Masaniya Tv

Masaniya Tv ILIMI / IMANI / WAYEWA…%

Fadar Shugaban Ƙasa ta yaba da ayyukan tituna a BenueFadar Shugaban Ƙasa ta ce ayyukan tituna da gwamnatin Tinubu ke gud...
07/08/2026

Fadar Shugaban Ƙasa ta yaba da ayyukan tituna a Benue

Fadar Shugaban Ƙasa ta ce ayyukan tituna da gwamnatin Tinubu ke gudanarwa na sauƙaƙa zirga-zirgar mutane,Ta ce aikin titin Makurdi-Otukpo-Enugu ya rage tsawon tafiya daga kusan sa’o’i uku zuwa awa ɗaya da rabi.

Mai ba Shugaban Ƙasa shawara, Bayo Onanuga,ne ya bayyana hakan yayin duba ayyukan more rayuwa a Jihar Benue.

Hukumar Ayyukan Gine-ginen Tarayya ta ce titin mai tsawon kilomita 250 ya ratsa Nasarawa, Benue, Kogi da Enugu, kuma ana sa ran kammala shi a shekarar 2028.

A Benue kuma, ana gyaran titin Oju-Awaji, an farfado da masana’antar Taraku Mills da ake sa ran samar da ayyukan yi sama da 2,000, yayin da Otobi Waterworks ke samar da ruwa ga Otukpo da wasu al’ummomin da ke kusa._____Dimocradiyya

Ƙungiyar 'Tinubu Again 2027' Ta Halarci Wasan Ƙwallon ƘafaYadda ƙungiyar (Tinubu Again 2027) ƙarƙashin jagorancin Ƙarami...
07/08/2026

Ƙungiyar 'Tinubu Again 2027' Ta Halarci Wasan Ƙwallon Ƙafa

Yadda ƙungiyar (Tinubu Again 2027) ƙarƙashin jagorancin Ƙaramin Ministan Tsaro Dakta Muhammad Bello Matawalle Maradun, ta halarci wasan ƙwallon ƙafa na sada zumunta da aka buga jiya Alhamis 6 ga watan Agustan 2026 a Filin Shinge da ke Kurna Babban Layi a jihar Kano, Domin taya gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf, Na cikar sa shekara Uku masu albarka da ya yi a gadon mulki tare da kawo ci gaba ga al'umma Kano da kwarara ayyukan raya ƙasa da bunƙasa harkokin kasuwanci da dawo da darajar ta a idanun duniya.___Rariya

Daga Anas Saminu Ja'en

"Ba Zan Tallata APC Ba Kuma Ba Zan Ce A Zaɓe Ta Domin Ba Ni Da Abun Da Zan Nuna Wanda APC Ta Yi Mana". -In ji jarumin Ka...
07/08/2026

"Ba Zan Tallata APC Ba Kuma Ba Zan Ce A Zaɓe Ta Domin Ba Ni Da Abun Da Zan Nuna Wanda APC Ta Yi Mana". -In ji jarumin Kannywood, Tahir Fagge.___Dokin Karfe Tv

Me za ku ce?

HOTUNA: YADDA wani matashi dan Jam'iyar ADC a jihar Bauchi mai suna Abba Moda, ya mayar da babur ɗinsa kalar tutar Jam'i...
07/08/2026

HOTUNA:

YADDA wani matashi dan Jam'iyar ADC a jihar Bauchi mai suna Abba Moda, ya mayar da babur ɗinsa kalar tutar Jam'iyar ADC, tare da rigar da ke jikin sa, wanda kuma a kullum haka yake yawo a cikin garin Bauchi

A jikin rigar tasa akwai hoton ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC Atiku Abubakar da kuma Jagororin Jam'iyar a matakin ƙasa ƙasa tare da hoton ɗan takarar kujerar gwamnan jihar Bauchi a jam'iyyar ADC Sanata Halliru Dauda Jika.___Albarka Radio

Akwai ƴan Nijeriya da ke tsare a gidajen yarin Saudiyya bayan kasa biyan tara - Jakadan NijeriyaJakadan Nijeriya a ƙasar...
07/08/2026

Akwai ƴan Nijeriya da ke tsare a gidajen yarin Saudiyya bayan kasa biyan tara - Jakadan Nijeriya

Jakadan Nijeriya a ƙasar Saudiyya, Dakta Yakubu Gambo, ya bayyana damuwarsa kan wasu ƴan Nijeriya ke ci gaba da zama a gidajen yarin kasar duk da sun kammala wa’adin hukuncin da aka yanke musu, saboda kasa biyan tarar da kotu ta ɗora musu.

Gambo ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin wata ziyarar da ya kai wa shugabar kuma babbar daraktar hukumar kula da ƴan Nijeriya mazauna ƙasashen waje (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa, a hedikwatar hukumar da ke Abuja.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’ar Yaɗa Labarai, Hulɗa da Jama’a ta NiDCOM, Violet Nwosu, ta sanya wa hannu.___DCL Hausa

Aikin babbar hanyar gaɓar tekun Lagos zuwa Calabar ya yi nisa, in ji Ministan AyyukaMinistan Ayyuka na Tarayya, Sanata E...
07/08/2026

Aikin babbar hanyar gaɓar tekun Lagos zuwa Calabar ya yi nisa, in ji Ministan Ayyuka

Ministan Ayyuka na Tarayya, Sanata Engr. David Umahi, ya ce aikin babbar hanyar gaɓar teku ta Lagos zuwa Calabar ya riga ya wuce Epe, yana mai cewa aikin na samun ci gaba a jihohi daban-daban wanda ake sa ran hanyar za ta ratsa.

Umahi ya bayyana hakan ne yayin da yake duba aikin Sashe na 4B na Lagos-Calabar Coastal Highway a Jihar Ondo ranar Laraba, 5 ga Agusta, 2026.

Ministan ya mayar da martani ne kan ra’ayin tsohon Gwamnan Jihar Cross River, Donald Duke, wanda ya taba bayyana shakku kan ko aikin hanyar zai wuce yankin Epe.

A cewar Umahi, abin da ake gani a wuraren da ake gudanar da aikin ya nuna cewa hanyar ta riga ta wuce Epe kuma tana ci gaba zuwa wasu jihohin kasar.

Ya ce: “Babbar Hanyar Lagos-Calabar Coastal Highway ta riga ta fara tafiya. Mun riga mun wuce Lagos, wanda shi ne abin da dan uwana Donald Duke ya yi magana a kai.”

Umahi ya ce aikin yana gudana a jihohi daban-daban, inda ya bayyana wasu daga cikin sassan da ake aiki a kansu.

Ya ce a Ogun ana aiki kan wani sashe mai tsawon kilomita 28, yayin da a Ondo ake aiki kan kilomita 52. Haka kuma, ya ce aikin ya fara a Calabar kan wani sashe mai tsawon kilomita 27.

A Akwa Ibom kuwa, Ministan ya ce sashe na farko yana da kusan kilomita 47 kuma ayyukan da ake gudanarwa a wasu daga cikin wadannan sassan sun kai sama da kashi 60 cikin 100 na kammalawa.

Ya kuma bayyana cewa akwai wani babban sashe mai tsawon kilomita 180 a Akwa Ibom, wanda yake daga cikin mafi tsawon sassan hanyar Lagos-Calabar.

Ya ƙara da cewa, sama da mutane 1,000 da kamfanin HITECH ya ɗauka aiki suna cikin wadanda s**a amfana da aikin a wani sashe.

Ya kuma bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana da cikakken kudurin ganin an kammala aikin, yana mai cewa shugaban ya tabbatar da cewa za a kammala hanyar.__Hausa Daily Times

An tura kudi asusun banki na Atiku Abubakar - Zargin madugun adawar NijeriyaDan takarar shugabancin Nijeriya na jam’iyya...
07/08/2026

An tura kudi asusun banki na Atiku Abubakar - Zargin madugun adawar Nijeriya

Dan takarar shugabancin Nijeriya na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya bayyana damuwa kan wasu kuɗaɗe da aka tura zuwa ɗaya daga cikin asusunsa na sirri ba tare da saninsa ko amincewarsa ba, yana mai zargin cewa an samu kutsen bayanan sirrin asusun bankinsa.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya fitar a ranar Juma’a.

Sanarwar ta bayyana cewa wani mutum da Atiku bai sani ba ne ya tura kuɗin zuwa asusun, tare da rubuta bayanin “Contribution Electioneering Campaign” a matsayin dalilin tura kuɗin.

Jaridar Punch ta ruwato cewa Atiku ya ce shi da kwamitin yaƙin neman zaɓensa ba su taɓa neman wannan gudummawa ba, ba su ba da izini ba, kuma ba su san wanda ya tura kuɗin ba.___DCL Hausa

TAYA MURNA: Dr. Bala Maijama'a Wunti Ya Zamu Babban Shugaban Hukumar World Energy Council Nigeria Na FarkoƘungiyar Bala ...
07/08/2026

TAYA MURNA: Dr. Bala Maijama'a Wunti Ya Zamu Babban Shugaban Hukumar World Energy Council Nigeria Na Farko

Ƙungiyar Bala Wunti Support Organisation (BWSO) Ta taya wanda ya kafa ƙungiyar, Dr. Bala Maijama'a Wunti, murnar naɗinsa a matsayin Babban Jami'in Gudanarwa (CEO) na World Energy Council Nigeria.
Ƙungiyar ta bayyana cewa wannan naɗi ya tabbatar da ƙwarewa, jajircewa da gagarumar gudummawar da Dr. Wunti ya bayar wajen bunƙasa harkokin makamashi a Najeriya.

BWSO ta yi addu'ar Allah Ya ba shi lafiya, hikima da nasara wajen gudanar da wannan muhimmin nauyi, tare da bayyana ƙwarin gwiwarta cewa jagorancinsa zai ƙara ɗaukaka Najeriya a fannin makamashi a duniya.

–Sanarwa Daga:
Kamal Ibrahim
Jami'in Hulɗa da Jama'a (PRO), BWSO
7 ga Agusta, 2026

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UNAllah Ya yi wa Alhaji Gidado Darazo, tsohon Kwamishina a lokacin mulkin tsohon Gwamna...
07/08/2026

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN

Allah Ya yi wa Alhaji Gidado Darazo, tsohon Kwamishina a lokacin mulkin tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Ahmed Adamu Mu'azu, rasuwa.

Za a gudanar da sallar jana'izarsa a Masallacin Gwallaga da misalin karfe 1:20 na rana, bayan kammala sallar Juma’a.

Muna rokon Allah Madaukakin Sarki Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa. Allah Ya bai wa iyalansa, 'yan uwansa da daukacin al'ummar Jihar Bauchi hakurin jure wannan babban rashi.

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un.

Sakataren yada labaran ADC a jihar Gombe ya fice daga jam'iyyarSakataren yaɗa labarai na jam'iyyar ADC a Jihar Gombe, Ab...
07/08/2026

Sakataren yada labaran ADC a jihar Gombe ya fice daga jam'iyyar

Sakataren yaɗa labarai na jam'iyyar ADC a Jihar Gombe, Abdulrahman Buba Zaune, ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar nan take.

Zaune ya bayyana hakan ne cikin wasiƙar murabus da ya rubuta mai ɗauke da kwanan wata 5 ga Agustan 2026, wadda ya aike wa Shugaban jam'iyyar ADC na Mazabar Zaune, a Ƙaramar Hukumar Dukku ta Jihar Gombe.

A cikin wasiƙar, wadda jaridar Punch ta gani a ranar Alhamis, tsohon Sakataren Yaɗa Labaran ya gode wa jam'iyyar bisa damar da ta ba shi na yin aiki da ita a matakai daban-daban, da s**a haɗa da matakin ƙaramar hukuma, na jiha da kuma na ƙasa.

Address

Sokoto

Telephone

+2347033018580

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Masaniya Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Masaniya Tv:

Shortcuts

Share

Category