Zuma Times Hausa

Zuma Times Hausa Burin mu sanar da ku 'yancin ku.
(2)

Gargaɗi Daga CBN:  A yi hattara da  wasiƙar dala bilyan 46, jabu ce ba daga CBN ta fito baAshafa Murnai Barkiya Babban B...
11/09/2026

Gargaɗi Daga CBN: A yi hattara da wasiƙar dala bilyan 46, jabu ce ba daga CBN ta fito ba

Ashafa Murnai Barkiya

Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya fitar da kakkausan gargaɗi cewa a yi hattara da wata wasiƙa ko satifiet, mai ɗauke da iƙirarin cewa bankin ya amince a bai wa wata cibiyar bayar da tallafi dala bilyan 46.

A cikin wata sanarwar gargaɗi da CBN ya fitar a ranar Alhamis, babban bankin ya ce Gwamnan CBN, Olayemi Cardoso bai bayar da wannan umarni a rubuce ba. Don haka takardar ta bogi ce.

Takardar bogin wadda ke ɗauke da kwanan watan 13 ga Agusta, 2026, na ɗauke da sa-hannun Cardoso, mai nuna a rubuce cewa ya amince a bai wa Cibiyar Bayar da Tallafi da Ayyukan Bunƙasa Al'umma na ATUFEG Empowerment and Development Center har zunzurutun kuɗi dala bilyan 46.

CBN ya ce takardar mai lamba GOV/END/2026/00050, jabu ce, daga 'yan damfara ta fito. Bankin ya kuma ya ja kunnen masu alkata irin wannan cewa akwai ranar ƙin dillanci.

Gargaɗi Daga Babban Bankin Nijeriya (CBN): * Har yanzu haramcin kekketa takardun naira na nan daram.* Har gobe hani kan ...
10/09/2026

Gargaɗi Daga Babban Bankin Nijeriya (CBN):

* Har yanzu haramcin kekketa takardun naira na nan daram.

* Har gobe hani kan wulaƙanta takardun naira yayin bukukuwa na nan daram.

* Ko yanzu jan-kunne kan duƙunƙune takardun naira na nan daram.

* Ko gobe dokar buga jabun kuɗi na nan da tsaurin ta.

* Darajar naira ma'aunin darajar tattalin arzikin Nijeriya ne.

* Shafa wa naira datti tamkar ƙasƙanci ne ga naira.

CBC: Jagoran bunƙasa tattalin arzikin Nijeriya

Ƙungiyar Kiristoci ta goyi bayan Tinubu a zaɓen 2027Ƙungiyar "Charismatic Bishops Conference of Nigeria" (CBCN) ta bayya...
10/09/2026

Ƙungiyar Kiristoci ta goyi bayan Tinubu a zaɓen 2027

Ƙungiyar "Charismatic Bishops Conference of Nigeria" (CBCN) ta bayyana goyon bayan ta ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a babban zaɓen 2027.

Shugaban CBCN, Archbishop Prof. Leonard Bature Kawas, shi ne ya bayyana matsayar ƙungiyar a ranar Laraba a Abuja, a lokacin da ake gudanar da babban taron Synod na 2026 na CBCN da ICCABA a Majami'ar Kiristoci ta Ƙasa.

Kawas ya ce ƙungiyar ta yi nazari kan ayyukan gwamnatin Tinubu, tare da bayyana shirin ta na ci gaba da mara wa shugaban ƙasar baya ta hanyar addu’a, bayar da shawarwari da kuma wayar da kai.

Ya ce: “Mun goyi bayan sa a yanzu. Mun goyi bayan sa yau, za mu goyi bayan sa gobe, kuma za mu ci gaba da goya masa baya muddin yana son kasancewa shugaban ƙasar mu.”

Ya ƙara da cewa: “Wannan gida ya amince da shi a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na 2027.”

Da yake jawabi a wajen taron, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci shugabannin addini da su yi amfani da tasirin su wajen ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da kyakkyawar mu’amala tsakanin al’umma gabanin zaɓen 2027.

Ya ce: “Ci gaba da haɗa kan wannan ƙasa na buƙatar fiye da matakan gwamnati. Yana buƙatar jagoranci nagari daga dukkan ɓangarorin al’umma, ciki har da jagorancin addini."

Idris ya yi gargaɗi kan yunƙurin nuna matsalolin tsaron Nijeriya a matsayin yaƙin addini, yana mai cewa ’yan ta’adda da ƙungiyoyin masu aikata laifuka sun kai wa ’yan Nijeriya hare-hare ba tare da la’akari da addinin su ko asalin su ba.

“Kada a bari wani zaɓe ya sa Kirista ya juya wa Musulmi baya, ko Musulmi ya juya wa Kirista baya, ko Arewa ta juya wa Kudu baya, ko wata ƙabila ta juya wa wata baya. Nijeriya tamu ce baki ɗaya,” inji shi.

Da yake wakiltar Shugaban Ƙasa Tinubu, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya yaba wa ma'abota cocin kan gudunmawar su ga zaman lafiya da haɗin kan ƙasa, tare da kira da a samu ƙarin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da shugabannin addini.

Ya ce: “Gwamnati tana buƙatar gudunmawar Kiristoci wajen kyautata ɗabi’a da tarbiyyar al’umma, yayin da Kiristoci suke buƙatar yanayin da zai ba su damar gudanar da ayyukan su da kyau. Fiye da komai, Nijeriya tana buƙatar mu yi aiki tare domin amfanin kowa.”

Rahotanni Sun Bayyana Cewa An Shigo Har Gida Àn̈ Ķashè Mai Shaŕhi Kan Al'amuran Siyasa, Ibrahim Khalil Ɗan Shagamu A Kan...
09/09/2026

Rahotanni Sun Bayyana Cewa An Shigo Har Gida Àn̈ Ķashè Mai Shaŕhi Kan Al'amuran Siyasa, Ibrahim Khalil Ɗan Shagamu A Kano

Matar Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo Dake Kano Ta RasuAllah ya yi wa amaryar Shugaban Karamar Hukumar Kabo ta Jihar Kano,...
09/09/2026

Matar Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo Dake Kano Ta Rasu

Allah ya yi wa amaryar Shugaban Karamar Hukumar Kabo ta Jihar Kano, Hon. Lawan Najume, Hajiya Maimuna wadda aka fi sani da Hajjo, rasuwa.

Lawan Najume ne ya tabbatar da rasuwar matarsa a wani saƙon da ya wallafa a shafinsa. na Facebook

Najume ya bayyana cewa, marigayiyar ta rasu ne bayan ta yi fama da rashin lafiya.
Hajiya Maimuna ta rasu ne a ƙasar Masar ranar Talata 8 ga Satumba, 2026.

Tuni shugaban ƙaramar hukumar ya soma karɓar saƙonnin taʼaziyya kan rashinta

Daga Mukhtar Lawan Liver Gwarzo

CBN ya ƙara bada fifikon sa-ido wajen daƙile hadahadar kuɗaɗen ɗaukar nauyin ta'addanciDaga Ashafa Murnai BarkiyaA ƙoƙar...
09/09/2026

CBN ya ƙara bada fifikon sa-ido wajen daƙile hadahadar kuɗaɗen ɗaukar nauyin ta'addanci

Daga Ashafa Murnai Barkiya

A ƙoƙarin sa na kare darajar tsarin harkokin kuɗi a Nijeriya, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ƙara ƙarfafa sa-ido wajen kula da harkokin kuɗi, domin daƙile duk wasu hanyoyi da kafofin da masu ɗaukar nauyin ta'addanci ke bi.

CBN ya jaddada cewa ya mayar da wannan batu a matsayin ɗaya daga cikin manyan abubuwan da yake bai wa fifiko a halin yanzu, domin hana miyagun mutane amfani da tsarin kuɗin ƙasar nan wajen aikata ayyukan da ba su dace ba.

CBN ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Daraktar Riƙo a Sashen Hulɗa da Jama'a da Hulɗa da Masu Zuba Jari, Hajiya Hakama Sidi-Ali, wadda aka raba wa manema labarai a ranar Talata.

A ƙarƙashin wannan sabon matakin ƙara tsaurara sa-ido, CBN ya ce zai mayar da hankali sosai musamman kan yadda cibiyoyin kuɗi ke tafiyar da haɗarin da ke tattare da samar da kuɗaɗen tallafa wa ta'addanci, sa-ido kan hada-hadar kuɗi, aiwatar da takamaiman takunkuman hadahadar kuɗi, da kuma bayar da rahoton duk wata mu'amala mai cike da shakku da ake dangantawa da tallafa wa ta'addanci.

Bankin ya ce zai ci gaba da amfani da tsarin sa-ido bisa la'akari da girman haɗari, ciki har da bincike kai tsaye a cibiyoyin kuɗi da kuma sa-ido daga nesa, domin ƙarfafa matakan yaƙi da masu halatta kuɗaɗen haram (AML), yaƙi da masu samar da kuɗaɗen ta'addanci (CFT), da kuma hana hadahadar samar da kuɗaɗen yaɗuwar makamai masu haɗari (CPF) a faɗin ɓangaren harkokin kuɗi.

A cewar CBN, za a aiwatar da waɗannan matakai ne bisa ga dokoki da ƙa'idojin da ake da su a halin yanzu.

Babban bankin ya kuma bayyana cewa matakin yana tallafa wa haɗin gwiwar Nijeriya a gida da kuma ƙasashen duniya wajen yaƙi da samar da kuɗaɗen ta'addanci, hana samar da kuɗaɗen yaɗuwar makamai masu haɗari, da kuma faɗaɗa ƙoƙarin ƙarfafa mutuncin tsarin kuɗi da kare tsarin kuɗin ƙasar nan.

CBN ya ƙara da cewa, “za a ci gaba da gudanar da ƙarin sa-ido da tuntuɓa idan buƙatar hakan ta taso.”

Sanarwar ta ƙara da cewa wannan mataki yana nuna ci gaba da jajircewar CBN wajen kare tsarin kuɗi na Nijeriya daga ayyukan da ba bisa ƙa'ida ba, tare da bayar da gagarumar gudunmawa a fannin ƙoƙarin ƙarfafa mutunci da amincin tsarin kuɗi, a matakin cikin gida da kuma na ƙasa da ƙasa.

Tattalin Arziki: Asusun ajiyar kuɗaɗen wajen Nijeriya ya cika maƙil da dala biliyan 54, cika mafi  yawa cikin shekaru 18...
07/09/2026

Tattalin Arziki: Asusun ajiyar kuɗaɗen wajen Nijeriya ya cika maƙil da dala biliyan 54, cika mafi yawa cikin shekaru 18 -CBN

Ashafa Murnai Barkiya

Sabon bayanin da ya fito daga Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya nuna yadda asusun ajiyar kuɗaɗen waje na Nijeriya ya haura zuwa dala biliyan $54.08, wanda hakan ya zama cika mafi yawa cikin kusan shekaru 18, tare da zarce hasashen da CBN ya yi na ƙarshen shekarar 2026.

Bayanan na CBN sun nuna cewa asusun ajiyar ya kai dala biliyan $54.08 a ranar 3 ga Satumba, idan aka kwatanta da dala biliyan $53.99 a ranar 2 ga Satumba da kuma dala biliyan $53.90 a ranar 1 ga Satumba.

Wannan sabon matsayi shi ne mafi girma da aka samu tun ranar 22 ga Disamban 2008, lokacin da asusun ajiyar kuɗaɗen waje na ƙasar ya kai ƙimanin dala biliyan $54.21.

Asusun ajiyar ya ƙaru da kusan dala biliyan $1.42 daga dala biliyan $52.66 da aka rattaba a ranar 19 ga Agusta.

Tun daga farkon shekarar nan ta 2026 zuwa yanzu, asusun ya ƙaru da ƙimanin dala biliyan $8.52, daga dala biliyan $45.56 a ranar 2 ga Janairu, wanda ke nuna ƙarin kaso 18.7 cikin 100 cikin sama da watanni takwas kacal.

Wannan sabon hauhawar asusun ajiyar kuɗaɗen waje ya biyo bayan ci gaba da ƙaruwar asusun ajiyar a watan Agusta, inda ya fara haura dala biliyan $53 a ranar 24 ga Agusta, lokacin da ya kai dala biliyan $53.11.
Daga bisani, ya kai dala biliyan $53.30 a ranar 26 ga Agusta, sannan dala biliyan $53.51 a ranar 28 ga Agusta, da kuma dala biliyan $53.81 a ranar 31 ga Agusta.

Asusun ajiyar ya tsaya kan dala biliyan $53.90 a ranar 1 ga Satumba, kafin daga bisani ya haura matakin dala biliyan $54 bayan kwana biyu.

Sabon matsayin ya kuma zarce hasashen CBN na dala biliyan $51.04 na asusun ajiyar kuɗaɗen waje zuwa ƙarshen shekarar 2026 da ƙimanin dala biliyan $3.04.

Gwamnan CBN, Olayemi Cardoso, ya danganta ci gaba da ƙaruwar asusun ajiyar da ƙaruwar shigar kuɗaɗen musayar waje cikin ƙasar, ciki har da kudaden da ake samu daga haraji masu alaƙa da ɗanyen mai da kuma wasu kuɗaɗen da ke shigowa daga wasu ɓangarori na waje.

Ƙaruwar asusun ajiyar kuɗaɗen waje ta kuma zo daidai da ci gaba da ƙarfin naira a kasuwar musayar kuɗaɗen waje.

Rahoton ya nuna cewa naira ta ƙara daraja zuwa Naira 1,315 kan kowace dala a kasuwar hukuma a ranar Alhamis, wanda shi ne mafi ƙarfin matsayin ta cikin shekaru biyu.

Ƙaruwar asusun ajiyar kuɗaɗen waje na samar wa tattalin arzikin Nijeriya ƙarin kariya da damar tinkarar ƙalubalen kuɗaɗen waje, tare da ƙara wa CBN ƙarfin tabbatar da zaman lafiyar kasuwar musayar kuɗaɗen waje.

CBN: Liɗifi da tagomashin kasuwanci ya inganta karo na uku a jereDaga Ashafa Murnai BarkiyaBabban Bankin Nijeriya (CBN) ...
07/09/2026

CBN: Liɗifi da tagomashin kasuwanci ya inganta karo na uku a jere

Daga Ashafa Murnai Barkiya

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana rahoto mai ɗauke da bayanin cewa yanayin gudanar da harkokin kasuwanci a Najeriya ya ci gaba da inganta har tsawon wata na uku a jere, lamarin da ke nuna ci gaba da bunƙasar harkokin tattalin arziki duk da matsin lambar tsadar rayuwa da kuma ƙalubalen gudanar da kasuwanci.

Wannan ci gaban na zuwa ne yayin da 'yan kasuwa ke ci gaba da daidaita kan su da sauye-sauyen manufofin kuɗi da yanayin tattalin arziki, inda ƙaruwar harkokin kasuwanci ke samar da yanayi, liɗifi da tagomashi mafi dacewa ga zuba jari da faɗaɗa ayyuka.

Sabon binciken da CBN ya gudanar ya ƙara tabbatar da wasu bayanai na baya-bayan nan da ke nuna cewa tattalin arzikin Nijeriya na ci gaba da farfaɗowa.

Harkokin Kasuwanci Na Ci Gaba da Ƙaruwa:

Wannan sabon ci gaban ya ƙara tsawaita yanayin ingantuwar harkokin kasuwanci da Nijeriya ta shafe watanni uku tana samu.

Binciken CBN ya zo ne a daidai lokacin da harkokin tattalin arziki gaba ɗaya ke nuna alamun ci gaba, inda bayanai na baya-bayan nan s**a nuna bunƙasar ayyuka a muhimman fannoni daban-daban na tattalin arzikin ƙasar nan.

A fannin 'yan kasuwa, ci gaba da ingantuwar yanayin gudanar da ayyuka na iya ƙara musu ƙwarin gwiwar ci gaba da samar da kayayyaki, faɗaɗa ƙarfin ayyukan su da kuma yanke shawarar zuba jari na dogon lokaci.

Sai dai kuma, 'yan kasuwa na ci gaba da fuskantar ƙalubale sakamakon tsadar gudanar da ayyuka, yanayin samun rance, matsalolin ababen more rayuwa da kuma hauhawar farashi.

Masana'antu da Sauran Fannoni Na Da Muhimmanci:

Yanayin kasuwanci a Nijeriya na da alaƙa sosai da yadda ayyuka ke gudana a fannonin masana'antu, ayyukan hidima, noma da sauran sassan da ke samar da kayayyaki da ayyuka.

Masana'antun ƙera kayayyaki musamman suna buƙatar haɗuwar abubuwa kamar rance mai sauƙin samu, ingantacciyar wutar lantarki, sufuri mai kyau da kuma samun kayan da ake amfani da su wajen samar da kayayyaki cikin sauƙi domin su faɗaɗa ayyukan su.

Saboda haka, tabbatar da samun ingantuwar yanayin kasuwanci na buƙatar tafiya tare da rage tsare-tsaren da ke ƙara tsadar gudanar da ayyuka, domin farfaɗowar tattalin arzikin ceta haifar da ƙarin zuba jari daga ɓangaren masu zaman kan su.

A halin yanzu, sabon binciken CBN ya nuna cewa yanayin kasuwanci a Nijeriya na ci gaba da inganta.

Zan rage farashin man fetur zuwa N200 duk lita idan ƴan Najeriya su ka zaɓe ni a 2027- Adebayo Ɗan takarar shugaban ƙasa...
06/09/2026

Zan rage farashin man fetur zuwa N200 duk lita idan ƴan Najeriya su ka zaɓe ni a 2027- Adebayo

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar SDP, Adewole Adebayo, ya yi alkawarin rage farashin man fetur, iskar gas da man jiragen sama zuwa N200 kan lita cikin shekara guda idan aka zaɓe shi a 2027.

Adebayo ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) a Abuja, inda ya ce za a cimma hakan ta hanyar farfaɗo da matatun man fetur na cikin gida da kuma samar da yanayi mai kyau ga ƙananan matatun mai.

Ya kuma ce gwamnatinsa za ta dawo da tsarin tallafin man fetur na baya, inda ake ware ganga 450,000 na ɗanyen mai domin amfanin cikin gida, sannan a yi amfani da kuɗin da ake samu daga sauran sinadaran man wajen daidaita farashin.

Dan takarar ya ce muhawarar cire tallafin mai na ɗauke hankalin gwamnati daga muhimmin abin da ya kamata a mayar da hankali a kai, wato samar da isasshen ƙarfin tace ɗanyen mai a cikin Najeriya.

Adebayo ya kuma yi alkawarin inganta sufurin jama’a da layin dogo, tare da rage kuɗin sufuri da gidaje ga ma’aikata, da samar da ilimi da kiwon lafiya kyauta idan SDP ta samu nasarar kafa gwamnati.

Ya ce gwamnatin SDP za ta kuma mayar da hankali kan noma da samar da wadataccen abinci domin rage tsadar rayuwa.

06/09/2026

Magana Cikin Hikima

Address

Number 17B Sidi Plaza Behind Old NEPA Off Sulemanu Barau Road Suleja
Abuja
910101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zuma Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zuma Times Hausa:

Shortcuts

Share