16/05/2026
Cikin iko da hukuncin Ubangiji, mun kammala shirin Mallam Zaki Fellowship, shiri mai albarka da kungiyar Katagum Youth League ta shirya domin horas da matasa a fannonin shugabanci, hidimtawa alβumma, da gina tunani nagari.
Bayan watanni muna karbar horo ta yanar gizo, mun samu damar gudanar da kwanaki uku masu cike da ilmantarwa da ayyukan anfani a garin Azare. A cikin shirin, mun kai ziyara gidan marayu domin kara fahimtar darajar tausayi da hidimtawa jamaβa, mun gudanar da shukar bishiyoyi a Yana domin bada gudunmawa wajen rage dumamar yanayi, mun ziyarci kabarin marigayi Mallam Ibrahim Zaki, sannan muka kammala da tattaunawa mai amfani tare da dalibai a Gamawa.
Hakika, wannan tafiya ta sauya tunani tare da kara mini fahimtar nauyin jagoranci da muhimmancin anfani ga alβumma.
Ina taya dukkan yan uwana fellows murnar kammala wannan tafiya cikin nasara, tare da adduβar Allah Ya sanya albarka a cikin abin da muka koya, Ya bamu ikon anfani da shi wajen amfanar da jamaβa, Ya daukaka mu tare da shiryar da mu zuwa aikata alheri. Amin.