
25/07/2025
A wani rikici da ya barke tsakanin yan kasuwa da yan sandan ruwa a karamar hukumar mulki ta yauri a jahar kebbi .A ranar laraba.
Rikicin dai ya faru ne sakamakon wani bangare da aka ware ake ikirarin mallakin yan sanda ne Kuma su keda hurumin yadda s**a so da wurin ,Filin Wanda yan sanda s**a Hana yan kasuwar Sana'a a wurin sai gashi sun baiwa wani damar ajiye shago adaidai wurin lamarin da yan kasuwa s**a Kira da rashin adalci.
Fadan ya barke tsakanin yan sanda da yan kasuwa abin da ya haifar da mummunar rikici da yakai ga yan sanda harba barkonon tsohuwa lamarin da ya haifar da jikkata mutane da dama mussamman mata tsofafi.
A zantawar wakilin bakandamiya Tv da ya yi da shugaban karamar hukumar mulki ta yauri da mataimakin sa , Aliyu Musa da Alh Abubakar shuaibu sun bayyana cewar Izuwa yanzu likitoci suna kokari wurin ganin anceto rayuwar jama'ar da lamarin ya shafa , mussamman wata mata Mai asama wadda da kyar aka samu motsinta.
Mai martaba sarkin yauri Dr. Zayyanu Abdullahi tare da yan majalisar sa da shuwagabannin karamar hukumar mulki ta yauri sunyi alawadai da wannan rikicin Wanda bashi ne karon farko ba ko Ashekarar 2024 fada ya barke tsakanin yan kasuwa da yan sanda lamarin da ya haifar da rashin rayuwa na wani yaro da baiji ba bai gani ba s**a harbeshi .
Saidai azaman sulhu da ya gudana ajiya Alhamis shugaban yan sandan ya yi mubaya'a ga shuwagabanni inda ya yi alkawarin hakan bazata Kara faruwa ba. Sai dai duk da haka sarkin yauri ya Kira kwamishinan yan sanda jahar cp Bello m sani ya labar ta masa abin da ke faruwa Domin daukar mataki.
Daga karshe yan kasuwa da sauran jama'a sunyi Kira da kakkausar murya da a canza wannan shugaban na yan sanda a cewar su Domin ba'a San abinda zai auku gaba ba.