Global Access Hausa

Global Access Hausa Online Newspaper

Ray Ban AI Glass da aka sace wa Sowore a lokacin da yake zangar-zangar   jiya a Abuja. Kuɗinsa ya kai kimanin Naira dubu...
22/07/2025

Ray Ban AI Glass da aka sace wa Sowore a lokacin da yake zangar-zangar jiya a Abuja. Kuɗinsa ya kai kimanin Naira dubu ₦855,000.

Ga kaɗan daga cikin amfaninsa:

1. Yana iya ɗaukar Hoto ko Bidiyo mai kyau ba tare da amfani da waya ba.

2. Zaka iya bashi umarni kamar kace: "AI take a photo” Or “Record a video"

2. Zaka iya yin live video kai tsaye a Facebook ko Instagram daga tabarau.

3. Yana da AI Assistant, zaka iya tambayarsa da murya kamar haka: "Translate this sign for me." "Read this text for me". Or What kind of object is this?" da dai sauransu.

4. AI Glass ɗin zai iya gaya maka abin da yake gani a gaban ka!

5. Zai iya karanta rubutu a bango ko a takarda da murya, misali: "Rubutun turanci, Faransanci, ko wani harshe daban ya fassara maka.

6. Zaka iya karɓar kira ko aika saƙonni ta WhatsApp, Messenger da Instagram ta amfani da murya.

7. Yana da speaker mai magana da Microphone a cikin tabarau, zaka iya jin kiɗa kai tsaye ba tare da amfani da "Earpiece" ba.

Naxeer Kaoje ✍️

Copied

Da dumi'dumi: Shugaba Muhammadu Buhari ya Saki Aisha Buhari kafin ya rasu -Farooq Kperogi Shahararren marubucin nan dake...
16/07/2025

Da dumi'dumi: Shugaba Muhammadu Buhari ya Saki Aisha Buhari kafin ya rasu -Farooq Kperogi

Shahararren marubucin nan dake zaune ƙasar Amurka Farooq Kperogi ya bayyana a shafinsa yana mai cewa Jama’a na ta yada wata magana da aka danganta ga Aisha Buhari, inda suke cewa Buhari ya nemi ta nemi gafarar ‘yan Najeriya a madadinsa.

Ba zan iya tabbatar da ingancin wannan ikirari ba, amma abin da na sani shi ne kafin rasuwar Buhari, shi da Aisha babu aure.

Sun rabu, Aisha ta koma sunanta Aisha Halilu.

Idan ka lura da kyau za ka ga Aisha ba ta je Daura ba a lokacin da ya yi ritaya zuwa garin bayan ya bar ofis. Shi ma Buhari shi kadai ne daga baya ya koma Kaduna.

Hasali ma lokacin da ya kamu da rashin lafiya aka ce Aisha ta tafi Landan don ta kula da shi, sai aka ce ta hakura saboda ba matarsa ba ce. A ƙarshe ta tafi cikin ƴan kwanaki kafin ya mutu, amma sai bayan lallashi mai tsanani.

Ko a yanzu, a wannan lokacin na baƙin ciki, da alama ta sami sabani game da aikinta.

Don haka ina matukar sha’awar sanin yaushe da kuma inda Buhari ya ce mata ta roki ‘yan Nijeriya a gafarta musu. A ina ma ta ce wannan?

13/06/2025

Kano ta dabo tumbin giwa, akwai garuruwan Krista da Musulmi Bai Isa yaje Da'awa wajen ba haka kazalika akwai garuruwan Musulmai wadda Krista Bai Isa yaje Da'awa wajen ba.

Babban Limanin  Cocin Katolika na Garin Yola a Jihar Adamawa Ya Gina Masallaci ya ba  Musulmai  Suyi Sallah a Ciki. A wa...
12/06/2025

Babban Limanin Cocin Katolika na Garin Yola a Jihar Adamawa Ya Gina Masallaci ya ba Musulmai Suyi Sallah a Ciki.

A wani gagarumin aikin jin kai da sadaukar da kai ga hadin kan addinai, Bishop Stephen Dami Mamza na Cocin Katolika na garin Yola a Jihar Adamawa, ya kare matakin da ya dauka na gina masallaci ga musulmin da rikicin Boko Haram ya rabasu da muhallansu a jihar Adamawa.

Da yake jawabi a wata hira da aka yi da shi a ranar 6 ga watan Yuni 2025, Bishop Mamza yace abinda ya bashi sha'awar gina Masallaci shine a lokacin da yakin boko Haram ya tsananta a Jihar Adamawa dubban Kirista da Musulmai ne s**a nemi mafaka a babban cocin Katolika na St. Theresa’s Cathedral da ke garin Yola sai na lura a cikin harabar babban cocinmu akwai coci, makaranta, da kuma asibiti. Amma yan'uwanmu Musulmai ba su da masallaci sai nayi tunani ya dace kawai a samar musu da wurin ibada domin kasancewa cikin al'ummarmu, wasu ma daga zuri'a daya ne akwai Musulmi da Krista. Don haka na yi amfani da kudaden Cocinmu wajen gina musu masallaci.

Wannan karimcin da wannan Limamin Cocin yayi mutane da yawa sun yaba mishi a matsayin gwarzo mai son zaman lafiya.

𝐒𝐡𝐚𝐧𝐯𝐢𝐡 𝐈𝐛𝐫𝐚𝐡𝐢𝐦 𝐓𝐚 𝐙𝐚𝐦𝐚 𝐀𝐛𝐢𝐧 𝐀𝐥𝐟𝐚𝐡𝐚𝐫𝐢 𝐰𝐚 𝐉𝐚𝐡𝐚𝐫 𝐁𝐚𝐮𝐜𝐡𝐢Yayinda kowace jaha a faɗin Tarayyar Najeriya ke koƙrin ganin cewa ...
12/06/2025

𝐒𝐡𝐚𝐧𝐯𝐢𝐡 𝐈𝐛𝐫𝐚𝐡𝐢𝐦 𝐓𝐚 𝐙𝐚𝐦𝐚 𝐀𝐛𝐢𝐧 𝐀𝐥𝐟𝐚𝐡𝐚𝐫𝐢 𝐰𝐚 𝐉𝐚𝐡𝐚𝐫 𝐁𝐚𝐮𝐜𝐡𝐢

Yayinda kowace jaha a faɗin Tarayyar Najeriya ke koƙrin ganin cewa ta samu wakilci a ɓangarori daban-daban, Shanvih Ibrahim, ta kasance jakadiyar Jahar Bauchi a ɓangaren ƙwallon ƙafar mata.

𝐖𝐚𝐜𝐞𝐜𝐞 𝐢𝐭𝐚 𝐤𝐮𝐦𝐚 𝐝𝐚𝐠𝐚 𝐢𝐧𝐚 𝐭𝐚𝐟𝐢𝐭𝐨 ? Shanvih Ibrahim, ƴar asalin Jahar Bauchi, daga garin Boi, Ƙaramar Hukumar Bogoro.

Ta kasance ɗaya daga cikin jerin ƴan wasan ƙwallon ƙafar matan Najeriya, kuma zata wakilci Najeriya a Gasar cin kofin Duniya na mata ƴan shekara 17 zuwa ƙasa.

Ta zama abin koyi ga na baya kuma abin alfahari ga Jahar Bauchin Yakubu, Arewa Maso Gabas, da Arewacin Najeriya.

Wuce fata kuke yi mata ?

Bauchi International-News
9th June, 2025.

Mutumin da Ya Kirkiro  Maganin Zubar da Ciki (abortion) Ya Mutu Ƙwararren mai binciken kimiyya wanda ya ƙirƙiri maganin ...
01/06/2025

Mutumin da Ya Kirkiro Maganin Zubar da Ciki (abortion) Ya Mutu

Ƙwararren mai binciken kimiyya wanda ya ƙirƙiri maganin zubar da ciki a 1984, Étienne-Émile Baulieu ya mutu yana da shekara 98 a duniya.

Maganin da ya ƙirƙiro, Mifepristone ya kawo sauyi a tsarin haihuwa a duniya.

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Yakubu Dogara A Matsayin Shugaban Hukumar NCGC Don Ƙarfafa Karɓar Bashi Ga ‘Yan KasuwaShugaban Ƙa...
29/05/2025

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Yakubu Dogara A Matsayin Shugaban Hukumar NCGC Don Ƙarfafa Karɓar Bashi Ga ‘Yan Kasuwa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin tsohon Kakakin Majalisar Wakilai na Ƙasa, Rt. Hon. Yakubu Dogara, a matsayin Shugaban Hukumar National Credit Guarantee Company Limited (NCGC). Wannan naɗi na zuwa ne a daidai lokacin da aka kaddamar da sabuwar hukuma da nufin sauƙaƙa wa ‘yan kasuwa karɓar bashi daga cibiyoyin kuɗi a Najeriya.

A cikin jerin naɗe-naɗen da Shugaban Ƙasa ya amince da su, an kuma naɗa Mr. Bonaventure Okhaimo a matsayin Manajan Darakta kuma Babban Shugaban Hukuma (MD/CEO) na kamfanin.

Kamfanin National Credit Guarantee Company Limited (NCGC) da Shugaba Tinubu ya ƙaddamar, na da cikakken goyon bayan gwamnatin tarayya, tare da wani babban tallafin farko na naira biliyan ɗari (₦100bn).

Babban burin wannan hukuma shi ne rage hadarin da bankuna da cibiyoyin ba da rance ke fuskanta wajen ba da bashi, musamman GaKanana da matsakaitan masana’antu (MSMF ‘Yan kasuwa masu zaman kansu Masana’antun cikin gida
Masu sana’o’in hannu Da manyan kamfanoni masu buƙatar tallafin jari

Wannan mataki na daga cikin manyan manufofi da Shugaba Tinubu ke aiwatarwa domin Farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa ta hanyar ba da dama ga ‘yan ƙasa da ke da ƙwazo amma ba su da isasshen jarin farawa ko faɗaɗa kasuwancinsu.

Za'a yi Janaizan Rev. Dauda Ayuba Azzaman Ran 31 ga watan Mayu 2025 a Jihar Kaduna.A wani sanarwa daga Cocin King Worshi...
27/05/2025

Za'a yi Janaizan Rev. Dauda Ayuba Azzaman Ran 31 ga watan Mayu 2025 a Jihar Kaduna.

A wani sanarwa daga Cocin King Worship Chapel And Ministry Inc. dake lamba 72 titin Kunai daura da hanyar post office a Jihar Kaduna Wanda Global Access Hausa ta samu da cewa za'a yi Janaizan Shararen Malamin Addinin Kristan nan Wanda ya Rasu a hatsarin mota Rev. Dauda Azamman Ran 31 ga watan Mayu 2025 a Jihar Kaduna.

Za'a fara da Sujadar wake keep ranar Jumma'a 30 ga watan Mayu 2025 da karfe 4 na yamma a makarantar Firamaren Gobnati na Ungwan Sabo dake GRA a Jihar Kaduna.

Za'a mishi Sallah irin ta Addinin Krista washegari ran 31 ga watan Mayu 2025 da karfe 10 na safe a
Cocin King Worship Chapel And Ministry Inc. dake lamba 72 titin Kunai daura da hanyar post office a Jihar Kaduna kafin ayi Janaizarsa a ranan a makabartan Kristoci na Barnawa.

In ba'a manta ba a ranar 26 ga Mayu, 2025 Global Access Hausa ta sami labari cewa Rev. Dauda Ayuba Azzaman ya rasu sakamakon haɗarin mota yayin da yake tafiya daga Jihar Benue zuwa Kaduna.

Rasuwarsa ya girgiza Kristocin Nijeriya, inda da dama daga cikinsu sun daukeshi a matsayin mai wa'azi addinin Krista cikin ƙwazo da kuma mai tsayawa tsayin daka wajen kare hakin Kiristoci a Nijeriya.

Mashahuren Malaman Addinin Krista Guda  Biyu a Arewacin Nijeriya da Mutuwarsu a Lokuta Dabam Dabam ya Girgiza Kristocin ...
26/05/2025

Mashahuren Malaman Addinin Krista Guda Biyu a Arewacin Nijeriya da Mutuwarsu a Lokuta Dabam Dabam ya Girgiza Kristocin Nijeriya.

Madalla Kadiri Daga Bauchi

Baba Paul Gindiri da Kuma Rev. Dauda Ayuba Azzaman Mashahuren Malaman Addinin Krista ne a Arewacin Nijeriya da s**a yi kaurin suna ta wurin kiran mutane Zuwa ga addinin Krista. Salon da'awarsu yayi K**a da na juna, Mutuwarsu a Lokuta Dabam Dabam ya Girgiza Kristocin Nijeriya.

Baba Paul Gindiri

Baba Paul Gindiri, wanda aka fi sani da Evangelist Paul Gindiri, ya kasance ɗaya daga cikin fitattun masu wa'azin Kiristanci a Arewacin Najeriya a karni na 20. An haife shi a ranar 3 ga Maris, 1935, a ƙauyen Punbush (Kasuwan Ali), kusa da Gindiri, a Jihar Filato. Ya fito ne daga kabilar Pyem da ke karamar hukumar Mangu.

Bayan ridda da yayi daga addinin Islama zuwa addinin Kirista, Baba Paul Gindiri ya zama mashahurin mai wa'azin addinin Krista mai tsauri, wanda ya ke kira ga mutane su tuba daga zunubansu kuma su bi Yesu Kristi. Ya yi amfani da harshen Hausa wajen isar da saƙonninsa, wanda hakan ya ba shi damar isa ga jama'a da dama a Arewacin Najeriya. Wa'azinsa ya haifar da sauye-sauye masu yawa, inda mutane da dama s**a karɓi Kiristanci.

Baba Paul Gindiri ya rasu a shekarar 1996, amma tasirinsa ya ci gaba da rayuwa ta hanyar mabiya da kuma al'ummomin Kirista da ya taimaka wajen kafa su. An san shi da ƙwazo, tsoron Allah, da kuma jajircewa wajen yada bishara duk da ƙalubale da ya fuskanta.

Rev. Dauda Ayuba Azamman.

Rev. Dauda Ayuba Azzaman (wanda kuma ake kira Pastor David Ayuba Azzaman) ya kasance babban malamin addinin Kirista daga Arewacin Najeriya, wanda ya yi fice wajen wa'azin bishara da kare imanin Kirista. Ya kasance babban mai wa'azi a The King Worship Chapel and Ministry, Inc., da ke Kaduna, Jihar Kaduna, Najeriya.

Rev. Azzaman ya kammala digirinsa na farko a fannin Noma daga Jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Daga nan ya halarci Rhema Bible College, Kaduna Campus, tsakanin 2016 zuwa 2017. A halin yanzu yana ci gaba da karatun digiri na biyu.

Bayan kammala hidimar kasa a Damaturu, Jihar Yobe, Rev. Azzaman ya yi aiki a matsayin malamin Kimiyyar Noma a Federal Government Girls College, Bakori, Jihar Katsina daga 2000 zuwa 2004. Daga nan ya shiga harkar banki, inda ya yi aiki a Lion Bank da Diamond Bank (wanda yanzu ya zama Access Bank) daga 2004 zuwa 2015. Ya yi aiki a wurare daban-daban ciki har da Port Harcourt, Abuja, da Kafanchan.

Kyaututtuka da Lambar Yabo

Rev. Azzaman ya samu lambobin yabo da dama, ciki har da:

National Best Teacher Rice Essay Competition Award (2004)

Diamond Bank Best Customer Service Award (2010)

Diamond Bank Long Service Award (2016)

Christian Advocacy Award (2021)

Harbinger Of Christ To The World Award (2022)

A matsayinsa na mai bishara, Rev. Azzaman ya gudanar da ayyukan mishan a wurare da dama ciki har da Shanga (Jihar Kebbi), Rijau (Jihar Neja), da Panda (Jihar Nasarawa). Ayyukansa sun haifar da kafa filayen mishan guda biyu a Kebbi da Neja. Ya yi aure da Agatha Raymond Angani, kuma suna da 'ya'ya hudu: Ann, Irene, Asa, da Jada.

A ranar 26 ga Mayu, 2025, an ruwaito cewa Rev. Dauda Ayuba Azzaman ya rasu sakamakon haɗarin mota yayin da yake tafiya daga Jihar Benue zuwa Kaduna. Rasuwarsa ta girgiza al'umma da dama, inda aka bayyana shi a matsayin mai wa'azi mai ƙwazo da kuma mai tsayawa tsayin daka wajen kare imanin Kirista.

Takaitacen Tarihin Rev. Dauda Ayuba Azamman.  Rev. Dauda Ayuba Azzaman (wanda kuma ake kira Pastor David Ayuba Azzaman) ...
26/05/2025

Takaitacen Tarihin Rev. Dauda Ayuba Azamman.

Rev. Dauda Ayuba Azzaman (wanda kuma ake kira Pastor David Ayuba Azzaman) ya kasance babban malamin addinin Kirista daga Arewacin Najeriya, wanda ya yi fice wajen wa'azin bishara da kare imanin Kirista. Ya kasance babban mai wa'azi a The King Worship Chapel and Ministry, Inc., da ke Kaduna, Jihar Kaduna, Najeriya.

Rev. Azzaman ya kammala digirinsa na farko a fannin Noma daga Jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Daga nan ya halarci Rhema Bible College, Kaduna Campus, tsakanin 2016 zuwa 2017. A halin yanzu yana ci gaba da karatun digiri na biyu.

Bayan kammala hidimar kasa a Damaturu, Jihar Yobe, Rev. Azzaman ya yi aiki a matsayin malamin Kimiyyar Noma a Federal Government Girls College, Bakori, Jihar Katsina daga 2000 zuwa 2004. Daga nan ya shiga harkar banki, inda ya yi aiki a Lion Bank da Diamond Bank (wanda yanzu ya zama Access Bank) daga 2004 zuwa 2015. Ya yi aiki a wurare daban-daban ciki har da Port Harcourt, Abuja, da Kafanchan.

Kyaututtuka da Lambar Yabo

Rev. Azzaman ya samu lambobin yabo da dama, ciki har da:

National Best Teacher Rice Essay Competition Award (2004)

Diamond Bank Best Customer Service Award (2010)

Diamond Bank Long Service Award (2016)

Christian Advocacy Award (2021)

Harbinger Of Christ To The World Award (2022)

A matsayinsa na mai bishara, Rev. Azzaman ya gudanar da ayyukan mishan a wurare da dama ciki har da Shanga (Jihar Kebbi), Rijau (Jihar Neja), da Panda (Jihar Nasarawa). Ayyukansa sun haifar da kafa filayen mishan guda biyu a Kebbi da Neja. Ya yi aure da Agatha Raymond Angani, kuma suna da 'ya'ya hudu: Ann, Irene, Asa, da Jada.

A ranar 26 ga Mayu, 2025, an ruwaito cewa Rev. Dauda Ayuba Azzaman ya rasu sakamakon haɗarin mota yayin da yake tafiya daga Jihar Benue zuwa Kaduna. Rasuwarsa ta girgiza al'umma da dama, inda aka bayyana shi a matsayin mai wa'azi mai ƙwazo da kuma mai tsayawa tsayin daka wajen kare imanin Kirista.

Global Access Hausa tana mika ta''aziya wa Kristocin Arewa bisa wànnan Babban rashi.

20/05/2025

Fatawa Aka Basu idan duk laifin dakayi ko Sata ko Halakar da Bayin Allah idan Sunje Aikin Hajj Za a Yafe Musu
😹😹

Shugaba Tinubu ya gana da Peter Obi, Fayemi a fadar VaticanShugaban kasa Bola Tinubu, Mista Peter Obi, dan takarar shuga...
18/05/2025

Shugaba Tinubu ya gana da Peter Obi, Fayemi a fadar Vatican

Shugaban kasa Bola Tinubu, Mista Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, da tsohon gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi, sun gana a wajen taron rantsar da Paparoma Leo na 14 a ranar Lahadi a birnin Rome.

Address

Bauchi

Opening Hours

Monday 09:00 - 23:00
Tuesday 09:00 - 23:00
Wednesday 09:00 - 23:00
Thursday 09:00 - 23:00
Friday 09:00 - 23:00
Saturday 09:00 - 23:00
Sunday 09:00 - 23:00

Telephone

+2348117992681

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Global Access Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Global Access Hausa:

Share