Giade Daily Post

Giade Daily Post ๐†๐ˆ๐€๐ƒ๐„ ๐ƒ๐€๐ˆ๐‹๐˜ ๐๐Ž๐’๐“
(๐“๐š๐ฌ๐ก๐š๐ซ ๐€๐ฅ'๐ฎ๐ฆ๐ฆ๐š)
๐“๐ข๐ค๐ญ๐จ๐ค ๐Ÿ‘‰ tiktok.com/

๐–๐š๐ญ๐ฌ๐š๐ฉ๐ฉ/๐‚๐š๐ฅ๐ฅ
๐ŸŽ๐Ÿ•๐ŸŽ๐Ÿ‘๐Ÿ—๐Ÿ‘๐Ÿ—๐Ÿ–๐Ÿ‘๐Ÿ–๐Ÿ“ ๐Ÿ“ž๐Ÿ“ž
๐ŸŽ๐Ÿ•๐ŸŽ๐Ÿ’๐Ÿ–๐Ÿ’๐Ÿ–๐Ÿ“๐Ÿ–๐Ÿ‘๐Ÿ โ˜Ž๏ธโ˜Ž๏ธ

Babu Akida Babu Addini ๐Ÿ‘‡โœ…โœ๏ธ
29/09/2025

Babu Akida Babu Addini ๐Ÿ‘‡โœ…โœ๏ธ

29/09/2025

MU TATTAUNA:
Idan aka cire matsalar kudi menene kuma matsalar ka yanzu?๐Ÿ™„

PATE KAWAI 2027 TA KADDAMAR DA AIKIN MANNA POSTER NA PROF ALI PATE A KARAMAR HUKUMAR MISAU. An fara gudanar da bikin man...
29/09/2025

PATE KAWAI 2027 TA KADDAMAR DA AIKIN MANNA POSTER NA PROF ALI PATE A KARAMAR HUKUMAR MISAU.

An fara gudanar da bikin manna hotunan Professor Muhammad Ali Pate a bayan keke Napep a cikin garin Misau, karkashin jagorancin ฦ™ungiyar Pate Kawai wacce Hon. Ibrahim Makama Misau, tsohon ษ—an majalisar tarayya mai wakiltar Misau/Dambam, ke jagoranta.

Wannan shiri na ฦ™ungiyar Pate Kawai wani ษ“angare ne na yaษ—a manufofin Professor Muhammad Ali Pate da kuma nuna goyon baya gare shi a fadin jihar Bauchi. Aikin manna hotunan a jikin Napep ษ—in zai kasance ci gaba, inda aka shirya gudanar da shi a kowace ฦ™aramar hukuma da ke faษ—in jihar.

ฦ˜ungiyar ta bayyana cewa wannan aiki na ษ—aya daga cikin hanyoyin nuna ฦ™auna da goyon bayan jamaโ€™a ga Professor Muhammad Ali Pate, wanda ya zama abin alfahari ga alโ€™ummar Bauchi da Najeriya baki ษ—aya.

29/09/2025

KARATUN LITTAFIN

*AKHDA'UL MUSALLIN*
(kurakurai yayin Iqama)
DARASI NA 21

TARE DA
SHEIKH ABUBAKAR MUSA GIADE
(Hafizahullah)

DAGA MASJID UTHMAN BIN AFFAN JUMA'AT
MATSANGO AZARE.

RANAR LITININ
29-09-2025
07-04-1447

Kasance Da sautulhikma.com domin samun karatuttukan malam

JIBWIS SOCIAL MEDIA
KATAGUM L.G.A
BAUCHI STATE.

29/09/2025

Live Streaming

KARATUN LITTAFIN ADDA'U WADDAWA'U

Tare Da :--- Dr Magaji Bappha Sulaiman Azare
Darasi Na 20

Audio Na ADDA'U WADDAWA'U
๐Ÿ‘‡๐Ÿฝ
https://sautulhikma.com/book/246

Complete Audio Na Taskiyatun Nufus
๐Ÿ‘‡๐Ÿฝ
https://sautulhikma.com/book/38

๐Ÿ•Œ๐Ÿ•Œ๐Ÿ•Œ๐Ÿ•Œ๐Ÿ•Œ๐Ÿ•Œ๐Ÿ•Œ๐Ÿ•Œ๐Ÿ•Œ
Daga Masallacin Juma'a Na Aliyu ibn Abi Dalib ( Gandun Wambai Azare


WhatsApp:
https://chat.whatsapp.com/DDseaimdcqLHCFKWvf7Z5u

Telegram:
https://t.me/+hvbMBxpG5HsyNzM8

Duk Ranar Litinin Tsakanin Magariba Zuwa Isha'i

Ayi sauraro lafiya.

Ku cigaba da kasancewa da Sautul Hikma a wadannan kafafen sada zumuntar domin samun karatuttukan Maluman Sunnah a saukake.

Radio: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.sautulh.radio

Facebook:
https://mobile.facebook.com/sautulhikmang

Telegram:
https://t.me/sautul_hikma

Whatsapp:
https://chat.whatsapp.com/CbrsShDVbCzBbL4m8dh7iO

https://whatsapp.com/channel/0029VavxWFLKGGGHC2egZi2P

YouTube:
https://youtube.com/c/sautulhikmatv

Twitter:
https://twitter.com/sautulhikmang

Website:
https://sautulhikma.com

Kasance da sautulhikma.con domin samun Karatuttukan malam a saukake

Salim Yaya Azare

JIBWIS SOCIAL MEDIA Salim Yaya Katagum

International Conference Center ICC BauchiGiade Daily Post
29/09/2025

International Conference Center ICC Bauchi

Giade Daily Post

Kungiyar Malaman Jamiโ€™oโ€™i ta Kasa (ASUU) ta bai wa Gwamnatin Tarayya waโ€™adin makonni biyu domin tsunduma yajin aiki mudd...
29/09/2025

Kungiyar Malaman Jamiโ€™oโ€™i ta Kasa (ASUU) ta bai wa Gwamnatin Tarayya waโ€™adin makonni biyu domin tsunduma yajin aiki muddin ta ci gaba da sakaci kan wasu buฦ™atu da take nema a biya.

A sanarwar gargaษ—i da ASUUn ta fitar yau Litinin, ta ce daga jiya Lahadi, 28 ga watan Satumba, za ta bai wa gwamnatin waโ€™adin kwanaki 14 domin ta karkata akala kan buฦ™atun da take nema, ko kuma ta tsunduma yajin aikin gargaษ—i na makonni biyu, inda daga nan zai rikiษ—e zuwa na sai baba ta gani.

Shugaban ASUU, Farfesa Chris Piwuna, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya sa wa hannu bayan taron majalisar zartarwar ASUU na ฦ™asa da aka gudanar a jamiโ€™ar Abuja a ranar Lahadi.

Ya ce ฦ™ungiyar ta gaji da yadda Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da nuna halin ko in kula da harkar ilimi, musamman batutuwan da s**a daษ—e suna tattaunawa a kai

ASUU ta wassafa jerin buฦ™atunta da s**a haษ—a da bitar yarjejeniyar 2009 da samar da isassun kuษ—aษ—en farfaษ—o da jamiโ€™oโ€™i da biyan bashin albashin malamai da kuma samar da tsayayyen tsarin samun kuษ—aษ—en gudanarwa na jamiโ€™oโ€™i.

โ€œIna sanar da cewa, idan bayan waโ€™adin kwana 14 gwamnatin tarayya ta kasa aiwatar da waษ—annan buฦ™atu, ฦ™ungiyar za ta fara da yajin gargaษ—i na makonni biyu kafin ta shiga yajin aikin sai baba ta gani,โ€ in ji sanarwar.

FIFA ta kashewa tawogar ฦ™wallon ฦ™afar Afirka ta Kudu maki 3 bisa ojoron ษ—an wasa Hukumar ฦ™wallon ฦ™afa ta duniya, FIFA, t...
29/09/2025

FIFA ta kashewa tawogar ฦ™wallon ฦ™afar Afirka ta Kudu maki 3 bisa ojoron ษ—an wasa

Hukumar ฦ™wallon ฦ™afa ta duniya, FIFA, ta hukunta tawogar ฦ™wallon ฦ™afa ta Afirka ta Kudu, Bafana Bafana, sakamakon saka ษ—an wasa da bai cancanta ba a ษ—aya daga cikin wasannin neman cancantar shiga gasar cin Kofin Duniya da ta ke bugawa.

FIFA ta sanar da wannan hukunci ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Litinin.

Kwamitin ladabtarwa na FIFA ya tabbatar da cewa Afirka ta Kudu ta saka ษ—an wasa Teboho Mokoena, wanda bai cancanta ya buga wasan ba, a cikin wasan rukuni na C da s**a fafata da ฦ™asar Lesotho a ranar 21 ga Maris, 2025.

Kwamitin ya yanke hukunci cewa Bafana Bafana sun karya โ€œsashe na 19 na dokokin ladabtarwa na FIFA (FDC) da kuma sashe na 14 na dokokin gasar cancantar shiga Kofin Duniya na 2026.โ€

Kwamitin ya bayyana cewa a halin yanzu, an hukunta cewa Lesotho CE mai nasarar wasan da 3-0 akan Afirka ta Kudu.

An ba Lesotho maki uku daga wasan, yayin da aka rage wa Bafana Bafana maki daga 17 zuwa 14.

Wannan yasa s**a sauka zuwa matsayi na biyu a teburin rukuni, saboda bambancin kwallaye da ฦ™asar Benin, wacce ita ma tana da maki 14.

Giade Daily Post

Gwamnatin Taraiya ta ayyana Laraba a matsayin ranar hutun bikin cikar Nijeriya 65 da samun ฦดancin-kai.Olubunmi Tunji-Ojo...
29/09/2025

Gwamnatin Taraiya ta ayyana Laraba a matsayin ranar hutun bikin cikar Nijeriya 65 da samun ฦดancin-kai.

Olubunmi Tunji-Ojo, ministan harkokin cikin gida ne ya baiyana haka a wata sanarwa da Babban Sakataren ma'aikatar harkokin cikin gida, Magdalene Ajani ya sanyawa hannu.

Tunji-Ojo ya kuma taya yan Nijeriya murnar "wannan babbar rana".

Daga: Habu Ibrahim Giade

Wani gari ne nan kuma miye sunan titin?
29/09/2025

Wani gari ne nan kuma miye sunan titin?

29/09/2025

Big shout out to my newest top fans! Ibrahim Haruna, Comr Shehu Maaji Akuyam, Nura Haske Qurba, Aliyu Abubakar, Omer Can, Abbatee Saleh, Sabon Zakin Bege, Dawood Ma'aji, Abdurraman Wadabanbiyo Wada, Yusuf Sh*tu, Abdulkadir Officer, Real M Ozil Sakajiki I, Saadu Mahmood Sk, Abdulkadir Musa Giade, Abdulmusawwir Sulaiman Dass, Habibu Danfillo Miya, Muhammad Nuruddeen Mukhtar, mustapha Adam, Ibrahim Muhammad, Ibrahim Accountants Kusada, Mรผhd ร‹smรฃรฏl B Gรฏรฃdรซ, Auwalu Saleh, Abubakaryusufbaba Gyd, Abul Ihsan Ama, Abubakar Sadeeq, Sani Da'u Alaska Tsatsumburum, Abubakar Usman, Kabiru Muhammad, Abdulhakeem Abubakar Yareema, Umar Sale, Abdulrahman Dan Dadey, Mohammed M Aliyu, Khalipha Abba, Profe Muhammad Adamu Mu'azu, Adamu Gambo, Ahmad Tijjani Lawan, Aminu Salisu, Muhd Suraj, Ahmad Muhammad Adam, Sani Abubakar, Baba Ibrahim Dango, Sulaiman Haruna, Muhammad Umar Bello, Expecter Nuhu Ibrahim, Jibrin Jikan Harikangere, Abdulrashid Saleh, Yunusa Yakubu Bununu, Sarkin Matasa Fathers, Jamila Ismail, Adamu Ibrahim Aliyu

Address

Giade Local Government
Bauchi
2023

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Giade Daily Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Giade Daily Post:

Share