Matattarai Labarai

Matattarai Labarai Kamfanin jarida

RANAR HAUSA TA DUNIYASu Waye Hausawa?Daga Al-mansoor GusauHausa al'umma ce dake zaune a Arewa maso yammacin tarayyar Nij...
26/08/2022

RANAR HAUSA TA DUNIYA

Su Waye Hausawa?

Daga Al-mansoor Gusau

Hausa al'umma ce dake zaune a Arewa maso yammacin tarayyar Nijeriya da kuma kudu maso yammacin Jamhuriyyar Nijar.

•Al'umma ce mai ɗimbin yawa, sun bazu a cikin ƙasashen Afirka da ƙasashen Larabawa, kuma a al'umma ce mai matukar hazaƙa, aƙalla akwai sama da mutane miliyan hamsin (50) wadanda harshen Hausa shi ne asalin harshen da su ke magana da shi.

•A tarihi ƙabilar Hausawa na tattare a salasalar birane watau alqarya. Hausawa dai sun sami kafa daularsu ne tun daga shekarun 1300's, sa'adda s**a sami nasarori da dauloli k**ar su daular Mali, Songhai, Borno, da kuma Fulani, a karni na 19 Hausawa suna amfani da Doki ne domin yin sifiri da balaguro.

•Mutane kimanin sama da miliyan 50 ne ke magana da harshen Hausa a Najeriya, Nijar, Arewacin Gana da kuma wasu al’umma daga yankin Kaolack a Senigal har zuwa Khartum dake ƙasar sudan, asalin inda zuciyar Hausawa take shi ne garin Kano, Katsina da Sokoto.

•Asalin al’ummar Hausawa maguzawa ne, amma sun shafe daruruwan shekaru da karbar addinin musulunci ƙarƙashin mulkin sarakunan Haɓe, wanda s**a daina yin bori da tsubbace-tsubbace, zuwan Shehu Usman Ɗan Fodio ne yasa ya kawar da mulkin wadannan sarakunan na ƙasar Hausa, ta hanyar yaƙar Hausawa da sarakunansu na haɓe a Gobir, Zazzau da wasu yankunan ƙasar hausa. Wanda wannan juyin mulkin ne yasa Usman Ɗan Fodio ya kafa Daular Fulani a Hausa Fulani a ƙasar Hausa Kuma Hakan yasa masarautun ƙasar Hausa sun kasance a ƙungiyar Tuta ɗaya na Usman Ɗan Fodio.

•Hausawa suna kiran al’adunsu da al’adan gargajiya, wacce su ke yi duk shekara, ko a talabijin ko Bidiyo, ko kuma aikace cikin al’amuran yau da kullum.

•Na daga cikin rubutun Hausawa, suna yin rubutu ne asali da Ajami, rubutu ne da haruffan larabci amman a luggar hausa, kuma suna rubutawa ne a fallen takarda.

Harshen Hausa yana da ire-ire da yawa k**ar haka:

GABACIN HAUSA.

Kanawa
Kataguwa
Hadejawa
Gumelawa
Katsinawa

YAMMACIN HAUSA.

Daurawa.
Sakkwatawa.
Katsinawa.
Kurfayawa.
Gobirawa.
Adarawa.
Kebbawa.
Zamfarawa.

Babu ko shakka harshen Hausa, rayayyen harshe ne da Allah (SWT) ya daukaka kima da darajarsa a duniya, domin kuwa shi kadai ne harshen da ke iya aron haruffan wani harshe ya yi rubutu da shi da harshensa na Hausa, mai asalin harshen ya kasa karanta abunda Bahaushe ya rubuta da haruffansa.

Ajamin Larabci: - Bahaushe ya ari haruffan Larabci ya mayar da su na Hausa, wanda Balarabe ba zai iya karantawa ba, kuma ya tabbatar da haruffansa ne aka juya.

Ajamin Boko: - Haka zalika Bahaushe ya ari haruffan Boko na Ingilishi ya rubuta magana da harshensa na Hausa Bature ba zai iya karantawa ba, dole sai dai kallo ko kuma ya nemi sani a gurin al’ummar Hausawa.

Al’ummar Hausawa ne ko da Addinin Musulunci ya shigo kasarsu ta Hausa ya tarar da su da kyawawan halaye da dabi’un da su ka yi dai-dai da koyarwar Addinin Musulunci, shi ya sa ma Bahaushe ke yi wa kabilun Nijeriya da su ka karbi Addinin Musulunci kallon hadarin kaji:

MISALI:

•Zumunci.
•Kunya.
•Kara.
•Taimako.
•Kyamar zina.
•Kyamar sata.
•Auren mace fiye da daya.

- Kai rabu da shi Musulunci Bayarrabe.
- Kai ai ka san daga baya ya Musulunta.
- Kai ai ka san asalinsu ba Hausawa ba ne.

Muna rokon Allah (SWT) ya cigaba da daukaka kima da darajar al’ummar Hausawa a Nijeriya, Nijar da duniya baki dayanta, Allah (SWT) ya kawo zaman lafiya, kwanciyar hankali, walwaha, arziki a cikin al’ummar Hausawa da Addinin Musulunci, Allah (SWT) ya zaunar da Arewacin Nijeriya da Kudancin Nijar da daukacin kasashen lafiya alfarmar Annabi Muhammad (SAW).

AL’MANSOOR GUSAU,
ADVOCATE.

26 August 2022.

Jawabin Atiku Abubakar Na Farko Amatsayin Dan Takarar Shugaban Kasa Na PDP Azaben 2023Daga Abubakar A Adam BabankyautaYa...
29/05/2022

Jawabin Atiku Abubakar Na Farko Amatsayin Dan Takarar Shugaban Kasa Na PDP Azaben 2023

Daga Abubakar A Adam Babankyauta

Yau ranace mai matukar tarihi kuma ranace da zata tabbatar da cewa Nijeriya ta kalli alkibula a zaben 2023, Cewar Atiku Abubakar

Bayan nasararsa a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya aika da sakon murna ga yan Nijeriya.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce ya yi farin ciki sosai da kasancewar sa wanda zai daga tutar jam'iyyar adawa ta PDP a zabe mai zuwa.

Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP a babban zaben kasar mai zuwa, Alhaji Atiku Abubakar ya sha alwashin hada kan kasar nan.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya kuma dauki alkawarin magance matsalolin tsaro da na tattalin arziki da ke tunkarar kasar.

Atiku ya kuma yiwa gwamnatin APC wankin babban bargo cewa ta lalata duk wasu nasarori da gwamnatin PDP ta shimfida.

Adaran jiya ne jam'iyar adawa ta PDP ta sanar da nasarar Alhaji Atiku Abubakar na lashe zaben fidda gwani na shugaban kasa karkashin inuwar jam'iyar ta PDP

Bayan sanar da nasarar Alhaji Atiku Abubakar a matsayin dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar jam'iyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya sha al'washin maido da Nijeriya cikin haiyyacin ta idan har yan Nijeriya s**a zabe shi a matsayin shugaban kasa 2023.

Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da yake bayar da jawabin amincewarsa bayan an ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwanin shugaban kasa na PDP.

Atiku ya caccaki jam’iyyar APC kan yadda ta mayar da nasarorin da jam’iyyar PDP ta samu a lokacin da ta ke rike da madafun iko baya, inda ya yi alkawarin gyara su idan aka sake zabar su.

Atiku Abubakar Ya ce: “Zan magance matsalolin tsaronmu a kasar nan. Na kuma dauki alkawarin tunkarar matsalolin tattalin arzikinmu. Jam’iyyar PDP ta sanya Nijeriya ta zama daya daga kasashe masu ci gaba da wadata a nahiyar Afirka.

Mun aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziki da s**a kawo ayyukan yi, da wadata a kasar nan. Amma Jam’iyyar APC ta shigo ta goge duk wadannan nasarori. Shi ya sa na ce yau rana ce mai matukar tarihi a Nijeriya.

Domin hakan zai ba mu damar gyara duk wani rashin shugabanci na gwamnatin APC.

Ya kuma nemi hadin kan sauran yan takarar da s**a fadi a zaben fidda gwani, yana mai cewa babban abun da ke gaban mu yanzu shine kwato Nijeriya daga hannun jam’iyyar APC mai mulki.

Domin dukkan mu munyi imani cewa Nijeriya ta fada cikin wani hali a karkashin inuwar mulkin jam'iyar APC saboda haka ya k**ata musani cewa Nijeriya da yan Nijeriya na matukar bukatar hadin kan mu domin kawo karshin mulkin APC a yayin zaben 2023.

Atiku ya ce: "Bari na yi amfani da wannan damar wajen kira ga abokan takarata. Sannan na basu tabbacin cewa a shirye nake na hada kai da aiki tare da su sannan na basu damar taka rawa a wannan jam'iyyar da gwamnatinmu ta gaba.

Saboda haka ’yan uwana, ina son in yaba da kokarinku na zurfafa tsarin dimokuradiyya a tsarin wannan jam’iyya. Zaben fidda gwani ne mai inganci. Don haka, na yaba muku akan haka kuma ina fatan yin aiki tare da ku kai da kai. Ta yadda za mu gina wannan jam’iyyar tare zuwa matakin da za mu iya kwace mulki.

Atiku Abubakar ya kuma bayyana cewa fafutukar sake gina Nijeriya tare da inganta ta zuwa matakin ci gaba ya fara aiki daga yanzu da ya lashe tikitin takarar shugabancin kasar.

Acikin jawabin nasa Alhaji Atiku Abubakar ya ce yan Nijeriya zasuyi alfahari da shi a matsayin shugaban kasar Nijeriya idan har s**a zabe shi 2023.

Bashir Ahamad Kenan...........Wato jama'a shima Bashir Ahamad ya dage sai ya zama dan Majalisar Wakilan Nijeriya mai wak...
07/05/2022

Bashir Ahamad Kenan...........

Wato jama'a shima Bashir Ahamad ya dage sai ya zama dan Majalisar Wakilan Nijeriya mai wakiltar Gaya-Ajingi-Albasu a karkashin jam'iyar APC 2023

Saidai kuma khas Bashir Ahamad ya manta cewa shi mutum ne mai halin dan tsako samu kaki dangi.

Domin Bashir Ahamad ya zama babban mataimaki na musamman ga shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari a bangaran sabbin kafufin sada zumunta a 2015 amma har kawo yanzu da nake wannan rubutun Bashir Ahamad bai taimaki yan Social Median jihar kano ba bare muce Nijeriya.

Yau kusan shekaru 7 kenan Bashir Ahamad na aiki da shugaba Buhari a matsayin mataimaki na musamman bangaran sabbin kafufin sada zumunta amma ko sau daya Bashir Ahamad bai taba tunanin ya taimaki masoya kuma magoya bayan shugaba Buhari yan Social Media ba.

Bashir Ahamad Kenan" Yanzu a haka kake tunanin zama dan Majalisar Wakilan Nijeriya? bayan baka da kyakkyawar mu'amala da mutane.

Yanzu haka Bashir Ahamad baida kyakkyawar halaka da yan Social Median Gaya-Ajingi-Albasu didda kasancewar shi hadimin shugaba Buhari bangaran Social Media wanda hakan ya tilasta mai tallata kanshi da kanshi a cikin kafafen sada zumunta.

Saboda haka nake bama al'ummar kana nan hukumomin Gaya-Ajingi-Albasu shawarar cewa su waye kafun a masu kanta waye domin na tabbata cewa Bashir Ahamad kanta waye yake shirin masu 2023.

Daga Abubakar A Adam Babankyauta.

01/04/2022

Babu labarin ganin jinjirin watan Ramadana ya zuwa yanzu, Cewar kwamitin ganin wata

Daga Abubakar A Adam Babankyauta

A daren yau Juma'a ne a kwamitin ganin wata na kasa ya bukaci musulmai a Najeriya su fara duban jinjirin watan Ramadana.

Ya zuwa yanzu, kwamitin ya ce bai samu labarin ganin wata ba daga wasu sassan jihohin kasar nan.

Kwamitin ya bayyana haka ne a cikin wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

A cewar bayanin da ke neman jin ta bakin sauran al'umma, an ce:

Ya zuwa yanzu babu rahotannin da aka samu daga Bauchi, Gombe, Azare, Misau, Numan, Lagos, Kaduna, Abuja, Bajoga, Nafada, Maiduguri da dai sauransu.

Kwamitin ya kuma nemi jama'a da su ba da bayani sahihi daga yankunansu game da ganin jinjirin watan na Ramadana.

Jama'a ku tayamu yada wa domin sakon yakai zuwa ga al'ummar musulmai.

DA DUMI-DUMINTA: Wata Budurwa 'Yar Jihar Bauchi Ta Fara Tattaki Daga Bauchi Zuwa Abuja A Kafa, Domin Bayyana Goyon Bayan...
31/03/2022

DA DUMI-DUMINTA: Wata Budurwa 'Yar Jihar Bauchi Ta Fara Tattaki Daga Bauchi Zuwa Abuja A Kafa, Domin Bayyana Goyon Bayanta Ga Dan Takarar Gwamnan Jihar Bauchi A Jam'iyyar APC Farouk Mustapha

Idan Baku Manta Ba, A Kwanakin Baya Mun Ruwaito Muku Cewa 'Yar Gidan Dan Takarar Gwamnan Jihar Bauchi A Jam'iyyar APC Hamdiyya Farouk Mustapha, Ta Fito Cikin Talakawa A Wurin Taron Jam'iyyar Da Ya Gudana A Abuja

Wane Fata Zaku Yiwa Wannan Budurwar?

DAILY NEWS HAUSA

Indai Gudun Hawala Kake Daga Yau Ta Kare, Yan Ta'addan Daji Sun Fadawa Wani Magajin Gari Kafun Su Kashe ShiDaga Abubakar...
21/03/2022

Indai Gudun Hawala Kake Daga Yau Ta Kare, Yan Ta'addan Daji Sun Fadawa Wani Magajin Gari Kafun Su Kashe Shi

Daga Abubakar A Adam Babankyauta

Wato jama'a yan bindigan daji masu hallaka jama'a sun kashe hakimi sannan s**a tayar da garin shi baki daya a cikin jihar Zamfara.

Majiyar mu ta labarta mana cewa yan bindiga sun kashe aƙalla mutum 25 da s**a haɗa da Hakimi da wasu sarakunan gargajiya a ƙaramar hukumar Bukkuyyum a jihar Zamfara.

Yan bindigar sun abka ƙauyen Ganar Kiyawa ne a ranar Lahadi s**a kashe mutanen, k**ar yadda mazauna yankin s**a shaida wa majiyar mu.

Mutanen garin sun ce yan bindigar sun shiga garin na Ganar Kiyawa ne saman babura, kuma bayan mutane sun tsorata sun fara tserewa, yan bindiga s**a dinga harbinsu, cikin waɗanda aka kashe har da hakimin garin Bala Muhammadu da Magajin gari Sani Salihu da wani bafade da ake kira Sharu.

Wani wanda labarin ya rutsa da sh8 yace da ni da Hakimi da Magajin Gari mun yi gudun kilomita uku, kuma da s**a cimma Magajin Gari s**a tambaye shi me yake wa gudu ya ce wahala, sai s**a ce to ta ƙare, s**a harbe shi," a cewar wani mazauni garin da yake bayar da labarin da ƴar magajin garin da aka kashe ta faɗa masu bayan sun tsira.

Ya ce sun samu gawar mutum 25 da maharan s**a kashe, kuma ana ci gaba da binciken wasu gawawakin a daji."

Ya ce an yi wa gawar mamatan Sallar jana'iza ne a garin Adabka. Ya ce adadin na iya ƙaruwa saboda har yanzu akwai mutanen da ba a gani ba.

Maharan sun tarwatsa garin Ganar Kiyawa inda dubban mutane s**a tsere zuwa wasu ƙauyuka makwabta.

Hakimin Adabka ya shaidawa BBC cewa mutanen da ke cikin garinsa sun kai kusan mutum 3,000.

A cikin wata sanarwa bayan kai harin, gwamnatin jihar Zamfara ta jajantawa mutanen garin tare da bayar da umarnin kai masu tallafi.

Muna rokon ubangiji Allah ya nuna mana karshen wannan lamarin tare da azurta kasar mu Nijeriya da zaman lafiya mai daurewa.

Wasu Gungun Matasa Sun Gano Wata Burdurwa Mai karyan Gurgunta Acikin Jihar LagosDaga Abubakar A Adam Babankyauta Dubun w...
13/03/2022

Wasu Gungun Matasa Sun Gano Wata Burdurwa Mai karyan Gurgunta Acikin Jihar Lagos

Daga Abubakar A Adam Babankyauta

Dubun wata matashiyar yarinya da ke karyar gurgunta tare da zama akan keken guragu ya cika a jihar Lagos.

Mutane sun cika da mamaki bayan wasu gungun matasa sun tilastawa wata budurwar yarinya mai karyan gurgunta ta tashi tsaye daga kan keken guragun kuma ya bayyana karara cewa ba gurguwa bace.

An tilasta mata yin tafiya sannan mutanen da ke wajen s**a dunga mamakin yadda ta mikye tsaye da kafafunta garas.

Majiyar mu ta labarta mana cewa jama’a sun tofa albarkacin bakunansu bayan bayyanar wani bidiyo na wata mabaraciya da ta yi ikirarin cewa ita gurguwa ce don kawai ta tara kudi a harkar bara.

Yarinyar na zama ne a kan keken guragu wanda musamman ta tanade shi domin yin wannan harka da kuma yawo a yankin Ikeja tana rokon kudi daga hannun mutane a matsayin mai nakasa.

Lokacin da wasu matasa da suke lura da ita s**a k**a ta, sai s**a tilasta mata sauka daga keken guragun sannan s**a sa ta yin tafiya. Tana sauka, sai ya bayyana karara cewa duka kafafuwanta guda biyu lafiya suke babu abun da ya same su.

Awajen da abun ya faru daruruwan mutane sun bayyana matsayar su akan bama almajirar bara inda wasu s**a ce bazasu kara bama kowani mabaraci sadaka ba.

Wato jama'a irin wannan sana'ar ta barar karya tayi karfi a cikin Nijeriya musamman manyan buranan Nijeriya k**ar Lagos- Abuja- kaduna- Kano- Abia- Delta- Enugu da dai sauran su.

Muna rokon ubangiji Allah ya baramu da san zuciya.

Muna Kira Ga CSP Usman Shugaba Da Ya Tsaya Takarar Gwamnan Jihar Kaduna 2023, Cewar Jagoran Gungun Matasan Jihar KadunaD...
08/03/2022

Muna Kira Ga CSP Usman Shugaba Da Ya Tsaya Takarar Gwamnan Jihar Kaduna 2023, Cewar Jagoran Gungun Matasan Jihar Kaduna

Daga Abubakar A Adam Babankyauta

Jagoran gungun matasan jihar kaduna Haruna Jibril ya yi kira ga babban ADC uwar gidan shugaban Nijeriya Hajiya Aisha Muhammadu Buhari CPS Usman Shugaba daya gaggauta neman kujerar gwamnan jihar kaduna 2023.

Acewar Haruna Jibril babban dogarin uwar gidan shugaban Nijeriya Hajiya Aisha Muhammadu Buhari CSP Alhaji Usman Shugaba ya chanchanci ya zama gwamnan jihar Kaduna a 2023

Domin CSP Usman Shugaba mutum ne" Na mutane wanda yasan yak**ata a cikin dukkanin al'amuran shi.

Haruna Jibril yaci gaba da bayyana cewa duk wani matashin dake cikin jihar kaduna babu shakka alkairin CSP Usman Shugaba ya kai gareshi walau kai tsaye ko kuma ta bayen fage.

Domin CSP Usman Shugaba ya kawo abubuwan more rayuwa ta fuskoki daban daban musamman fannin ilimin yara da kuma matasa a cikin jihar kaduna baki daya.

Makusanta CSP Usman Shugaba sun sanshi da taimakon marayu wanda suke mai lakabi da garkuwan marayu.

Akarshe Haruna Jibril ya roki Allah ya tabbatar da CSP Usman Shugaba a matsayin gwamnan jihar Kaduna.

Ƴan Ta'adda Sun Kashe Mutane 62 A Garin Zuru Dake Jihar Kebbi, Da Wasu Yankuna A Jihar Neja..Ƙungiyar "Arewa Media Write...
08/03/2022

Ƴan Ta'adda Sun Kashe Mutane 62 A Garin Zuru Dake Jihar Kebbi, Da Wasu Yankuna A Jihar Neja
..Ƙungiyar "Arewa Media Writers" tana kira ga gwamnatin Najeriya da ta gaggauta kawo ƙarshen matsalar rashin tsaron da ya addabi yankin mu na Arewa.

Daga Ƙungiyar "Arewa Media Writers"

Ƙungiyar marubutan Arewa "Arewa Media Writers" ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar na ƙasa Comr Abba Sani Pantami, tayi Allah wadai da kisan da ƴan ta'adda s**a yiwa al-ummar garin Zuru dake jihar Kebbi da wasu yankuna na jihar Neja da s**a haɗa da ƙaramar hukumar Rija'u da sauran su.

"Arewa Media Writers" tayi takaici da jimamin faruwar wannan mummunan ta'addacin da aka yiwa ƴan uwan mu dake yankunan.

Haka zalika ƙungiyar tana sake kira da kakkausan harshe ga gwamnatin Najeriya da ta gaggauta kawo ƙarshen matsalar rashin tsaron da ya addabi yankin mu na Arewa, don al'ummar yankin su zauna cikin kwanciyar hankali.

Ƙungiyar "Arewa Media Writers" tayi Addu'ar samun rahama ga mamatan da s**a rasa rayukan su, wa ƴanda s**a rasa ƴan uwansu Allah ya basu ikon jure rashin.

Daga ƙarshe Ƙungiyar tana Addu'a tare da rokon Ubangiji ya kawo mana zaman lafiya mai ɗorewa a yankin mu na Arewa dama ƙasar Najeriya baki ɗaya. Amin

Hattara Al'ummar MusulmaiDaga Abubakar A Adam Babankyauta Muna masu kira ga al'ummar musulman Nijeriya da ma na duniya b...
05/03/2022

Hattara Al'ummar Musulmai

Daga Abubakar A Adam Babankyauta

Muna masu kira ga al'ummar musulman Nijeriya da ma na duniya baki daya da su kula da irin kalan kayan da za su siya su sa a jikin su. Domin akwai sabbin kayan sawa t-shirt t-shirt da s**a shigo cikin Nijeriya musamman kudancin Nijeriya masu dauke da sunan Allah a jikin su.

Wannan daya daga cikin irin t-shirt din da muka gano kenan wanda wani bawan Allah Musulmi ya siyo domin ya yi ado da ita anan cikin Abuja.

Lallai ya k**ata al'ummar Musulmai su sa ido akan irin kayan da zasu siyo susa a jikin su domin gudun kada susa kaya masu sunan Allah da Manzon Allah S.A.W a jikin su.

Ni Ba Tsoho Bane, Matashi Ne Mai Jini A Jika Domin Zan Iya Mulkar Nijeriya Har Inkai Ta Tudun Na Tsira, Cewar TinubuDaga...
28/02/2022

Ni Ba Tsoho Bane, Matashi Ne Mai Jini A Jika Domin Zan Iya Mulkar Nijeriya Har Inkai Ta Tudun Na Tsira, Cewar Tinubu

Daga Abubakar A Adam Babankyauta

Jagoran jam'iyyar APC kuma mai neman takarar kujerar shugaban kasa a zaben 2023, Bola Tinubu ya bayyana kansa a matsayin matashi mai jini a jika.

Tinubu ya jaddada cewar zai iya jagorantar kasar harma ya kai ta ga matakin ci gaba.

Tsohon gwamnan na jihar Lagas ya kuma bayyana cewa APC za ta ci gaba da kare ra’ayin yan Nijeriya a gida da waje.

Tinubu ya yi wannan furucin ne a daidai lokacin da ake kiraye-kirayen a baiwa matasa damar yin mulkin Nijeriya.

Da yake jawabi Tinubu ya tabbatar da cewar yana da karfin jagorantar Nijeriya yace yana da ikon yi wa Nijeriya hidima da kuma daukaka darajar ta a fadin duniya.

Ya fada ma magoya bayansa a wani taro da aka yi kwanan nan cewa APC za ta ci gaba da kare ra’ayin yan Nijeriya a gida da wajen Nijeriya.

Tinubu ya bayyana cewa gani a nan tsaye a gabanku" kuma ni matashi ne mai fafutukar ganin cigaban Nijeriya.

Gwamnatin Nijeriya Ta Fitar Da Iyakokin Da Yan Nijeriya Mazauna Kasar Ukraine Zasu Fada Domin Samun Daukin GaggawaDaga A...
27/02/2022

Gwamnatin Nijeriya Ta Fitar Da Iyakokin Da Yan Nijeriya Mazauna Kasar Ukraine Zasu Fada Domin Samun Daukin Gaggawa

Daga Abubakar A Adam Babankyauta

Wato jama'a rikicin Rasha da Ukraine ya jefa miliyoyin mutane cikin hatsari ciki ko harda yan Nijeriya musamman mazauna kasar Ukraine.

Kamar yadda muka samu labari daga majiyar mu cewa Ofishin Jakadancin Nijeriya a Warsaw, kasar Poland ya sanar tun farko cewa jami’ai da yan sa-kai za su kasance a kan iyakokin Poland da Ukraine domin daukar ‘yan Nijeriya.

A jiya Asabar, 26 ga watan Fabrairu, 2022 gwamnatin tarayyar Nijeriya ta lissafa iyakokin da yan Nijeriya da ke tserewa daga yakin Ukraine da Rasha za su iya bi zuwa Poland.

Dakarun sojojin Rasha sun mamaye babbar birnin Ukraine, Kyiv, sannan an kashe mutane da dama tun bayan da aka fara yaki Tsakanin Rasha da Ukraine.

Abike Dabire-Erewa, shugabar hukumar kula da yan Nijeriya mazauna waje, ta bayyana hakan sannan ta sanar da iyakokin da ya k**ata yan Nijeriya da ke guje ma yakin su bi, k**ar yadda muka samu labari.

Iyakokin da yan Nijeriya zasu fada daga kasar Ukraine sune k**ar haka.

1. Hrebenne-Rawa Ruska,
2. Korczowa-Krawkowiec,
3. Medyka-Szeginie,
4. Budomierz-Hurszew.

Abike ta bayar da tabbacin cewa: “Kungiyoyin sa-kai na Nijeriya, da ma’aikatan ofishin jakadancin Nijeriya, za su kasance a iyakar domin kwashe yan Nijeriya.

Yanzu haka kasar Rasha na ci gaba da kai hare-hare masu zafi a cikin kasar Ukraine wanda hakan ke kara jefa mutane cikin hatsari.

Masana na harshashen cewa wannan yakin da ke faruwa tsakanin Rasha da Ukraine zai iya haifar da yakin duniya karo na uku.

Domin yanzu haka a na tunanin wasu kasashen duniya zasu tsuma hannuwan su a cikin yakin da ke faruwa tsakanin Rasha da Ukraine.

Wasu daga cikin kasashen da ake tsammanin zasu iya tsuma hannun su akan yakin bangarorin biyu sune k**ar haka

BANGARAN UKRAINE
1) USA
2) United kingdom
3) France
4) Germany
5) The Netherlands
6) Italy

BANGARAM RASHA
1) China
2) Iran
3) North Korea Serbia
4) Serbia
5) Venezuela

Wani sabon rahotan da muka samu ya nuna cewa Shugaban kasar Ukraine ya bukace kasashen duniya musamman bangaran Nato da su taya shi yakar kasar Rasha.

Address

Zone 1 Wuse Abuja
Asokoro
08030471966

Telephone

+2348030471966

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Matattarai Labarai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Matattarai Labarai:

Share