shekarar 2026 ne kuma za a dawo da ƙaramin harajin kayan abinci, idan aka samu cigba a fannin samar da abinci.

Waɗannan matakai sun nuna tare da tabbatar da cewa tsarin da wannan gwamnati ke amfani da shi wajen bunƙasa kayan abinci, ba a gina shi kan shigo da abinci kaɗai ba. An gina shi ne kan tunanin samar da sassaucin tsadar rayuwa, domin kaiwa ga iya dogaro da kai.

Saisaita Tunanin Masu Mummunar Fahimta:

Ra'ayin jaridar Daily Trust ya yi shaci-faɗin cewa ɗage biyan harajin shigo da kayan abinci da aka yi na wani lokaci, wai ya gurgunta manoman Arewa. Wannan kintace ne kawai, jaridar ba ta yi la'akari da cewa shi kan sa tattalin arzikin ya fuskanci tsadar musayar kuɗaɗen waje, matsalar wutar lantarki da sauran matsaloli, waɗanda s**a haifar da cikas ga samun riba, tun ma kafin a dakatar da karɓar harajin shigo da kayan abinci daga waje.

Maganar gaskiya tsarin shigo da abinci da aka yi, ya amfani masu samar da abinci a cikin ƙasa, domin ya daƙile hauhawar farashi, ya kawar da mummunar ɗabi'ar ɓoye abinci a fito da shi lokacin da ya yi tsada, kuma ya tabbatar da samun kayan aikin noma daidai gwargwadon ƙarfin aljihun manoma, sai kuma samar da kayan masarufi ta yadda sauƙin sa ya sa bai yi ƙaranci ba. Matsawar aka daƙile hauhawar farashin kayan abinci, to manoma za su iya tsara yadda za su yi noma da cin moriyar sa, ba tare da shakku ba.

Kuma yana da muhimmanci a sani cewa tsarin samar da abinci a Nijeriya yana da alaƙa tsakanin wannan yanki da sauran kowane yankin ƙasa. Adadin amfanin gonar da ake buƙata a birane da garuruwa na da tasiri ga kasuwannin yankunan karkara, yayin da sauƙaƙa farashi, zai kawar da yunƙurin tayar da tarzoma. Kuma zai zama kandagarkin kare nauyin aljihun miliyoyin marasa ƙarfi.

Fa'idoji da Alfanun Ɗage Harajin Shigo da Abinci:

Ci Gaba da Ƙarfafa Manoma da Kare Masu Sayen Kayan Abinci:

Yayin da ake ci gaba da samun haske, Gwamnatin Tarayya za ta dawo da harajin shigo da kayan abinci tare da faɗaɗa tsarin sarrafa amfanin gona, adana kayan gona da kuma safarar sa. Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya na aiki tare da Ma'aikatar Gona ta Tarayya, Ma'aikatar Harkokin Kuɗaɗe, Babban Bankin Nijeriya, CBN da Majalisar Tattalin Arziki domin tabbatar da cewa kuɗaɗen yin manyan ayyukan inganta tattalin arziki irin su gina titina a yankunan karkara, samar da masana'antun takin zamani da rumbunan tanadin hatsi duk an ba su fifiko a jihohin arewa.

Burin da ake so a cimma a nan, shi ne bayar da dama yadda manoman Arewa za su riƙa gogayya da na Kudu ta ɓangaren yawan albarkar noma, samun lamuni da kuma samar da kayayyakin inganta rayuwa da ƙasa baki ɗaya.

A ƙarshe, a yi wa shirin shigo da abinci daga waje da Shugaba Tinubu ya bijiro da shi kyakkyawar fahimta cewa shiri ne na gaggawar magance matsalar abinci da ta kunno kai, domin hana ta yi muni. Amma ba an yi don a dagula ko gurgunta kasuwar kayan abinci ba. Yunƙuri aka yi mai tabbatar da kyakkyawan jagorancin nuna tausayi ga marasa galihu.

Yayin da komai ke ƙara ɗaukar saiti sannan tsadar kayayyaki na ci gaba da lafawa nan zuwa watan Disamba 2025, Nijeriya za ta fara tafiya bisa cikakkar turbar samar da wadataccen abinci a cikin gida. Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya na jaddada ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke kan yi wajen bunƙasa harkokin noma a Arewa, a matsayin yankin wanda da shi ne jagoran samar da wadataccen abinci ga ƙasa, sannan kuma ya kasance yanki mai yalwar arziki.

Saboda haka a daina fassara wannan shirin shigo da abinci na wucin-gadi a matsayin kauce wa tsarin da ake a kai. A'a, hanya ce ta gaggauta farfaɗowa - kuma ana tafiya ɗoɗar kan turbar shirin farfaɗo da noma a Nijeriya.

*Yakubu shi ne Babban Darakta, Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya,
Fadar Shugaban Ƙasa,
Abuja.

‎China Ta Caccaki Amurka Kan Tsoma Baki a Harkokin Najeriya — DW Hausa‎‎Gwamnatin kasar China ta caccaki Amurka kan abin...
04/11/2025

‎China Ta Caccaki Amurka Kan Tsoma Baki a Harkokin Najeriya — DW Hausa

‎Gwamnatin kasar China ta caccaki Amurka kan abin da ta bayyana a matsayin tsoma baki cikin harkokin cikin gida na Najeriya, tana mai jaddada goyon bayanta ga Najeriya a matsayin abokiyar hulɗarta ta gaskiya.

‎Kafar DW Hausa ta ruwaito cewa, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen China, Mao Ning, ta bayyana cewa Beijing ba ta goyon bayan kowace ƙasa da ke amfani da batutuwan addini ko ‘yancin ɗan Adam a matsayin hujja don tsoma baki ko yin barazana ga wata ƙasa mai ‘yanci.

‎Ta kuma jaddada cewa China na kallon Najeriya a matsayin muhimmiyar abokiyar hulɗa a nahiyar Afirka, tare da niyyar ci gaba da ƙarfafa dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu bisa ginshiƙan mutunta juna da moriyar juna.

SHIRIN ƘARFAFA JARIN BANKUNA: CBN ya shawarci bankunan da ba su da ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su gejiAshafa Mur...
04/11/2025

SHIRIN ƘARFAFA JARIN BANKUNA: CBN ya shawarci bankunan da ba su da ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

Ashafa Murnai Barkiya

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Olayemi Cardoso, ya yi magana dangane da ƙoƙarin da bankuna ke yi domin ganin sun cika sharuɗɗan adadin ƙarfin jari da CBN ya gindaya masu.

Ya ce da yin hakan zai sa a guje wa sake maimata kura-kuran da aka taɓa yi can a baya.

"Mun bai wa bankunan kasuwanci isasshen lokaci da kuma zaɓi domin ganin sun cika sharuɗɗan da aka gindaya masu. Saboda haka ba wani abin tayar da hankali ko razana a nan." Inji Cardoso.

Da yake magana kan batun tsare-tsaren inganta tattalin arziki, kuɗaɗen ruwa da kuma taƙaita karɓar lamuni daga masu kasuwanci, gwamnan ya ce tilas batun bunƙasa tattalin arziki mai ɗorewa shi ne farkon abin dubawa, kafin a yi maganar batun ramce mai karsashi.

"Domin idan tattalin arziki bai samu nagartaccen tushe ko tubali na, to samun ci gaba ba zai yiwu ba. Maganar cewa kuɗin ruwa ya yi tsada kuma haka ɗin ne, amma tunda tattalin arziki ya hau kan miƙaƙƙar hanya, za a sassauta kuɗin ruwan."

Ya yi wannan jawabi wurin taron da London Business School tare da haɗin guiwar JP Morgan da Goldman Sachs s**a shirya.

A wani labarin kuma, Ministan Harkokin Kuɗaɗe, Wale Edun, ya jinjina wa Gwamnan CBN, Cardoso, dangane da nasarorin da yake samu wajen aiwatar da tsare-tsaren tattalin arzikin ƙasa masu tasirin daƙile tsadar rayuwa da kuma taka wa hauhawar farashin kayayyaki burki.

Edun ya yi bayanin a wurin taron da Cibiyar Chartered Institute of Bankers of Nigeria (CIBN) ta shirya, a Legas.

Ya ce CBN na ƙoƙari matuƙa wajen dawo wa tattalin arzikin Nijeriya da tsarin hada-hadar kuɗaɗe darajar su a idon masu zuba jari.

BA ZAMU ZUBA IDO IDAN AMURKA TAYIWA NIGERIA KATSALANDAN A HARKOKIN CIKIN GIDANTADaga Rabiu BiyoraA wata sanarwar da ofis...
04/11/2025

BA ZAMU ZUBA IDO IDAN AMURKA TAYIWA NIGERIA KATSALANDAN A HARKOKIN CIKIN GIDANTA

Daga Rabiu Biyora

A wata sanarwar da ofishin kula da harkokin kasashen waje na China ta fitar a wannan rana ta Talata, China tace ba zata zuba ido ta bari Amurka tayiwa Nigeria katsalandan a harkokin cikin gidanta ba, zancen cewa Gwamnatin Nigeria ta zuba idanu ana halaka kiristoci ba gaskiya bane sharri ne da amurka tare da yan kanzangi s**a shirya domin cimma wasu burikansu...

Tabbas akwai matsalolin tsaro dake faruwa a Nigeria wanda ya shafi kowanne bangare na addinai a Nigeria ba wai kiristoci zallah ba, yan ta'adda masu halaka mutane suna aikata ayyukansu akan musulmi da kiristoci..

China babbar aminiyar Nigeria ce, zamu cigaba da kasancewa Aminai a lokacin daɗi da lokacin barazana, Shugaba Tinubu yana da kyakkyawar alaka da kasar China sannam china tana da hannu wajen ganin rayuwar yan Nigeria ta ingantu a sabbin yarjejeniyoyin da aka sanyawa hannu na kara inganta harkokin tattalin arzikin Nigeria...

Nigeria ta dauko hanyar zama babbar kasa mai tasiri a duniya, ba zamu zuba ido mu bari Amurka ta lalata wannan kudiri na Nigeria ba, muna tare da Nigeria a kowane hali inji Mao Ning kakakin Hukumar kula da harkokin kasashen waje na China

Mawakin Kudu, Burna Boý Ya Kàrbì MusuĺùncìShahararren mawakin Najeriya, Damini Ogulu wanda aka fi sani da 'Burna Boy', y...
03/11/2025

Mawakin Kudu, Burna Boý Ya Kàrbì Musuĺùncì

Shahararren mawakin Najeriya, Damini Ogulu wanda aka fi sani da 'Burna Boy', ya bayyana cewa ya karɓi Musulunci bayan dogon lokaci yana nazari da neman gaskiya game da addini da manufar rayuwa.

A cewar Burna Boy, babu wanda ya tilasta masa sauya addini, sai dai ya samu nutsuwa da fahimtar gaskiya bayan zurfin tunani.

“Na binciki addinai da yawa, ina tambayar kaina menene gaskiya game da rayuwa. A ƙarshe zuciyata ta samu natsuwa da Musulunci, don haka na karɓe shi,” in ji shi.

Mawakin ya ƙara da cewa yana mutunta dukkan addinai, kuma yana kira ga jama’a su zauna lafiya da juna, su guji rarrabuwa saboda addini ko ƙabila.
Boy, wanda ya yi fice da wakoki k**ar “Last Last” da “City Boys”, ya ce burinsa shi ne ya rayu cikin gaskiya da mutunci, ba wai don sunan addini kawai ba.

Daga Sawaba Fm

ZAA DENA AMFANI DA DOLLAR A SIYEN TICKETS A NIGERIA....Rabiu BiyoraGwamnatin Nigeria tana duba yiyuwar dakatar da siyen ...
03/11/2025

ZAA DENA AMFANI DA DOLLAR A SIYEN TICKETS A NIGERIA....

Rabiu Biyora

Gwamnatin Nigeria tana duba yiyuwar dakatar da siyen tikitin jiragen saman kasashen waje da akeyi da Dollar...

A yanzu kusan duk Tickets da ake siya na kamfanonin jiragen sama da suke jigilar fasinjojin Nigeria suna siyar da Tickets dinsu ne da Dollar maimakon Naira wanda hakan ke karawa Dollar daraja a Nigeria kuma yake rage darajar Naira, sai dai a iya cewa hakan na gaf da zama tarihi domin gwamnatin Nigeria tace hakan ba zai cigaba da faruwa a kasarta ba..

Kamfanonin jiragen sama irinsu British Airway, Lufthansa da Emirates suna siyar da Tickets dinsu da Dollar maimakon Naira duk da cewa fasinjojin Nigeria suke dauka a cikin Nigeria, akwai sauran kamfanoni masu yawa da suma suke siyar da Tickets da Dollar maimakon Naira ..

Gwamnati tace dole ne ta kawo tsare tsaren da zasu durkusar da Dollar tare da hanata cigaba da hauhawa....

Yadda Dolar take a matsayin kudi haka ita ma Naira take don haka dole ne a mutumta Naira a cikin Nigeria, ba zai yiyu aki amfami da Naira a Amurka sannan ace zaa dinga amfani da Dollar a Nigeria....

Daga shafin TRT HausaMenene ra'ayinku?
03/11/2025

Daga shafin TRT Hausa

Menene ra'ayinku?

03/11/2025

Kowa ya saurari wanna bayani, ya fada mana ko ya yarda da ita ko sabanin haka.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!!Yanzu mu ke samun labarin rasuwar Malam Nata'ala a cikin daren bayan fama da jinya...
02/11/2025

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!!

Yanzu mu ke samun labarin rasuwar Malam Nata'ala a cikin daren bayan fama da jinya.

Farfesa Sheriff Almuhajir daga jihar Yobe ne ya tabbatar da labarin. Inda ya nuna matuƙar kaɗuwarsa da rsuwar.

Martanin Tinubu ga Trump kan ikirarin kashe-kashen Kiristoci a NajeriyaGwamnatin Tarayyar Najeriya ta karyata kalaman  S...
02/11/2025

Martanin Tinubu ga Trump kan ikirarin kashe-kashen Kiristoci a Najeriya

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta karyata kalaman Shugaban Amurka, Donald J. Trump, da ya yi ikirarin cewa ana kashe Kiristoci da yawa a Najeriya, tare da kira da a sanya kasar cikin jerin kasashen da ke take hakkin addini.

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar ranar Asabar, 1 ga Nuwamba, 2025, mai dauke da sa hannun Kimiebi Imomotimi Ebienfa, mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, gwamnatin ta ce kalaman Trump ba sa nuni ga ainihin halin da ake ciki a kasar ba.

Sanarwar ta ce: “Najeriya tana godiya da damuwar kasashen duniya game da kare hakkin bil’adama da ‘yancin addini, amma wannan ikirari ba shi da tushe. ‘Yan Najeriya mabiya dukkan addinai suna rayuwa, aiki da kuma ibada tare cikin lumana.”

Ma’aikatar ta kara da cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ci gaba da jajircewa wajen yaki da ta’addanci, karfafa zumuncin addinai, da kare rayuka da hakkokin dukkan ‘yan kasa.

Najeriya ta kuma bayyana cewa za ta ci gaba da yin aiki tare da gwamnatin Amurka domin inganta fahimtar juna kan harkokin yankin da kuma kokarin da ake yi wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasar.

CBN YA YUNƘURO: Naira ta hana Dalar Amurka numfashi mai ƙarfi a ƙarshen OktobaAshafa MurnaiNaira ta ci kasuwar ƙarshen w...
02/11/2025

CBN YA YUNƘURO: Naira ta hana Dalar Amurka numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

Ashafa Murnai

Naira ta ci kasuwar ƙarshen watan Oktoba tare da samun galabar Naira 15.33 kan Dalar Amurka, a ranar 31 ga Oktoba.

Naira ta samu wannan tagomashin na Naira 15.33 a ranar Juma'a kan Dala a kasuwar 'yan canji da kuma Hada-hadar Musayar Kuɗaɗe ta bai-ɗaya (NAFEM).

A Abuja dai an sayar da Dala $1 kan Naira 1450, yayin da masu canji s**a saya kan Naira 1440.

An samu rangwame idan aka kwatanta da yadda aka sayi Dalar Amurka kan Naira 1,465 a ranar Alhamis.

Masu lura da kuma sharhi kan tattalin arzikin ƙasa da hada-hadar kuɗaɗe sun danganta wannan gwauron numfashi da Naira ta yi da irin ƙoƙarin da CBN yake kan yi wajen saisaitawa da daidaita farashin musayar kuɗaɗe.

Address

Number 17B Sidi Plaza Behind Old NEPA Off Sulemanu Barau Road Suleja
Abuja
910101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zuma Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zuma Times Hausa:

Share