07/08/2026
Aikin babbar hanyar gaɓar tekun Lagos zuwa Calabar ya yi nisa, in ji Ministan Ayyuka
Ministan Ayyuka na Tarayya, Sanata Engr. David Umahi, ya ce aikin babbar hanyar gaɓar teku ta Lagos zuwa Calabar ya riga ya wuce Epe, yana mai cewa aikin na samun ci gaba a jihohi daban-daban wanda ake sa ran hanyar za ta ratsa.
Umahi ya bayyana hakan ne yayin da yake duba aikin Sashe na 4B na Lagos-Calabar Coastal Highway a Jihar Ondo ranar Laraba, 5 ga Agusta, 2026.
Ministan ya mayar da martani ne kan ra’ayin tsohon Gwamnan Jihar Cross River, Donald Duke, wanda ya taba bayyana shakku kan ko aikin hanyar zai wuce yankin Epe.
A cewar Umahi, abin da ake gani a wuraren da ake gudanar da aikin ya nuna cewa hanyar ta riga ta wuce Epe kuma tana ci gaba zuwa wasu jihohin kasar.
Ya ce: “Babbar Hanyar Lagos-Calabar Coastal Highway ta riga ta fara tafiya. Mun riga mun wuce Lagos, wanda shi ne abin da dan uwana Donald Duke ya yi magana a kai.”
Umahi ya ce aikin yana gudana a jihohi daban-daban, inda ya bayyana wasu daga cikin sassan da ake aiki a kansu.
Ya ce a Ogun ana aiki kan wani sashe mai tsawon kilomita 28, yayin da a Ondo ake aiki kan kilomita 52. Haka kuma, ya ce aikin ya fara a Calabar kan wani sashe mai tsawon kilomita 27.
A Akwa Ibom kuwa, Ministan ya ce sashe na farko yana da kusan kilomita 47 kuma ayyukan da ake gudanarwa a wasu daga cikin wadannan sassan sun kai sama da kashi 60 cikin 100 na kammalawa.
Ya kuma bayyana cewa akwai wani babban sashe mai tsawon kilomita 180 a Akwa Ibom, wanda yake daga cikin mafi tsawon sassan hanyar Lagos-Calabar.
Ya ƙara da cewa, sama da mutane 1,000 da kamfanin HITECH ya ɗauka aiki suna cikin wadanda s**a amfana da aikin a wani sashe.
Ya kuma bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana da cikakken kudurin ganin an kammala aikin, yana mai cewa shugaban ya tabbatar da cewa za a kammala hanyar.__Hausa Daily Times