Arewa Media Centre

  • Home
  • Arewa Media Centre

Arewa Media Centre Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Arewa Media Centre, News & Media Website, .

YANZU-YANZU: Kotu ta tura Farfesa Usman Yusuf gidan yari kan wa 'yan nan laifuffukan 👇👇👇An k**ashi saboda yace da arziki...
03/02/2025

YANZU-YANZU: Kotu ta tura Farfesa Usman Yusuf gidan yari kan wa 'yan nan laifuffukan
👇👇👇

An k**ashi saboda yace da arzikin Arewa aka gina Lagos ba wai da iya arzikin jahohin yarabawa ba.

An k**ashi saboda yace Lagos ba ta fi kowacce jaha a Arewa cancantar arzikin kasa ba.

An k**ashi saboda ya tona asirin Tinubu na ganin an tattare arzikin Nigeria gaba daya a yankin yarabawa.

An k**ashi saboda yace talakawa suna shan bakar wahala a hannun Tinubu.

An k**ashi saboda yace dokar haraji zalunci ce dole a tsaya a mata gyara yadda ya k**ata.

An k**ashi saboda yace 'yan Arewa ne s**a zabi Tinubu kuma suke da damar zaben kowanne kalar dan takara.

An k**ashi saboda yace malamai su ji tsoron Allah su daina biyewa 'yan siyasa suna cutar da talakawa.

An k**ashi saboda yana wayar da kan talakawan Arewa akan su tashi tsaye su san 'yancin kansu kuma su ba bayi ba ne mutane ne masu daraja.

An k**ashi saboda ya watsar da jin dadin duniya ya zabi zama cikin talakawa da wayar musu da kai domin gobensu ta gyaru.

Abun Kunya: Tsohon Dogari Ya Zama Mataimakin Watsa Labarai na Ministan Abuja – Shamsudeen Bala MohammedDan Gwamnan Jihar...
28/01/2025

Abun Kunya: Tsohon Dogari Ya Zama Mataimakin Watsa Labarai na Ministan Abuja – Shamsudeen Bala Mohammed

Dan Gwamnan Jihar Bauchi, Shamsudeen Bala Mohammed, ya yi martani mai zafi ga tsohon Kakakin Majalisar Tarayya, Yakubu Dogara, Shamsudeen, wanda aka sani da s**ar masu adawa da mahaifinsa, ya bayyana cewa wannan abun kunya ne wa Dogara

Shamsudeen ya ce: “Dogara wanda a baya yake da babbar kujera a Majalisar Tarayya yanzu ya koma matsayin da bai dace da irin tarihinsa ba. Wannan wata alama ce ta yadda rashin alkibla ke jawowa mutum ya rasa matsayinsa.”

Ya kara da cewa Yakubu Dogara ya rasa tasirinsa ne tun bayan rikicin da ya barke tsakaninsa da Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed.

Farfesa Muhammad Ali Pate, ya na ɗaya daga cikin mutane 'yan ƙalilan da ke da ƙarfin faɗi a ji a harkokin kiwon lafiya a...
28/01/2025

Farfesa Muhammad Ali Pate, ya na ɗaya daga cikin mutane 'yan ƙalilan da ke da ƙarfin faɗi a ji a harkokin kiwon lafiya a duniya. Su ke da alhakin tsara dokokin kiwon lafiya a duniya, sannan kuma su raba tallafin lafiya wa al'ummomi mabukata. Inda za mu ƙarfafa shi da kujerar gwamnan jihar Bauchi, da zai inganta harkokin kiwon lafiya, ta hanyar da har mutane daga ƙasashen waje, za su ringa zuwa jihar Bauchi jinya.

Kowa ya ga irin gudunmawar da Farfesa Muhammad Pate ya ke kan ci gaba da baima harkokin ci gaban kiwon lafiya a jihar Bauchi, a matsayin sa na ministan lafiya. Ina ga kuma in ya zamo gwamnan jihar Bauchi?

Wannan fahimta ta ce!

Shehu Hassan Makwallah

MANYAN MALAMAI KUN BA MU KUNYA: A Ce Ku Je Har Bauchi Amma Ku Kasa Zuwa Duba Malam Idris Dutsen Tanshi Da Ba Shi Da Lafi...
16/01/2025

MANYAN MALAMAI KUN BA MU KUNYA: A Ce Ku Je Har Bauchi Amma Ku Kasa Zuwa Duba Malam Idris Dutsen Tanshi Da Ba Shi Da Lafiya?

Daga Datti Assalafiy

Hakika Malaman da s**a zo Bauchi s**a ki zuwa gaishe da Malam Idris Abdul-Aziz Bauchi sun bamu kunya, basu kyauta ba, kuma basu bi karantarwan Musulunci ba.

Malam Idris Abdul-Aziz ya kai kusan wata guda yanzu yana fama da jinya, karfin hali kawai yake yi shiyasa kuke ganinsa yana hawa mimbari, amma tabbas yana fama da rashin lafiya sosai.

Ya k**ata yadda Malamai s**a zo Bauchi daurin auren babban Malaminmu Sheikh Dr Ibrahim Disina da wadanda s**a zo yiwa Gwamnan jihar Bauchi ta'aziyyar rasuwar step mother dinsa sun yi amfani da wannan damar sun je sun gaishe da dan uwansu Malam Idris Abdul-Aziz

Raddi na ilimi da Malam yake yiwa Malamai 'yan uwansa wannan bai taba zama dalilin da zai sa zasu kullaceshi da tsananin gaba haka ba.

Gaskiya Malamai kun bamu mamaki, zamu cigaba da karban abinda ya tabbata na gaskiya da ya fito daga bakunanku, amma ba shakka zamu dena koyi da wasu daga cikin dabi'unku irin na 'yan siyasa.

Inda dan siyasa ne da yake rike da madafun iko yayi rashin lafiya haka a guje zaku je ku gaishe shi saboda zai bada kudi, amma Malami dan uwanku don ya muku raddi babu ruwanku da shi.

Allah Ka shiryar da Malaman mu tare mu gaba daya zuwa tafarkin tsira duniya da lahira.

Allah Ka yaye wa Malam Idris Abdul-Aziz Bauchi jinyar da take damunsa, Ka kara masa lafiya da imani da tsawon rayuwa mai albarka

MARYAM TA JE ABUJA KARBAN iPhone 16 KO? LISSAFI YA KWABE!, DARASIN RAYUWA!Dazu da safe, Manajan gidan hotel na Palasa da...
16/01/2025

MARYAM TA JE ABUJA KARBAN iPhone 16 KO? LISSAFI YA KWABE!, DARASIN RAYUWA!

Dazu da safe, Manajan gidan hotel na Palasa dake yankin Gwagwalada Abuja ya kai kara ofishin 'yan sanda na Gwagwalada bayan wani mutum ya mutu a dakin hotel din da ya k**a shi da wata karuwa

Sunan wanda ya mutu Lawal Ibrahim, sunan karuwarsa kuma Maryam Abba daga birnin Dutsen Jihar Jigawa, wanda sun hadu a social media watanni uku da s**a wuce

Abinda ya faru shine, Lawal ya kira Maryam zuwa Abuja, jiya da dare ya sauketa a Palasa Hotel s**ayi zina, da garin yau Laraba ya waye da misalin karfe 6 na safe s**a sake yin zina, Maryam tace suna cikin yin zina ya fado daga kanta ya suma numfashinsa ya dauke, ta yayyafa masa ruwa bai farfado ba

Shine sai ta sanar da ma'aikatan gidan hotel din akazo aka daukeshi aka kai asibiti inda Likita ya tabbatar da Lawal Ibrahim ya mutu, zaku samu bibiyo na cikakken abinda ya faru a Telegram ta nan
👇
https://t.me/DattiassalafiyTech

A yanzu haka Maryam tana hannun 'yan sanda an kaita zuwa Force CID Abuja don tabbatar da bincike akan musabbabin mutuwar abokin fasikancinta, abubuwa da aka samu sun hada da kankana da miyagun kwayoyi masu kara karfin jima'i

Darasin da zamu dauka anan shine:
👇
Maryam 'yar Jihar Jigawa ne daga birnin Dutse, ta yiwa iyayenta karya ta taho Abuja domin ayi lalata da ita, abokin lalata ya mutu a kanta lokacin da suke cikin yin fasikanci, Allah ne Kadai ya san ranar da zata kubuta daga wannan tuhuma na kisan kai da ake mata

Mutane mu ji tsoron Allah, babu wanda ya san a wani irin yanayi ajali zai zo masa, tabbas akwai abin takaici ace mutum musulmi yayi mummunan karshe irin wannan

Matansa da 'ya'yansa da iyayensa, da 'yan uwa da abokansa duk sai sun yi da na sanin saninsa a rayuwa

Haka ita ma yanzu Maryam sai tayi nadamar zuwanta duniya, domin yanzu lissafi ya kwabe mata, iyayenta da 'yan uwanta da sauran samarinta da take yaudara duk zasu san halin da take ciki

Don Allah mu yi iya bakin kokarinmu wajen aikata ayyukan alheri tare da gudun munanan abubuwa da zasu rusa mana tarihi su zubar da kima da mutuncin mu

Allah Ya tsare mana imanin mu, Ya bamu karfin yakar shaidan
Shi kuma Lawal Ibrahim Allah Ya yafe masa, Ya bashi Aljannah don rahamarSa

Wato Labarin Yarinyar nan da  wani mara imani yayi mata Fyade na da matukar tayar da Hankali duk dama cewa Case din yana...
08/01/2025

Wato Labarin Yarinyar nan da wani mara imani yayi mata Fyade na da matukar tayar da Hankali duk dama cewa Case din yana Gaban Kotu!

Wato a Zantawar da mukayi da iyayen yarinyar da kuma Shafa’atu wacca itace ta fara yiwa yarinyar video ta fada min abinda ya tayar min da hankalina matuka.

Ashe Wanda Ake Zargi ya dade da yiwa yarinyar Lalata, kuma tun tana Shekara 8 yake mata mummunar aika aika da farji da kuma ta dubura ( waiyazubillah). Da kuma zubar da kazantarsa a bakinta da tilasata mata hadeyewa.

Ashe ya jima yana yi mata barazana idan har ta sake ta fadawa iyayenta zai kashe ta. Tare da gana mata azaba.

Ashe Makwabta ne da yarinyar, kuma Yarinya ta kasance ba mai cikakakkiyar Hankali bace. Kuma iyayen basu da karfi akan case din nema har Allah yayiwa mahaifinta rasuwa. Har ya saka Mahaifiyar yarinyar zuwa Asibitin murtala dake kano.

Yarinyar Har yanzu ko kwanciya bata iyayi saboda bazata ma iya kwanciya ba. Sai sa ta dan ajeyi Kanta a kafadar uwar ta jingina sai tasamu dan hutu. Kullum suna cikin zullumi basu da wanda zai taimake su. Sai dai Allah ya kawo Baiwar Allah Shafa’atu Muhammad Adam ta Dauki video ta saka a shafinta har aka dinga taggin namu ni da Abba Hikima da wasu masu Fafutuka.

Likitocin da s**a dubu yarinyar s**a ce, tunda suke basu taba ganin Lalata da illa irin yadda aka yiwa wannan baiwar Allah’n ba. S**a ce ko da ma ta samu Sauki zaiyyi wuya ta samu haihuwa ko juna biyu saboda Abun ya taba mata Mahaifa wanda abun har ya taba mata Hanjinta.

A Yanzu dai Mai Girma Gwaman Jahar Jigawa tare da mai Dakinsa sun aika da tawaga zuwa Asibitin murtala har ma an Aikata zuwa Mal Aminu Kano Kano don yi mata aiki. Don Shi Mai Girma Gomna baya Kasar. Ita kuma Matar Gomna zata je kano don ta duna yarimyar tare da mika Godiya zuwaga Sarki Sunusi Lamido Don yadda yanuna Damuwarsa akan yanayin Yarinyar.

Mun tattauna da wakilan Gwanmatin Jahar jigawa waenda aka wakiltasa don tabbatar da cewa an kula da lafiyar yarinya.

Kuma Muna Mika Sakon Gaisuwa ta musamman da jinjina zuwa Ga Shafa’atu Muhammad Adam wanda ta fara dauka Video ta saka Duniya s**a kalla, Da kuma Kungiyoyi da s**a shiga cikin Al’amarin da kuma Jama’a waenda s**a tausaya mata. Allah ya saka muku da Alheri.

Insha Allah zanu bibiyi wannan case din nida Abokina Abba Hikima insha Allah sai mun tabbatar da anyi mata Adalci.

✍️ Barrister Hamza Nuhu Dantani

08/01/2025

TIRKASHI.. Kauran Bauchi ya cire Tsoro ya gayawa Sheikh Sani Yahaya Jingir Gaskiya.

A ganin ku ya k**ata ace Kaura ya fada haka a gaban Malam?

Akan Bashin Naira Dubu 300 Da Ake Binsa, Kotu Ta Siyar Da Gidansa Na Kusan Milyan 20 A Naira Milyan Biyu A KanoMalam Sur...
07/01/2025

Akan Bashin Naira Dubu 300 Da Ake Binsa, Kotu Ta Siyar Da Gidansa Na Kusan Milyan 20 A Naira Milyan Biyu A Kano

Malam Surajo Yarima ya ce a lokacin da aka kai karar kotu ya samu karaya ne inda yake jinya a jihar Adamawa, kuma ya nuna musu hotunan lokacin da yake jinya domin su zama hujja, amma duk da haka ba a karbi uzurinsa ba.

Ya ce yanzu haka an watsar da kayan su waje, inda ba su wajen kwana duk da cewa yana mata da hara tara.

Don haka ne Yarima ya roki gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya kai masa ɗauki domin shiga lamarin.

Rariya

07/01/2025

We Are still selling MTN GIFTING
1GB N200
3.5GB N600
15GB N2000
App Link 👇👇

05/01/2025

Kamfanonin sadarwa na Najeriya sun bukaci Gwamnatin kasar ta amince su yi karin kaso 100 bisa 100 na kudin Data da na kira, suna nufin madadin yadda suke saida MTN SME 1GB Naira 268.5 a yanzu, zai ninka ya koma 537 akan kowane 1GB.

ALHAMDULILLAH: An k**a motar da aka sace a hanyar Bauchi. Muna godiya da Sharing da Addu'o'inku.
04/01/2025

ALHAMDULILLAH: An k**a motar da aka sace a hanyar Bauchi. Muna godiya da Sharing da Addu'o'inku.

Subhanallahi.An sace wannan mota a kofar masallacin Fadan Gombe yanzu bayan kammala daurin aure, me ita ya fito yaga way...
04/01/2025

Subhanallahi.

An sace wannan mota a kofar masallacin Fadan Gombe yanzu bayan kammala daurin aure, me ita ya fito yaga wayam.

Honda Panadol Extra
Gombe FKY 412

A Temaka mana da sharing dakuma sa Ido.

Allah yasa bata fita rabo ba.

Wallahi Duk Wanda Ya Ji Tarihin Rayuwar Shamsiyya Sai Ya Tausaya MataJama'a Assalamualaikum cike d alhinin na ke sanar d...
03/01/2025

Wallahi Duk Wanda Ya Ji Tarihin Rayuwar Shamsiyya Sai Ya Tausaya Mata

Jama'a Assalamualaikum cike d alhinin na ke sanar da ku cewa na samu zarafin tattaunawa da Shamsiyyar Kiyawa, k**ar yadda kuke gani

Akwai tashin hankali akwai abun tausayi ka ga 'ya mace a irin wannan yanayi musamman me kananun shekaru k**ar takwara ta Shamsiyya.

Wallahilazem sai da na yi kwalla, wasu zasu ga ai k**ar ba abar tausayi ba ce, a zahiri ne hakan. Amma badinin Shamsiyya abar tausayi ce.

Na yi mata tambayoyi da s**a hada da dalilin fadawar ta ga wannan mummunar hanya, inda take fada min cewa tana bakin cikin ta zo gida ne ta ga kanenta ba abinci.

A cikin zantawar mu da ita ta bayyana min cewa, idan ta je gida da kudi mahaifiyar ta na tuhumar ta, inda ita kuma take ce mata aikin kamfani take yi.

Na ji tausayin Shamsiyya matuka. Har na yi burin a ce ni wata ce na biya kaf mutanen da Shamsiyya ta daukar wa wayyoyi sanan na killace ta da taimakon Alllah don ta samu ingantacciyar rayuwa.

Shamsiyya ta bayyana min cewa ba ta son ma ta fito daga gun 'yan sanda sabida kunya take ji ta hada ido da mutane, a ciki har da saurayin ta da aka sa musu ranar aure.

Shamsiyya ta ce min yanzun a shirye take da ta canza rayuwar ta, amma da taimakonmu mu al'umma.

Shamsiyya na matukar bukatar tallafin mu, mu al'ummar da take rayuwa tare da mu.

Allah Ya shiryi Shamsiyya da mu baki daya.

23/12/2024

Wani influencer yace wai duk masu follow to follow ɗin nan bamu da sana'a ne. Wai ga matasa can a Kwari suna neman kuɗi. Mu kuma mun tsaya anan muna neman followers. Shin wai dama da gaske rashin sana'a ne yasa kuke follow to follow?

Ku bada ɗan iya sarkin masu sana'a amsa.

Let's go.

Done!!

✍️ Elder Karofi

23/12/2024

ZANYI MAGANA SABODA YA YADA ABIN

Tabbas abinda Gfresh yayi da wancan arn!¥a ba abin koyi bane, Allah bai haramta Musulmi ya auri wacce ba Musulma, amma wannan basu kai ga aure ba s**ayi abinda s**ayi sannan s**a yada a media

Don Allah matasa kar ku dauki wannan a matsayin abin koyi, dabi'a ce ta dabbobi, Sheikh Aminu Daurawa yace: "mutum ba addini dabba yake komawa".

Har ga Allah da mutum ya haifi irin sh Gfresh da Murja Kunya gara yayi fatan Allah Ya hanashi haihuwa har abada

Daga karshe duk wanda yake son kada Allah Ya bashi 'ya'ya irin Gfresh to kar ya dinga mantawa da yin addu'ah kafin saduwa ko jima'i da iyali

Masu afkawa matansu da jima'i basa yin addu'ah ku sani kuna janyo wa al'ummah masifa ne, zaku haifo kangararru yara 'yan iska marassa ji su zo su addabi al'ummah

Allah Ka tsare mana imanin mu

KANASO FACEBOOK SU FARA BIYAN KA?Duk kokarin son tara Followers din ka, ka kuma yi kokarin kirkirar abinda zai kawo maka...
22/12/2024

KANASO FACEBOOK SU FARA BIYAN KA?

Duk kokarin son tara Followers din ka, ka kuma yi kokarin kirkirar abinda zai kawo maka Engagement a shafin ka da zaka samu damar samu kudaden da kake fatan samu.

Nan dai $11,624 ce wata ta samu
A lissafin Naira kusan Million 16 😄😄

Ya zaka ji a ranka a wayi gari ace kaine mammallakin kudin nan? Zaka samu in Shaa Allah amman fa sai da aiki tuƙuru da kuma addu'a.

Allah ya bamu Sa'a baki daya M AMINU

Facebook zasu saka 'yan Najeriya da yawa cikin Alkhairi dumu-dumu, musamman a farkon sabuwar shekara, bayan ka samu acti...
21/12/2024

Facebook zasu saka 'yan Najeriya da yawa cikin Alkhairi dumu-dumu, musamman a farkon sabuwar shekara, bayan ka samu active followers abunda kawai suke bukata shine ka dinga kirkirar sabbin abubuwa na bidiyo da na rubutu.

Matasa a cigaba da neman followers ta hanyar da ta dace. Allah ka bawa masu rabo sa'a.

Address

Bauchi

Telephone

+2348031366666

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media Centre posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Media Centre:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share