DAN ANKA News

DAN ANKA News All praise be to almighty allah

DA DUMI-DUMI: Babban Bankin Najeriya (CBN) Zai Kaddamar da Sabbin dokoki Kan Ma'amalolin ATM Daga 1 Ga Maris, 2025 Babba...
11/02/2025

DA DUMI-DUMI: Babban Bankin Najeriya (CBN) Zai Kaddamar da Sabbin dokoki Kan Ma'amalolin ATM Daga 1 Ga Maris, 2025

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya shirya fara sabon tsarin cajin kudade kan ma'amalolin ATM daga ranar 1 ga Maris, 2025. Ga yadda sabon tsarin zai kasance:

- ATM da ke cikin banki (On-site ATMs): Za a caje Naira 100 kan duk cire kudi har N20,000.

- ATM da ke wajen banki (Off-site ATMs): Za a caje Naira 100 tare da karin caji da ba zai wuce Naira 500 ba kan duk cire kudi har N20,000.

- ATM na bankin da aka buɗe asusu a ciki (On-Us transactions): Ba za a caje komai ba idan kwastoma ya cire kudi a ATM na bankinsa.

Wannan sabon tsari yana da nufin samar da daidaito a tsarin hada-hadar kudi a Najeriya.

KBC Hausa ta shafin Comr Abba Sani Pantami

Sojoji Sun Kashe Mai Safarar Mak**ai A Zamfara.Dakarun Operation Fansan Yanma sun yi nasarar kashe wani da ake zargin ma...
10/02/2025

Sojoji Sun Kashe Mai Safarar Mak**ai A Zamfara.

Dakarun Operation Fansan Yanma sun yi nasarar kashe wani da ake zargin mai safarar mak**ai ne a lokacin da yake kokarin tserewa bayan yayi artabu da jami'an tsaro. An k**a shi da mak**an da yake da nufin isarwa ga ‘yan bindiga.

Lamarin dai ya faru ne a wani samame da aka kai cikin dare a garin Nasarawa Burkullu a jihar Zamfara, inda jami’an tsaro da ke aiki da bayanan sirri s**a k**a wanda ake zargin yana safarar mak**ai daga garin Anka.

Da ganin sojojin, wanda ake zargin ya yi yunkurin tserewa amma cikin gaggawa aka kawar da shi.

Binciken farko da aka yi ya tabbatar da cewa yana jigilar bindigogi da alburusai ne zuwa ga kungiyoyin masu aikata laifuka da ke aiki a yankin, inda kungiyoyin ke kukan cewa sun samu karancin albarussai da mak**ai yayin da sojoji ke kara kaimi a kansu.

Daga shafin:- DAN

Gwamnatin sojin Nijar ta bai wa Bokaye kujera guda domin zama wakili a taron ƙasar da za'a fara a ƙarshen wannan makon. ...
10/02/2025

Gwamnatin sojin Nijar ta bai wa Bokaye kujera guda domin zama wakili a taron ƙasar da za'a fara a ƙarshen wannan makon. Wannan na daga cikin kujerun da aka warewa kungiyoyin addinai daban daban domin shiga taron wanda zai tatatuna makomar kasar. Sauran kujerun da baiwa ƙungiyoyin addinin sun nuna cewa an bai wa al'ummar Musulmi 16, sai kuma Kiristoci da aka bai wa kujeru guda 3. Ana saran gudanar da taron ne a cikin kwanaki 5 daga 15 ga watan nan zuwa 19.

DAN

'Ɗan Majalisar Najeriya dake wakiltar mazabar Bichi a Jihar Kano, Abubakar Kabir-Abubakar ya dauki malaman makaranta 200...
10/02/2025

'Ɗan Majalisar Najeriya dake wakiltar mazabar Bichi a Jihar Kano, Abubakar Kabir-Abubakar ya dauki malaman makaranta 200 aiki, kuma yana biyansu daga aljihunsa domin taimakawa wajen bunkasa ilimi a yankin. Abubakar ya kuma ƙarawa wasu malaman dake aiki a yankin 118 albashin da ake biyansu daga naira 18,000 a wata, zuwa naira 60,000. Wannan mataki na daga cikin yunkurin ɗan majalisar na tallafawa karatun Firamare da Sakandare da kuma Islamiya. Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito shugaban Gidauniyar Ɗan Majalisar dake kula da aikin, Habibu Usman-Abdu na cewa tun daga shekarar 2020 ya fara wannan aikin na biyan malaman da mutane 106, kafin a kara yawansu zuwa 118. Usman-Abdu ya ce daga cikin malaman akwai 50 dake makarantn Islamiya da 130 a firamare da 130 a kananan Sakandare, sai kuma 40 a manyan Sakandare.

📷 Daily Nigerian

YANZU-YANZU:  ƙudirin kafa sababbin jihohi 31 da aka gabatar wa Majalisar Wakilai ya rushesu tun kafin a fara tantance s...
10/02/2025

YANZU-YANZU: ƙudirin kafa sababbin jihohi 31 da aka gabatar wa Majalisar Wakilai ya rushesu tun kafin a fara tantance shi.

Wani babban jami’in majalisar, wanda bai so a ambaci sunansa ba, ya bayyana cewa babu ɗaya daga cikin ƙudurorin da s**a bi tsarin da kundin tsarin mulki ya tanada. Saboda haka, ba za su iya karɓar tsarin ba gaba daya.

Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai kuma Shugaban Kwamitin Bita Kan Kundin Tsarin Mulki, Benjamin Kalu, ya bayyana haka a ranar 6 ga Fabrairu cewa majalisar ta karɓi ƙudirin kafa sababbin jihohi 31. Sai dai ya jaddada cewa dole ne a sake gabatar da su bisa tsari wanda zai da ce da kundin tsarin mulki kafin nan da ranar 5 ga Maris, 2025.

Sai dai wani ɗan majalisa da ya yi magana da TheCable ya bayyana cewa waɗannan ƙudurori sun mutu tun kafin a fara tattaunawa a kansu.

A cewar sa, bisa tanadin Sashe na 8(1)(a) na Kundin Tsarin Mulki, matakin farko na kafa jiha shi ne tattara sa hannun kashi biyu bisa uku (⅔) na ‘yan majalisar da aka zaɓa daga yankunan da abin ya shafa, a majalisun dokoki na ƙasa da na jihohi. Wannan ba a yi shi ba, don haka ƙudurin ya rushe.

"An gabatar da waɗannan ƙudurori ne ta hanyar rubuce-rubuce daga jama’a da kuma dokokin mambobi na kashin kansu. Wannan ne sakataren kwamitin ya sanar da majalisa. Mataimakin kakakin majalisa ya karanta wasikar kuma ya jaddada cewa an samu matsala a wajen bin ka’ida. Amma wasu kafafen yaɗa labarai sun yi kuskure wajen bayar da rahoto cewa majalisa ta kafa sababbin jihohi 31," in ji ɗan majalisar.

10/02/2025

SABON LABARI
Akwai yiyuwar ƙara Samun Labari mai daɗi daga yankin Nasarawa, Muci Gaba da Addu'a

30/12/2024

Iran has confirmed the arrest of Italian journalist Cecilia Sala, state news agency IRNA said, citing the Iranian Ministry of Culture. IRNA said that Sala had been detained on December 19 after "violating the laws of the Islamic republic of Iran."

30/12/2024

Kamfanin dillancin labaran iqna ya labarta cewa, ya nakalto daga ma'aikatar al'adu ta kasar Iran cewa, Iran ta tabbatar da kame 'yar jaridar kasar Italiya Cecilia Sala. IRNA ta ce an tsare Sala ne a ranar 19 ga watan Disamba bayan da ta karya dokokin Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

24/12/2024

A TASHARMU TA DAN ANKA News

Zamuci Gaba Da Kawo Maku Labarai Da Rahotanni Daidai Sauransu Kukasance Tareda Tashar DAN ANKA News

A Matsayinka Na Matashi Kuma Mai Ilmi Da Tunani Wannan Sam Bai Kamata Damuba, Mu Aje Batun Siyasa Magana Ake Ta Tsaro Wa...
25/06/2024

A Matsayinka Na Matashi Kuma Mai Ilmi Da Tunani Wannan Sam Bai Kamata Damuba, Mu Aje Batun Siyasa Magana Ake Ta Tsaro Wanda Yashafi Garina, Garinka, Mahaifata, Mahaifarka, Tushena, Tushenka, Abun Bugun Gabanmu💪 Wato Anka Gari Mai Albarka Mai Cikakken Tarihi🙅‍♂

Idan Zamuci Gaba Da Siyasantar Da Komai Musamman Lamarinnan Na Tsaro Da Wasunmu Ke Dauka Bakomaiba, Wata Rana Za'a Cutar Dani, Dakai, Damu A Daidai Lokacinda Mafi Yawanmu Basuda Lokacin Fitowa Su Fadawa Duniya Damuwarsu, Kuma Koda Mun Fito Alokacin Wadansu Bazasu Sauraremuba🤦‍♂

Kuma Idan Muna Ganin Wannan Abun Dayake Faruwa Bai Shafeniba, Ko Bai Shafekaba, Tunda Ba'a Taba Danginkaba, Ko Dangina To Kajira, Mujira, Sannu A Hankali Zaizo Kanka, Alokacinda Bakada Wata Dabara

Fatanmu Akullun Allah Madaukakin Sarki Yabamu Zaman Lafiya Ko A Gwamnatin Waye, Domin Sai Ana Zaune Lafiya Za'a Iya Gudanarda Komai Na Rayuwa

Idan Mun Samu Zaman Lafiya, Yak**ata Mudawo Mudaba Shuwagabanninda S**ayi Ruwa Da Tsaki Domin Ganin Munsamu Zaman Lafiya, Daga Nan Sai Muyi Tsaye Tsayin Daka Domin Mubasu Dama Suje Su Wakilcemu, Domin Sune Wadanda S**a Damu Damu

Ubangiji Allah (SWA) Kabamu Lafiya Da Zaman Lafiya A Garina Jahata Dama Kasa Baki Daya Amin 🤲

23/06/2024

Wata Rana MANZON ALLAH (S.A.W) YA CE: IDAN AL'UMMATA SU KA AIKATA ABUBUWA GUDA GOMA SHA BIYAR (15), TO A SAURARI ZUWAN BALA'I

1. Idan dukiyar Baitil-Mali ta kasance Ganima ga wasu mutane.
A saurari zuwan Bala'i

2. Idan Amana ta kasance abin-cinyewa, wato aka wofintar da ita, ba'a bayar da ita k**ar yadda shari'a ta umurta.
A saurari zuwan Bala'i.

3. Idan ma su dukiya su ka dauki Zakka k**ar wani Haraji ne aka dora akansu.
A saurari zuwan Bala'i.

4. Idan aka wayi gari Mutum ya na girmama abokinsa, ya na wulakanta Mahaifinsa.
A saurari zuwan Bala'i.

5. Idan Mutum ya na girmama Matarsa, ya na wulakanta Mahaifiyarsa.
A saurari zuwan Bala'i.

6. Idan aka koma ana koyon Karatun
Al - Qurani ba don Allah ba, sai don saboda Duniya.
A saurari zuwan Bala'i.

7. Idan ya kasance ana girmama Mutum saboda sharrinsa.
A saurari zuwan Bala'i.

8. Idan ya kasance ana shan Giya iri Daban-Daban.
A saurari zuwan Bala'i.

9. Idan ya kasance ana ado da Alharini bayan Shari'a ta hana.
A saurari zuwan Bala'i.

10. Idan ya kasance ana Cudanya tsakanin Maza da Mata ana Rawa.
A saurari zuwan Bala'i.

11. Idan ya kasance an bullo da sabbin kayan Kade-Kade da Goge-Goge.
A saurari zuwan Bala'i.

12. Idan ka ji ana daga sauti ana hayaniya a Masallatai.
A saurari zuwan Bala'i.

13. Idan aka samu Al'ummar karshen zamani su na zagin wadanda s**a gabacesu.
A saurari zuwan Bala'i.

14. Idan Zinace Zinace su ka yawaita.
A saurari zuwan Bala'i.

15. Idan mutane s**a halatta cin Riba.
A saurari zuwan Bala'i.


Wannan duk halayenmu ne yanzu
Kafin Mu Zagi Shugabanni Mu Fara Gyara Kawunanmu Dan Allah

Allah ka Karemu Ka Tsare Mana Imanin Mu ￶👐🏾

23/06/2024

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Mubarak Sani Anka, Abdul'rahman Musa Ubandoma, Alh Bello Baraya

Address

Zamfara
Anka
ZMF

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DAN ANKA News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to DAN ANKA News:

Share