Bauchi News Daily

Bauchi News Daily Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Bauchi News Daily, Media/News Company, Bauchi.

Kungiyar kananan Yan kasuwa sun raba tallafin shinkafa ga mutane 500 wanda Sanata Shehu Buba Umar ya tallafa musu.______...
18/03/2025

Kungiyar kananan Yan kasuwa sun raba tallafin shinkafa ga mutane 500 wanda Sanata Shehu Buba Umar ya tallafa musu.
___________

Rabon shinkafa na kungiyar kananan Yan kasuwa ya gudana yanda akalla yan kasuwa 500 s**a amfana da Tallafin shinkafa karkashin jagorancin Munkaila Abdullahi Goje . Wanda aka raba 10k da kuma 5k Gwargwadon abinda ya shigo hannun su.

Kungiyar Pate Media Centre Ta Shirya Taron Shan Ruwa.A karon farko, kungiyar Pate Media Centre ta shirya taron shan ruwa...
18/03/2025

Kungiyar Pate Media Centre Ta Shirya Taron Shan Ruwa.

A karon farko, kungiyar Pate Media Centre ta shirya taron shan ruwa na hadin kai ga abokan gwagwarmaya, ba tare da la’akari da bambancin jam’iyyar siyasa ba.

Taron, wanda aka gudanar a dakin taro na Labari Daga Bauchi ya samu halartar matasa da shugabanni daga bangarori daban-daban na al’umma. Wannan yunkuri na kungiyar na da nufin kara dankon zumunci da hadin kai tsakanin masu fafutuka a fagen siyasa da ci gaban al’umma.

Shugaban kungiyar Shehu Hassan Makwalla ya bayyana cewa, manufar wannan taro ita ce tabbatar da cewa an hada kan al’umma ta hanyar musayar ra’ayi da fahimtar juna, ba tare da nuna bambancin siyasa ba.

Wannan mataki na Pate Media Centre na nuna irin rawar da kungiyoyi masu zaman kansu ke takawa wajen wanzar da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al’umma.

-Bauchi news Daily

Alhaji Sirajo Caps na daga cikin fitattun matasan da ke gwagwarmayar siyasa a jihar Bauchi, musamman a jam’iyyar PDP. Zi...
06/02/2025

Alhaji Sirajo Caps na daga cikin fitattun matasan da ke gwagwarmayar siyasa a jihar Bauchi, musamman a jam’iyyar PDP. Ziyarar da ya kai wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, a birnin tarayya Abuja na nuna alaka ta siyasa da kuma ci gaba da kokarin da matasa ke yi wajen taka rawa a siyasar Najeriya.

Ana ganin irin wadannan ziyarce-ziyarcen a matsayin wani bangare na tattaunawa da shawarwari da ke da nasaba da harkokin siyasa da kuma shirin gaba, musamman yayin da ake shirye-shiryen zabuka masu zuwa.

08/04/2024
Ba za ki san zawarci bala'i bane musamman a wannan karnin namu, sai kin kashe auren ki kin fito nan ne zaki san cewa kin...
21/06/2023

Ba za ki san zawarci bala'i bane musamman a wannan karnin namu, sai kin kashe auren ki kin fito nan ne zaki san cewa kin fita daga rahma kin shiga kaiton ki da nadama, sai wancan yazo kina ta murna ga kin samu ɗan fes fes ga kuɗi ga mota, zaizo kamar dagaske auren ki zaiyi sai dai kiji kawai ya fara ce miki kaza da kaza, in kin ci Sa'a kin kuɓuta baiyi lalata dake ya gudu ba, inkuma daman baki da wayo ga kuma kwadayin ki yakai makura daga nan haka wani ma zaizo har a wayi gari kin zamo yar karamar magajiya, ke bari kiji magana ta gaskiya haka ake ta fama. Ga kuma cututtukan da ake ɗauka.

Tun wuri kiyi hakuri da gidan mijin ki ki zauna, matukar ba aikata wani abu yake wanda dole ne ki rabu da shi wanda ya saɓawa Shari'a, inkuma kin fito lallaɓa ki koma in komawar bai haramta ba, inkuma ba halin komawa zauna kiyi ta addu'a ALLAH kawo miki na gari matukar yana da sana'a ga addini lallaɓa ki aure shi, baki san yaushe ne mutuwa za ta riske ki ba yar uwa ta a musulunci.

Rasheedah Bintu Abeebakar
(Daughter of islam)

Arewa Media Center

KOTU TA TURA SHEKH IDRIS ABDULAZIZ GIDAN YARI A JIHAR BAUCHI._____________Kotu ta tura malam Dr. Idris Abdul’aziz Dutsen...
15/05/2023

KOTU TA TURA SHEKH IDRIS ABDULAZIZ GIDAN YARI A JIHAR BAUCHI.
_____________

Kotu ta tura malam Dr. Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi gidan yari bisa zargin furta kalaman ta da zaune tsaye.

Malamin wanda ya amsa gayyatar ‘yansanda a yau Litinin, daga bisani sun gurfanar da shi a gaban kotu bisa zargin kalaman rashin da’a da ka iya barazana ga zaman lafiya.



yansandan sun gurfanar da shi ne a gaban kotun Majistire ta 1 kamar yadda leadership ta tabbatar.

Hukumar Shari'a ta jihar Bauchi ce ta fara tuhumar sa kan wani furucin sa da ya tayar da ƙura sosai ba ma a Jihar Bauchi ba a duk faɗin Nijeriya saboda abin da ya hukumar tace ya fadi ce'wa' Ko Manzon Allah ma ba su bukatar taimakonsa.” wanda aka nemi ya janye

Kotun ta tura shi zuwa gidan yarin ne kafin daga bisani a ci gaba da sauraron karar da ‘yansanda s**a shigar a gobe Talata.

Da yake tabbatar da kamun da aka yi wa malamin, Shugaban kungiyar Matasa Masu Neman Hadin Kan Malamai Da Cigaban Al’ummar Jihar Bauchi, Yusuf A. Jibrin, ya bayyana cewar malamin ya je wajen ‘yansanda domin amsa gayyatar da s**a yi masa ne amma daga bisani s**a gurfanar da shi a gaban kotu.

“Na san da gayyatar da aka yi wa Malam daga hukumar ‘yansanda wanda a yau da safe (Litinin) aka tabbatar mana da cewa Malam ya amsa wannan gayyatar. A da kam ma mun shirya har da ni muka ce za mu je mu yi masa rakiya. Amma da muka yi waya da Allaramma sai ya ce mana a’a malam ya ce bai bukatar kowa ya je. Zai je shi kadai da direba da Malam Ya’u.

“Dazu kuma sai shi Allaramma ya kira ni yake ce min an kai Malam gidan Yari. Yake ce min har an kaishi kotu, kotu kuma ta turashi gidan yari.”

Yusuf ya ce, dukkanin abun da ake cajin malamin nasu a kai abu ne da ya shafi akidarsu, “Wannan maganar da malam ya yi akidarmu ne a kai kuma muke fatan Allah ya karbi rayukanmu, kuma manufarmu daya kuma a kanta muke.”

A cewarsa, malaminsu ya koyar da su zaman lafiya da kwanciyar hankali, don haka za su bi dukkanin matakan da s**a dace a doron shari’a wajen nema wa malaminsu hakkinsa.

Shugaban, ya bayyana cewar su na ta kokarin kwantar wa almajiran malamin da hankali yayin da ake ci gaba da bin matakan da s**a dace wajen ganin malamin ya samu ‘yanci.

“Muna kira ga mutanenmu da su kasance cikin zaman lafiya kuma za mu bi lamarin a bisa tsarin doka domin mu tabbatar mun bi kadin abun da aka mana,” Yusuf A. Jibrin ya shaida.

Bayan kalaman malamin ne, hukumar shari’a ta jihar Bauchi ta aike da wasikar gayyata ga Malam Idris domin ya bayyana a gaban malamai domin wanke kansa ko kare kansa sai dai bayan ca! da malaman da ke goyan bayansa s**a yi hakan ya gagara ba tare da an samu yin mukabalar ba.

Ledership Hausa.

Address

Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bauchi News Daily posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share