BILAL BN RABAH RADIO

BILAL BN RABAH RADIO Shashine domin labaru da al'amuran yau da kullum na gidan radio BILAL BN RABAH ONLINE .

Jama'a Assalamu Alaikum, BILAL BN RABAH RADIO, KE MUKU SALLAMA DAGA NANBIRNIN BAUCHIN YAKUBU.
27/02/2024

Jama'a Assalamu Alaikum, BILAL BN RABAH RADIO, KE MUKU SALLAMA
DAGA NAN
BIRNIN BAUCHIN YAKUBU.

27/02/2024
**BILAL BN RABAH ONLINE RADIO***SHIRIN LABARUN MAKO*Yau LITININ: 25, ga watan sha'aban,1444h  wanda yayi dai dai 15/ may...
15/05/2023

**BILAL BN RABAH ONLINE RADIO**
*SHIRIN LABARUN MAKO*

Yau LITININ: 25, ga watan sha'aban,1444h wanda yayi dai dai 15/ mayu/2023m.

* DA FARKO GA MUHIMMAN KANUNSU*

(1) Wani malamin Addinin musulunci a jihar Bauchi, Mai suna ustaz sulaiman zakariyya (Abu bassam) ya shawarci iyayen Mata da suyi amfani da darrussan da s**a koya a lokacin gudanar da Azumin watan Ramadan.
(2) Shashen malamai Mata na makarantar Bilal BN rabah ya samu Karin sabowan Malama.
(3) An gargadi dalibai tare da Jan kunnensu akan yawan fita daga ajujuwansu a lokacin karatu.
(4)An ja hankalin dalibai akan suna kokarin dage ababen zaman karatunsu da kuma kujerun malamansu.
(5) A wani 6angare kuma An tunatar da dalibai akan suna kokarin xuwa makarantar da Kayan karatu dana rubutu.
(6) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal BN rabah tayi Kira da Babban murya,akan dalibai su daina tsayuwa akan hanya ko bin hanyar da ba hanyar tapia gida,da zaran an tashi daga makarantar.

**YANZU KAN MAI SAURARO SAI KA GYARA ZAMA DOMIN JIN CIKAKKAN SU WANDA NI SALISU ABUBAKAR DANDIJA ZAN KARANTU***

(1)Wani malamin Addinin musulunci a jihar Bauchi, Mai suna ustaz sulaiman zakariyya (Abu bassam) ya shawarci iyayen Mata da suyi amfani da darrussan da s**a koya a lokacin gudanar da Azumin watan Ramadan da yawuce,malami Mai karantarwan yayi wannan kiranne a lokacin da yake gudanar da wa'azin koron sallah, a babban Masallacin jumu'ar na Bilal bn Rabah dake nassarawa jahun unguwan dim a nan cikin garin Bauchi, a lokacin gudanar da wa'azin koron sallar yasamu halattar kungiyar Mata masu kula da Massalacin da sauran daukacin al'ummah na unguwani,daga karshe sai malamin Addinin sai yayi Addu'ar da fatan Allah yasaka wa kowq da alkhairi, daga bisani sai Kara da cewa zasu cigada gudanar da wa'azin karshen wata kamar yadda yasaba a ko wani karshen wata.
(2) Shashen malamai Mata na makarantar Bilal BN rabah yasamu sabon malama, Shashen malaman dayane daga cikin malamai masu koyarwa a makarantar,Wanda ya juma Yana bada gudumawansa, a 6angaran aikace -aikace na makarantar. (wakilanmu na makarantar Bilal BN rabah salisu Abubakar Yana tape da cigaban reportan)" Shashen malamai na mata dayane daga cikin Shashen da yake ba gudanarwansa a makarantar,a cikin wannan satin da muke cikine dai makarantar ta gabatarwa da sabowan malaman Mai suna " HAJARA ABDULLAHI" wa daliban makarantar na 6angaren islamiyya wanda tunin malaman tafara gudanar dakaratu,a makarantar daga karshe sai malama Hajara tayi fatan alheri wa makarantar Bilal BN rabah.(karshen reportan kinan salisu Abubakar).
* to an gaisheka*
(3)An gargadi dalibai tare da Jan kunnensu akan yawan fitowa daga ajujuwansu a lokacin da ake gudanar da karatu, wannan gargadi ya fitone daga bakin shugaban makarantar Bilal BN rabah, malam Abdurrahman Yusuf Adam, bisani ganin yadda dalibai s**an baro ajujuwansu sannar daga bisani su cigaba da wasa a farfajiyan makarantar,sai ya tunatar da malaman ajujuwa dasu zawo masu saka ido akan dukkan dalibai domin ganin sun zauna a ajinsu,daga karshe shugaban ya jadda daukan mataki akan haka.

** MAI SAURARO KAI DAI KASHA'AFA KANA SAURARON SHIRIN LABARUN MAKO NE DAKE ZUWA MAKA DAGA NAN SHASHIN LABARU DA AL'AMURAN YAU DA KULLUM NA GIDAN RADIO BILAL BN RABAH**

** TO MADALLAH BARKANMU DA DAWOWA*

(4)An ja hankalin dalibai akan suna kokarin dage ababen zaman karatunsu dana malamansu da zaran antashi a makarantar, wannan Kiran yafitone daga Hukumar makarantan Bilal bn Rabah, sunyi wannan kiranne ganin yadda muke tunkaran damina, a lokacin da yake isar da wannan sakon a wajen taron dalibai na makarantar Wanda akeyinsa a ko wani farkon mako wato ( Assembly),malamin sai ya jadda da matakin da makarantar zata dauka akan dukkan ajujuwan da s**a bar Kayan karatu ajin.
(5) A wani 6angarin kuma an tunatar da dalibai akan suna kokarin xuwa makarantar da Kayan karatu dana rubutu, makarantar tayi wannan kiranne ganin yadda taga kaso 75%na dalibai basa xuwa da Kayan karatu a makarantar,a lokacin da shugaban makarantar Bilal BN rabah malam Abdurrahman Yusuf Adam ya ziyarci wasu ajujuwan a makarantar daga cikin ajujuwan da shugaban ya ziyarta sun hada da 6angari rukunin ajujuwan Haddah Dana islamiyya,daga bisani sai shugaban makarantar yanada wani committee Wanda zai na zagayawa domin ganin ko wani dalibi Yana xuwa da Kayan karatu,Jim kadan bayan tabbatar da committee,sai ta fara gudanar da aikinta nan taki,bisa jagorancin malam zayyad Hussain Idris.
ZAYYAD HUSSAIN Idris sai ya sha alwashen hukunta duk wani dalibin dabaya xuwa da cikikkin Kayan karatu.
(6) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal BN RABAH tayi Kira da Babban murya, akan dalibai su daina tsayuwa akan hanya ko bin hanyar da ba hanyar tapia gida ba ,da zaran an tashi daga makarantar, Kiran yafitone daga bakin Shugaban makarantar Bilal BN rabah, shugaban yayi la'akari ne ganin yadda daliban s**a mayar dashi al'adah, sai yasha alwashen hukunta duk daliban da aka same su, a tsaye akan hanya bayan an tashi daga makarantar.

** DAMA WANNAN REPORTAN MUKE KAWO KARSHE LABARUN MAKO SAI WANI MAKO IDAN ALLAH YAKAIMU ZAKUJI MU DA WASU LABARUN NA DABAN**

YANZU KAN AMADADIN DAUKACIN GUDANARWAN MAKARANTAR BILAL BN RABAH DA TAKE KAWO MUKU
SAI EDITORMU NA WANNAN MAKON
ZAYYAD HUSSAIN IDRIS
SAI NI DANA SHIRYA KUMA NA GABATAR
SALISU ABUBAKAR DANDIJA NAKE ALLAH YAKAIMU WANI MAKO LAPIA.

** BILAL BN RABAH ONLINE RADIO**** SHIRIN LABARUN MAKO**Yau LAHADI: 07/05/2023M, Wanda yayi dai dai da 17/10/1444H.** DA...
08/05/2023

** BILAL BN RABAH ONLINE RADIO**
** SHIRIN LABARUN MAKO**

Yau LAHADI: 07/05/2023M, Wanda yayi dai dai da 17/10/1444H.

** DAFARKO MUHIMMAN KANUNSU**

(1) Makarantar Bilal BN RABAH, ta dawo domin cigaba da gudanar da karatu a makarantar bayan shape kwanaki suna hutu.
(2) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah ta Mika sakon taya murna wa daya daga cikin malaman makarantar bisa samun sarauta da yayi.
(3) Hukumar makarantar Bilal bn Rabah taja hankalin dalibai tare da yi musu gargadi akan zuwa da ababen da s**a haramta a makarantar. tare da hukunda Wanda Basu dawo makarantar ba a satin da akadawo.
(4) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah, ta haramta wa daliban makarantar soyayyar a tsakanin 'yan uwansu dalibai, musanman a makarantar.

YANZU KAN MAI SAURARO SAI KA GYARA ZAMA DOMIN JIN CIKAKKAN SU WANDA NI SALISU ABUBAKAR DANDIJA ZAN KARANTU.

(1) A jiya Asabar ne makarantar Bilal bn Rabah,ta dawo domin cigaba da gudanar da karatu a makarantar, biyo bayan shape kwanaki suna hutu a qalla na kwanaki hamsin da daya(51) suna hutu,da yake sannar da sakon dawowan makarantar, shugaban makarantar Bilal bn Rabah malam Abdurrahman Yusuf Adam sai yafara da Mika godiyarsa wa Allahu subuhanahu wata'ala daya bamu ikon dawowa daga hutu lpia,sai ya Kara da cewa makarantar zata cigaba da gudanar da karatu kamar yadda da saba,tare da daukan tsattsauran mataki,akan duk Wanda ya Saba dokan makarantar.daga karshe sai ya shawarci daliban da su cigaba da Mai da hankali akan karatunsu.
(2) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah,ta Mika sakon taya murna wa daya daga cikin malaman makarantar Mai suna ( malam Usman Jibril Umar) bisa samun sarauta da yayi a lokacin gudanar da hidimar sallah, Wanda Allah ya zabenshi a matsayin( SA'IN JARMAI NA FARKO) dake karamar Hukumar kanam a jihar plateau (jos) wannan matsayin da yasamu yazune bisa irin gudumawa dake bayarwa a yankinsa.shima a nashe jawabin Mai girma SA'IN JARMAI NA FARKO malam Usman Jibril Umar sai ya nuna farin cikinsa wa daukacin al'ummah musulmai da s**a taya Shi farin, daga karshe sai yayi godiya wa Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah, bisa nuna masa soyayya akan haka.

*** MAI SAURARO KAR DAI KASHA'AFA KANA SAURARON SHIRIN LABARUN MAKO NE DAKE ZUWA MAKA DAGA NAN SHASHIN LABARU DA AL'AMURAN YAU DA KULLUM NA GIDAN RADIO BILAL BN RABAH.***

**TO MADALLAH BARKANMU DA RATSE*

(3) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah, ta ja hankalin dalibai tare da yi musu gargadi akan zuwa da ababen da s**a haramta a makarantar,tare da hukunta wanda Basu dawo a satin da akadawo ba, wannan batun yafitone a lokacin da a ke gudanar da taron dalibai na mako wato (Assembly) Wanda makarantar tasaba yinsa a dukkan farko mako domin tunatar da dalibai muhimman batuttowa dake faruwa a makarantar, da yake gudanar da Assembly malam zayyad Hussain sai ya gargadi daliban dasu zamo masu bin dokokin makarantar sau da kafa.daga karshe sai ya karantu wani Shashi daga cikin dokokin makarantar,Wanda shashin na sha biyar (Sections 15 ) shashin da ya haramta wa dalibai zuwa da wayan ( hand set) da dai sauransu.
har illah yau Hukumar makarantan Tasha alwashen hukunta daliban da Basu dawo makarantar ba akan lokacin da zaran sun dawo makarantar zata hukunta su.
(4) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah, ta haramta wa daliban makarantar soyayya a tsakanin'yan uwansu dalibai, wannan haramcin ya zune a lokacin da mahukunta makarantar takai wani sumame yadda tasamu dalibai suna soyayya a tsakanin su,da yake shaidawa wa manema labarai akan matakin da makarantar ta daukan akan masu soyayya a makarantar a offishin sa, shugaban makarantar sai tabbatar mana da cewa makarantar zata sallamisu sannar Kuma gayyatan iyayen Baki.
wani 6angaren kuma Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah tana sanar da daukacin al'ummah da masu sha'awar Shiga ( DAURA ) Wanda tasaba gudanarwan duk shekara a tsakanin Yara domin ya Basu damar iyya hada baki, a wannan shekaran ma takawo waasu sha'awar Shiga, dasu garzawo haraban makarantar Bilal BN RABAH.

DAMA WANNAN REPORTAN MUKE KAWO KARSHE LABARUN MAKO, NA WANNAN MAKON SAI WANI MAKO IDAN ALLAH YAKAIMU ZAKUJI MU DA WASU.

YANZU KAN AMADADIN DAUKACIN GUDANARWAN MAKARANTAR BILAL BN RABAH DAKE DAUKAN NAUYIN KAWO MUKU.
SAI EDITOR MU NA WANNAN MAKON
ZAYYAD HUSSAIN
SAI NI DANA SHIRYA KUMA NA GABATAR
SALISU ABUBAKAR DANDIJA.

**BILAL BN RABAH ONLINE RADIO****SHIRIN NA MUSANMAN AKAN WATAN RAMADAN 1444AH/ 2023M****SHIRIN DAI zumukune a Ranar: MON...
17/04/2023

**BILAL BN RABAH ONLINE RADIO**
**SHIRIN NA MUSANMAN AKAN WATAN RAMADAN 1444AH/ 2023M**

**SHIRIN DAI zumukune a Ranar: MONDAY& TUESDAY: 26/27/09/1444AH/2023M. Wanda yayi dai dai Ranar 17/04/2023&18/04/2023.

* Shiri ne na musanman Wanda zai yi dubi akan yadda Rufe tafseerai na wannan watan Ramadan yake gudana Daga cikin wasu masallatai na nan cikin garin Bauchi.

GA kadan daga cikin masallatan.

(1) Masallacin jumu'ar na ( UTHMAN BN AFFAN) dake bayan tsohon bankin inland bank new G.R.A BAUCHI.WANDA (IMAM ANAS YUSUF ADAM ) yake gabatarwa.

(2) Masallacin jumu'ar na Bilal BN RABAH JUMU'AT MOSQUE DAKE nassarawa jahun unguwar dim, isah YUGUDA CRESCENT BAUCHI.wanda (IMAM MUHAMMAD YUSUF ADAM) Yake gabatarwa.

(3) (Masjidul RAHMAN) DAKE NASSARAWA JAHUN UNGUWAN DIM WANDA AKAFI SANI DA MASALLACIN MAI SHAYI, WANDA (MALAM AMINU YALWAN SHANDA) Yake gabatarwa.

Har illa yau da kuma 6angaren tafseerai na Mata, Wanda malamai suke gabatarwa, a masallatai daban-daban a cikin garin Bauchi.

(4) MALAM sulaiman zakariyya ( Abu bassam)Wanda yake gabatarwa a cikin Masallacin jumu'ar na Bilal bn Rabah.dake nan cikin garin Bauchi.

(5) MALAM Attahiru bakoji Wanda yake gabatarwa a makarantar sheikh ja'afar Mahmood Adam dake unguwan kuka kantudu Bauchi.

(6) Malam jamilu wanda yake gabatarwa a Masjidul RAHMAN DAKE nassarawa jahun unguwan dim, Bauchi.

Da dai sauransu, Allah ya sanya albarka a cikin wannan watan Ramadan da muke cikin ta,ku kasance damu domin samun su daya bayan daya.

Wanda gidan radio Bilal BN RABAH ONLINE RADIO ya dauki nauyin kawo muku.

YANZU KAN SAI KA GYARA ZAMA DOMIN JIN CIKAKKAN SU WANDA NI SALISU ABUBAKAR DANDIJA ZAN GABATAR:

** Azumin watan Ramadan dayane daga cikin rukunin Addinin musulunci,Wanda Allah ya shar'anta wa dukkanin ko Wani baligi kuma Wanda yake da cikikkin hankali da lpia,ya Zama wajibi a gare shi ya Azumci watan Ramadan,bisa haka ne saya dukkanin karshen Azumin watan Ramadan, malamai masu tafseer ai suke rufe tafseerai, a dai dai wannan lokacin.shima babban limamin massalacin jumu'ar na UTHMAN BN AFFAN(IMAM ANAS YUSUF ADAM) yabi sahun takororinsa wajen ganin ya rufe tafseer na wannan shekara 1444AH/2023M,A Yau litinin 26/09/1444Ah Wanda yayi dai dai da 17/04/2023m. a yayin rufe tafseer din yasamu halattar manya- manyan malamai da ma'aikatan gwamnati, daga cikin malaman da s**a halattar sun hada da Babban limamin massalacin jumu'ar na Bilal bn Rabah" IMAM MUHAMMAD YUSUF ADAM da Alarammomi da sauran al'ummah musulmai.

Ansamu gabatar da nasiha daga Bakin Hukumar gudanarwan na Masallacin da dai sauransu.

daga karshe IMAM ANAS YUSUF ADAM sai was Allah bisa gwadamasa karshen wannan tafseer na bana, daga bisa sai yayi amfani da damarsa wajen ganin yayi nasiha wa al'ummah da su zamo masu mutunta lokacin, saboda yadda yaga lokacin Yana gudu.

**BILAL BN RABAH ONLINE RADIO**** SHIRIN LABARUN MAKO**Yau  LARABA: 21/9/1444AH.   Wanda yayi dai dai da 12/04/2023M.**D...
12/04/2023

**BILAL BN RABAH ONLINE RADIO**
** SHIRIN LABARUN MAKO**

Yau LARABA: 21/9/1444AH.
Wanda yayi dai dai da 12/04/2023M.

**DAFARKO MUHIMMAN KANUNSU**

(1) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah ta bada hutun sallah na tsawon kimanin kwanaki Ashirin da shida(26) daga Ranar 09/04/2023 zuwa Ranar 06/05/2023.
(2) sannar Kuma Hukumar makarantar Bilal bn Rabah tana Kara tunatar da daukacin iyayen Yara akan suna biyan kudin makarantar 'yayan su akan lokacin,da zaran an Shiga wani sabon zangon karatu.
(3) shugaban makarantar Bilal bn Rabah ya tunatar da dalibai akan su Kara dagewa wajen cigaba da yin Addu'o'i wa kasa dama jihar Bauchi na samun dawwamammen zaman lpia.
(4) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah ta ja hankalin daliban makarantar da suyi koyi da abinda suke karantawa na alqur'ani.

** YANZUKAN MAI SAURARO SAI KA GYARA ZAMA DOMIN JIN CIKAKKAN SU WANDA NI SALISU ABUBAKAR DANDIJA ZAN KARANTU.

(1) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah ta bada hutun sallah har na tsawon kimanin kwanaki Ashirin da shida (26) daga Ranar 09/ 04/2023 har izuwa ranar 06/04/2023, sakon hutun sallah yafitone daga bakin shugaban makarantar Bilal bn Rabah, malam Abdurrahman Yusuf Adam yace sakon hutun ya biyo bayan shape kwanaki suna gudanar da karatu a cikin wannan watan Ramadan kamar yadda makarantar tasaba gudanarwan.
sai shugaban makarantar ya cigaba da Mika godiyar sa wa Allah da ya kawo mu yau muna cikin watan Ramadan mai alfarma da kuma daraja.daga karshe sai yayi Addu'ar da fatan kuwa sai hidimar sallah lpia.

(2) Shugaban makarantar Bilal bn Rabah malam Abdurrahman Yusuf Adam, Yana Kara tunatar da daukacin iyayen Yara akan suna biyan kudin makarantar'yayan su akan lokacin, da zaran an Shiga sabon zangon karatu, domin bayar wa makarantar tsare-tsarenta akan lokacin batare da wani matsalolin a cikin karatun 'yayan su ba,ya sannar da wannan sakonne a lokacin da yake isar da hutu a harabar makarantar, daga karshe sai ya roki Allah, sannar Kuma da daukacin iyayen Yara akan haka.

** MAI SAURARO KAI DAI KASHA'AFA KANA SAURARON SHIRIN LABARUN MAKO NE DAKE ZUWA MAKA DAGA NAN SHASHIN LABARU DA AL'AMURAN YAU DA KULLUM NA GIDAN RADIO BILAL BN RABAH.**

** TO MADALLAH BARKANMU DA RATSE**

(3) Shugaban makarantar Bilal bn Rabah"Malam Abdurrahman Yusuf Adam"ya tunatar da daliban makarantar akan su Kara dagewa wajen cigaba da yin Addu'o'i wa kasa dama jihar Bauchi na samun dawwamammen zaman lpia, wannan tunatarwan yafitone a lokacin da yake ganawa da manema labarai a cikin makarantar Bilal bn Rabah, Abdurrahman Yusuf Adam sai yafara da nuna muhimmanci Addu'o'i wa kasa dama jihar baki daya, idan akayi la'akari da yanda muke cikin wani hali a kasan.daga karshe sai yayi Addu'ar Allah yakawomana sauki a cikin rayuwanki.

(4) Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah ta ja hankalin daliban makarantar dasu yi koyi da abinda suke karantawa na alqur'ani da Hadisai na manzon Allah sallalla'hu Alaihi wasallam, domin su dace da alkhairi da yake cikin sa, da yake wannan Jan hankalin wa daliban makarantar ("" malam MUHAMMAD MUHAMMAD AS GUNNAH) sai ya fara da nuna musu muhimmanci aikin da abinda mutum yakoya domin bashi kariya daga karshe Muhammad Muhammad sai yayi Addu'ar Allah yasanya alkhairi a cikin wannan watan Ramadan da muke cikin sa.
wani 6angari kuma Hukumar gudanarwan makarantar Bilal bn Rabah ta yi nasiha wa daliban makarantar da suji tsoron Allah a lokacin da suke gudanar da hidimar karamar sallah,kamar shigar da bata dace da addini kamar( MATA) ko zuwa party da sauransu kamar (MATA ko MAZA), Daga karshe Hukumar gudanarwan makarantar sai tayi Kira wa iyayen Yara akan su Riki kiwon da Allah yabasu domin Abin tambayane a gobe kiyama.

**DAMA WANNAN REPORTAN MUKE KAWO KARSHE LABARUN MAKO SAI WANI MAKO IDAN ALLAH YAKAIMU ZAKUJI MU DA WASU***

YANZU KAN AMADADIN DAUKACIN GUDANARWAN MAKARANTAR BILAL BN RABAH,TA DAUKI NAUYIN KAWO MUKU.

SAI WANDA YA TACE MANA SHI KAMAR YADDA KU KAJI, MUHAMMAD ZAYYAD HUSSAIN.

SAI NI DANA SHIRYA KUMA GABATAR.
SALISU ABUBAKAR DANDIJA.
SAI WANI MAKO

07/04/2023

** BILAL BN RABAH ONLINE RADIO**
Gidan radio BILAL BN RABAH ONLINE RADIO ta shirya domin fara kawo muko shirye-shiryenta:
Wanda ya shafe ilimantarwa da fadakarwada kuma dabe muku kiwanku.
(1) Shirin LABARUN MAKO.
(2) Shirin INNA MAFITA .
(3) SHIRIN DAUSAYIN AL'QUR'ANI MAI GIRMA.
DA DAI SAURANSU.

05/02/2023
**MOCK EXAMINATION 2022/2023 ACADEMIC SESSION*** Hukumar gudanarwan makarantar Bilal BN RABAH ta shirya wa daliban makar...
05/02/2023

**MOCK EXAMINATION 2022/2023 ACADEMIC SESSION***
Hukumar gudanarwan makarantar Bilal BN RABAH ta shirya wa daliban makarantar jarrabawa gwaji na (mock examination) a tsakanin daliban domin tantance masu kokari a tsanin daliban kamar yaddan ta saba a kowace shekara.

Address

Nassarawa Jahun, Unguwar Dim, Opposite Bilal Bn Rabah Jumu'at Mosques Bauchi
Bauchi

Telephone

+2347035214942

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when BILAL BN RABAH RADIO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category