City News Channel

City News Channel Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from City News Channel, Media/News Company, Kano.

DA DUMI-DUMI: Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya miƙa lambar yabo ga Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulƙadir Mohamm...
07/12/2025

DA DUMI-DUMI: Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya miƙa lambar yabo ga Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulƙadir Mohammed, a matsayin gwarzon gwamna da ya yi fice wajen ingantaccen shugabanci da bunƙasa birane.

An ba da wannan karramawa ne a wani baje kolin kimanta ayyukan shugabanni da Ma’aikatar Sakataren Gwamnatin Tarayya ta shirya tare da hadin gwiwar cibiyar Best Strategic Media, wacce ta ƙware wajen tantance ayyukan manyan jami’an gwamnati a faɗin ƙasa.

Shugaban ƙasa Tinubu, wanda Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya wakilta, ya bayyana cewa Gwamna Bala Mohammed ya cancanci wannan girmamawa sakamakon kyakkyawan tsare-tsaren sa na ci gaban birane, manufofin da s**a haɓaka tattalin arziki da jin daɗin al’umma, da kuma jajircewarsa wajen gudanar da mulki bisa gaskiya da rikon amana.

A yayin bikin miƙa lambar yabo da aka gudanar a babban dakin taro na Fadar Shugaban Ƙasa, Akume ya jaddada cewa gwamnatin tarayya na maraba da irin gudummawar jagoranci mai inganci da gwamnonin da s**a keɓanta suke bayarwa, yana mai cewa irin waɗannan kyaututtuka na ƙarfafa nagarta da gasa mai kyau tsakanin shugabanni.

Gwamna Bala Mohammed ya yi godiya bisa wannan karramawa, yana mai cewa za ta ƙara masa ƙaimi wajen ci gaba da aiwatar da manyan manufofi da tsare-tsare da ke canza fuskokin birane tare da inganta rayuwar al’umma a Bauchi da ma sauran Arewa maso Gabas.

Mun yi nisa wajen kokarin ceto dalibai ‘yan mata da aka sace a makarantar mata ta GGCSS Maga in ji Gwamnan Kebbi Nasir I...
18/11/2025

Mun yi nisa wajen kokarin ceto dalibai ‘yan mata da aka sace a makarantar mata ta GGCSS Maga in ji Gwamnan Kebbi Nasir Idris Kauran Gwandu wanda ya shaida wa iyayen daliban haka a yayin ziyarar jaje da ya kai musu a ranar Litinin.

Za'a kirkiro johohi shida a NigeriaKwamitin haɗin gwiwa na majalisar dattawa da ta wakilan Najeriya kan yi wa kundin tsa...
26/10/2025

Za'a kirkiro johohi shida a Nigeria

Kwamitin haɗin gwiwa na majalisar dattawa da ta wakilan Najeriya kan yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar garambawul ya amince da a ƙirƙiro jihohi guda shida.

BBC ta rawaito cewa wannan na cikin matsayar da aka cimmawa a ƙarshen taron ƙara wa juna sani na kwana biyu, wanda mataimakin majalisar dattawa Sanata Barau I. Jibrin da mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu s**a jagoranta a jihar Legas.

Kwamitin ya tattauna ne kan buƙatu guda 69, ciki har da buƙatar ƙirƙirar jihohi 55 da buƙatar a ƙirƙirar ƙananan hukumomin 278 kamar yadda jaridar Daily Trust mai zaman kanta ta ruwaito.

A game da buƙatar ƙirƙirar jihohi 55 da aka gabatar a ranar Asabar, kwamitin ya amince da ƙirƙirar jihohi guda shida a duk shiyoyin ƙasar guda shida.

Idan aka amince da ƙirƙirar sababbin jihohi, Najeriya za ta zama tana da jihohi 42 ke nan.

Gwamnatin Tarayya ta Fitar da Naira Biliyan 32.9 Don Inganta Kiwon Lafiya — Ministan LafiyaGwamnatin Tarayya ta amince d...
23/10/2025

Gwamnatin Tarayya ta Fitar da Naira Biliyan 32.9 Don Inganta Kiwon Lafiya — Ministan Lafiya

Gwamnatin Tarayya ta amince da sakin Naira Biliyan 32.9 dan gudanar da shirin Basic Health Care Provision Fund (BHCPF), wanda zai tallafawa cibiyoyin kiwon lafiya a matakin ƙasa baki ɗaya. Wannan shi ne zagaye na uku na wannan shirin a bana.

Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa mai taken Jar Wasiƙa “The Red Letter”, inda ya jaddada cewa kudaden sun riga sun fara shiga asusun ajiyar kuɗi na cibiyoyin kiwon lafiya na gundumomi a duk faɗin ƙasar.

Pate ya ce wannan mataki na nufin bai wa al’ummomi ikon tsara yadda za su kashe kudaden domin tabbatar da cewa kuɗin ya samar da ingantaccen sakamako ga jama’a.

Ya ce gwamnatin tarayya ta cika nata alkawari wajen samar da kudaden, yanzu al’ummomi ne ke da hakkin tabbatar da cewa an yi amfani da su yadda ya dace.

Ministan ya yi kira ga kowane ɗan Najeriya da ya tashi tsaye wajen kare lafiyar jama’a ta hanyar shiga cikin kwamitocin kula da asibitoci, duba yadda ake kashe kudaden, da kuma tabbatar da gaskiya da bayyananniyar hanya wajen amfani da su.

Ya ƙara da cewa gwamnati tana son ganin wannan saƙo ya isa kowace unguwa, gunduma da gida, don tunatar da ‘yan ƙasa cewa inganta lafiyar Najeriya abu ne da yake hannun yan Najeriya.

10/10/2025

Kungiyar matasan Dass, Tafawa Balewa, da Bogoro sunyi Kira ga barrister Aminu Balarabe Isah da ya fito takarar Dan majalisar tarayya

"Sunusi Adamu Kobi"

Da Dumi Dumi: Wani Matashi Yà Zùbà Shìñkafaŕ Bèrà A Cikin Abincin Da Ya Siya A Wani Shagon Abinci A Kano, Inda Ya Yankè ...
26/09/2025

Da Dumi Dumi: Wani Matashi Yà Zùbà Shìñkafaŕ Bèrà A Cikin Abincin Da Ya Siya A Wani Shagon Abinci A Kano, Inda Ya Yankè Jiki Ya Fadi, Bayan Ya Ci Abiñçìñ, Inda Daga Bisani Aka Garzaya Da Shi Asibiti

Lamarin dai ya auku ne cikin daren nan a wani gidan abinci dake kan titin Audu Bako a birnin Kano, inda majiyar ta rawaito cewa tuni aka garzaya da shi asibitin Malam Aminu Kano domin ceto ransa.

Ko me ya yi zafi?

Da Dumi Dumi: an Bude ofishin Sen. Natasha akpoti oduagan Sanatar da ke wakiltar kogi ta tsakiya bayan rufeshi na dogon ...
23/09/2025

Da Dumi Dumi: an Bude ofishin Sen. Natasha akpoti oduagan Sanatar da ke wakiltar kogi ta tsakiya bayan rufeshi na dogon lokaci bisa dakatarwar da majalisar tayimata Kan rashin da'a.

Majalisar ta Bude ofishin ne bisa nuna cewa taqaddamar tayi sauki Kuma wa'adi ya cika Amma tare da sharadin rubuta takardr bada hakuri ga zauren majalisar kamar yadda shugaban marasa rinjaye ya nema Mata.

Ranar 07-10-2025. Zauren zai koma zamansa bayan hutun da aka tafi, a wannan rana ne majalisar zata yanke hukuncin bada dama ga dawowar Sanatar kodai ta hanyar rubuta takardr hakurin kokuma hakanan batare da wani sharadi ba.

MAM✍️

Osmane Dembele ya lashe kyautar mafi kyawum Dan kollo a duniya wato (Ballond'or ta 2025)Wani fata kuke masa?
22/09/2025

Osmane Dembele ya lashe kyautar mafi kyawum Dan kollo a duniya wato (Ballond'or ta 2025)

Wani fata kuke masa?

Marayu 15 sunci gajiyar tallafin karatu a gidan PhDShugaban kungiyar Bauchi state women amalgamation for Hon. Yakubu PhD...
22/09/2025

Marayu 15 sunci gajiyar tallafin karatu a gidan PhD

Shugaban kungiyar Bauchi state women amalgamation for Hon. Yakubu PhD project 2027 Aisha fayyaz ta dibi wasu marayu ta maidasu makaranta tare da basu litattafan karatu su kimanin mutum 15

Wannan yunkurin yazo ne a daidai lokacinda yara S**a koma makaranta su kuwa wadannan marayu basuda damar hakan wannan baiwar Allah taga ya dace ta maidasu makaranta sannan wadanda Basu Shiga ba ta dauki nauyin karatun nasu

Wannan yasa jajirtacciya a fagen tunani a Kan Mata da mafitar su a gidan Hon. Yakubu Adamu PhD taga ya dace ta karfafi guiwar wadannan wajen zuwa makaranta domin nuna musu muhimmancin ilimi da martabarsa domin Zama manyan gobe.

MAM✍️

Labari cikin Hotuna kungiyar B.W. Movement 2027 tana Kiranye Ga Dr. Bala Majama’a Wunti Domin ya fito takaran kujeran Gw...
21/09/2025

Labari cikin Hotuna

kungiyar B.W. Movement 2027 tana Kiranye Ga Dr. Bala Majama’a Wunti Domin ya fito takaran kujeran Gwamnan Bauchi mai taken

“Amsa Kiran Al’ummar Jihar Bauchi: Dr. Bala Majama’a Wunti B.W. Movement 2027”

Dan Arewa Daga Jihar Jigawa, Ismail Muhammad Adam Ya Zama Na Uku A Gasar Fasaha Mafi Girma A AfirkaGasar Digital for All...
20/09/2025

Dan Arewa Daga Jihar Jigawa, Ismail Muhammad Adam Ya Zama Na Uku A Gasar Fasaha Mafi Girma A Afirka

Gasar Digital for All Challenge, wacce ita ce gasar koyon fasaha mafi girma a Afirka, an shirya ta ne ta hannun Tech4Dev tare da haɗin gwiwar Foreign, Commonwealth & Development Office (FCDO), NITDA da kuma UK-international development Tech Hub. Gasar ta sake samun wani babban ci gaba inda Ismail Muhammad Adam, wanda ya wakilci yankin Arewa maso Yamma, ya fito a matsayin na uku (2nd Runner-Up) a rukuni na matasa (Youth Intermediate Category).

Rukunin, wanda shi ne mafi girma daga cikin rukunan gasar, an tsara shi ne domin gwada ƙwarewar mahalarta a fannin fasaha da kuma yadda za su iya amfani da ita a aikace.

A matsayin ladan nasarar da ya samu, Ismail Muhammad Adam ya karɓi kudin ₦10,000,000 tare da samun takardar shaidar ƙwararren mai haɓaka manhajar kwamfuta (Certified Software Developer), wanda ke nuna babban ci gaba a rayuwar aikinsa.

Yayin da yake wakiltar Jihar Jigawa, shi ne kaɗai ɗan takara da jami’an gwamnatin jiha s**a raka, abin da ya ƙara tabbatar da jajircewar Gwamnatin Jihar Jigawa wajen bunƙasa ilimin fasaha da ƙarfafa matasa. Sabon Daraktan Hukumar ICT da Tattalin Arzikin Dijital ta Jihar Jigawa ya bayar da muhimmin tallafi ta hanyar kasancewa tare da shi har zuwa ƙarshen gasar.

Jam'iyyar adawa ta PDP ta ce shugaba Tinubu ya fara shirye-shiryen mika mata ragamar mulki, domin 'yan Najeriya ba za su...
20/09/2025

Jam'iyyar adawa ta PDP ta ce shugaba Tinubu ya fara shirye-shiryen mika mata ragamar mulki, domin 'yan Najeriya ba za su sake zabar sa ba.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when City News Channel posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share