Albarka Radio

Albarka Radio Albarka Radio 97.5 FM is a Nigerian English and Hausa Radio Station based in and broadcasting from Bauchi, Bauchi State, Nigeria.
(2)

Catch us Live on TuneIn, Radio Garden or visit live.albarkaradio.com to Listen to us Live Online. Albarka Radio 97.5 FM Bauchi is a Nigerian English and Hausa radio station based in Bauchi, Bauchi State. It was founded and owned by Arrowhead Global Communication services Limited. Renowned for its humorous approach to broadcasting, the station broadcast a mixture of news, features, sport, entertain

ments, talk shows, topical issues and interviews. and also promote businesses through advertisement. Mission
As an independent broadcast station, Albarka radio shall reflect and promote all sides of issues and opinions and build a tradition of trust and credibility with our audience. Vision
To be a reference point in quality radio broadcasting in Nigeria using the professional ethics of balance and fairness to motivate the listeners.

Kiran ya biyo bayan labarin da muka wallafa kan karin albashin kashi dari cikin dari da aka yiwa Likitoci da sauran ma'a...
13/12/2025

Kiran ya biyo bayan labarin da muka wallafa kan karin albashin kashi dari cikin dari da aka yiwa Likitoci da sauran ma'aikatan jinya inda Hamisu Aliyu ya ce; "Allah yasa Malaman firamare ma ayi musu haka" yayin da shi kuwa Salisu Halilu kuwa ya ce; "Su kuma Malaman Firamare su ce yaya kenan. Allah ka zama gatansu ameen."

Suhailu Abubakar da shima ya yi tsokaci a karkashin labarin ya ce "Malaman makaranta Sun fi cancantar hakan domin kowa sai da ya bi ta wajensu ya zama abinda ya zama", yayin da ita kuwa Maryam Aliyu Abubakar ta rubuta cewa "Malamai magada annabawa".

Ana ci gaba da gudanar da gwaje-gwaje, bayar da magunguna, rarraba gilashi da kuma yin aikin ido kyauta ga masu fama da ...
13/12/2025

Ana ci gaba da gudanar da gwaje-gwaje, bayar da magunguna, rarraba gilashi da kuma yin aikin ido kyauta ga masu fama da cututtukan ido a ƙananan hukumomin Alkaleri da Kirfi na Jihar Bauchi.

Shirin na gudana ne ƙarƙashin tallafin Honarabul AKY (Makaman Duguri), ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Alkaleri/Kirfi a Majalisar Wakilai ta tarayya, a wani yunkuri na rage matsalar ciwon ido da kuma inganta lafiyar al’umma a yankin.

Rahotanni sun nuna cewa shirin ya samu karɓuwa matuƙa daga jama’a, inda dubban mazauna yankin ke cin gajiyar gwaje-gwajen ido, magunguna, gilashi da kuma aikin ido kyauta, lamarin da ya rage musu wahalar kashe kuɗaɗe wajen neman irin waɗannan ayyukan lafiya.

Wasu daga cikin waɗanda s**a amfana sun bayyana farin cikinsu da jin daɗinsu bisa wannan tallafi, inda s**a yaba da ƙoƙarin ɗan majalisar wajen kawo ayyukan jin ƙai kai tsaye zuwa ga al’umma.

Sun kuma yi addu’ar Allah ya saka masa da alheri, ya ƙara masa lafiya da ƙarfin gwiwa domin ci gaba da aiwatar da ayyukan raya mazabar.

Masu ruwa da tsaki a yankin sun bayyana cewa irin wannan shiri zai taimaka matuƙa wajen rage matsalolin makanta da sauran cututtukan ido, tare da ƙarfafa gwiwar jama’a kan muhimmancin kula da lafiyar ido.

Shirin na daga cikin manyan tsare-tsaren kiwon lafiya da Hon. AKY (Makaman Duguri) ke tallafawa domin inganta rayuwar al’ummar mazabar Alkaleri/Kirfi.

Gwamnatin Jihar Bauchi ta amince da ƙarin albashi da kashi 100 cikin 100 ga likitoci da sauran ma’aikatan lafiya, a wani...
13/12/2025

Gwamnatin Jihar Bauchi ta amince da ƙarin albashi da kashi 100 cikin 100 ga likitoci da sauran ma’aikatan lafiya, a wani yunkuri na dakile yawaitar barin aiki da kwararrun ma’aikatan lafiya zuwa wasu jihohi ko ƙasashen waje, abin da aka fi sani da “Japa”.

An yanke wannan matsaya ne a taron Majalisar Zartarwa ta Jihar Bauchi, kamar yadda Kwamishinan Lafiya, Muhammad Sani Dambam, ya shaidawa manema labarai a ranar Asabar bayan kammala taron a Fadar Gwamnati, Bauchi.

Kwamishinan ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan nazari kan shawarwarin da wani kwamiti na musamman da aka kafa domin tantance tasirin kuɗi na aiwatar da sabon tsarin ga ma’aikatan lafiya ya gudanar.

Ya ce sakamakon wannan nazari ya haifar da cikakken ƙarin albashi a tsarin da ake da shi, inda ya bayyana hakan a matsayin ɗaya daga cikin manyan tsare-tsaren jin dadi da walwalar da aka taɓa amincewa da su a bangaren lafiya a jihar.

A cewarsa, an ɗauki wannan mataki ne domin riƙe ƙwararrun ma’aikatan lafiya da kuma kyautata ingancin ayyukan jinya, musamman a daidai lokacin da ake fuskantar yawaitar ficewar likitoci zuwa wasu wurare.

A cikin sabon kunshin, gwamnatin ta kuma amince da gabatar da wasu ƙarin alawus-alawus na musamman, ciki har da alawus na aiki a wuraren da ke wajen manyan birane, domin ƙarfafa likitoci da sauran ma’aikatan lafiya su karɓi aiki tare da ci gaba da zama a irin waɗannan yankuna.

Haka kuma, Kwamishinan ya ƙara da cewa ma’aikatan lafiya da ke ƙarƙashin Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Jihar Bauchi za su amfana da waɗannan alawus-alawus, lamarin da zai kawo ƙarshen bambance-bambancen da aka daɗe ana fuskanta wajen jin daɗin aiki a fannin.

Ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da biyan bashin kuɗaɗen ƙarin girma (promotion arrears) ga ma’aikatan lafiya, inda fiye da ma’aikata 2,000 ake sa ran za su ci gajiyar hakan.

Domin ƙara ɗaga ƙwarin gwiwar ma’aikatan, Kwamishinan ya ce gwamnati ta amince da ba su damar samun rancen sayen mota da gida, domin rage musu matsin tattalin arziƙi da inganta rayuwarsu.

A ƙarshe, ya bayyana cewa za a fara amfani da tsarin tantancewa na zamani (biometric attendance and verification) a cibiyoyin lafiya a faɗin jihar, a matsayin wani ɓangare na matakan tabbatar da gaskiya, ɗaukar nauyi da kuma inganta ayyukan lafiya.

13/12/2025

Sanarwar gayyatar daurin auren 'yar Farfesa Zubairu Abubakar Madaki daga Al'mustapha Haji Sufi

Duk wanda ya san wannan mata mai suna Hafsat Garba Ahmed, ya sanar da ita cewa an tsinci jakar hannu (purse) ɗauke da ho...
13/12/2025

Duk wanda ya san wannan mata mai suna Hafsat Garba Ahmed, ya sanar da ita cewa an tsinci jakar hannu (purse) ɗauke da hoton da ke ƙasa da kuma sauran muhimman abubuwa dake ɗauke da sunan Hafsat Garba Ahmed.

Idan Allah ya sa an dace, a tuntubi 08067197174 ko kuma sashin cikiya da sanarwa na Albarka Radio.

Wani masharhanci kan al'amuran yau da kullum, Comrade Sabo Mohammed, ya bayyana cikakken goyon bayansa ga kudurin da ke ...
13/12/2025

Wani masharhanci kan al'amuran yau da kullum, Comrade Sabo Mohammed, ya bayyana cikakken goyon bayansa ga kudurin da ke gaban Majalisar kasa na sauya Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU), Bauchi daga jami’ar kimiyya da fasaha zuwa jami’ar gama garia (conventional university).

Comrade Sabo ya bayyana hakan ne a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya shawarci bangarorin da ke goyon baya da kuma masu adawa da kudurin da su kasance masu nutsuwa, fahimta mai zurfi, da gabatar da hujjoji na gaskiya wajen kare matsayinsu a wannan muhawara ta kasa.

Ya ce a matsayinsa na tsohon dalibin ATBU, uwa-uba a fannin ilimi, kuma wanda ya shafe kusan shekaru goma yana aiki a jami’ar, tare da rike mukamai daban-daban a kungiyar ASUU da kuma wakiltar ma’aikatan jami’ar a majalisar koli ta Jami'ar (Senate) na tsawon shekaru biyu ba tare da katsewa ba, ba zai amince da duk wani mataki da zai rage kima, martaba da darajar ilimi da masana ba, musamman ma matsayin farfesa.

A cewarsa, yana cikakken goyon baya ga matakin sauya tsarin jami’ar, yana mai jaddada cewa hujjojin da masu goyon bayan kudurin s**a gabatar sun gamsar, musamman bayanan da Sanata Shehu Buba, mai daukar nauyin kudurin, ya gabatar a yayin taron sauraron ra’ayoyin jama’a da aka gudanar ranar Alhamis, 11 ga watan Disamba na shekarar 2025 a Abuja. Ya kuma tabbatar da cewa ya mika nasa bahasin ga kwamitin Majalisar dattawa mai kula da manyan makarantu da Asusun tallafawa manyan Makarantu TETFUND.

Comrade Sabo ya bukaci masu adawa da kudurin da su fito karara su bayyana, da hujjoji masu karfi, amfanin da ake ikirarin sauyin zai kawar, da kuma yadda sauyin zai iya cutar da ci gaba da makomar jami’ar.

Haka kuma ya ce ya dace su gamsar da jama’a da hujjoji na zahiri, ba wai kalaman siyasa ba, kan cewa sauyin zai iya rage karfafa ilimin kimiyya da fasaha a yanayin kasuwar ayyukan yi ta duniya.

A karshe, ya jaddada cewa ATBU mallakin kowa ce, ba ta wani bangare ko rukuni kadai ba, don haka ya dace a tattauna wannan batu bisa gaskiya, ilimi da mutunta ra’ayoyi, kamar yadda masana ke da dabi’ar yi.

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai sun dakile wani hadin gwiwar hari da ‘yan ta’addar ISWAP s**a kai a wani sansanin s...
13/12/2025

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai sun dakile wani hadin gwiwar hari da ‘yan ta’addar ISWAP s**a kai a wani sansanin soji na gaba (FOB) da ke Mairari a Jihar Borno, inda s**a kashe da dama daga cikin ‘yan ta’addan.

Rahotanni sun bayyana cewa harin ya faru ne a daren Jumma’a, 12 ga watan Disamba, ns shekarar 2025, zuwa safiyar Asabar, 13 ga watan Disamba, na shekarar 2025. Sojojin sun gano yunkurin ‘yan ta’addan na kutsawa cikin sansanin ne ta hanyar amfani da motoci biyu da aka dasa bama-bamai, amma aka gano su cikin gaggawa tare da lalata su kafin su kai ga cimma manufarsu.

A wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar Hadin Gwiwa ta Arewa Maso Gabas, Laftanar Kanal Sani Uba, ya fitar, ya ce an dakile harin ne ta hanyar hadin gwiwar sojojin kasa da na sama, lamarin da ya yi matukar rage karfin ayyukan ISWAP a yankin.

Ya ce hotunan kyamarori da kuma binciken da aka gudanar a filin daga sun tabbatar da cewa da dama daga cikin ‘yan ta’addan sun mutu, yayin da wasu s**a jikkata, inda ragowar s**a tsere dauke da gawarwaki da wadanda s**a jikkata.

Bayan dakile harin, sojojin Sashi na Uku na Operation Hadin Kai, tare da hadin gwiwar Rukunin Daukar Matakin Gaggawa, ‘yan sanda na musamman, da kuma rundunar Civilian Joint Task Force, sun gudanar da bincike mai zurfi a yankin.

A yayin aikin, an gano gawar ‘yan ta’adda da dama tare da kwace makamai da kayan aiki da s**a hada da bindigogi kirar AK-47, alburusai, gurneti, babura, kayan sadarwa, kayan yaki, kayayyakin jinya da sauran kayan da ke nuna shirin kai hare-hare na dogon lokaci.

Laftanar Kanal Sani Uba ya kara da cewa lalata motocin bama-baman biyu ya jawo barna a wasu sassan hanya, amma ba a samu kutsawa cikin sansanin soji ba, abin da ke nuna shiri da jajircewar sojojin.

Ya tabbatar da cewa sojoji na ci gaba da zagaye da sintiri mai tsanani a yankin domin hana duk wani sabon hari, tare da kwantar wa al’ummar yankin hankali kan ci gaba da tsaro.

A karshe, rundunar ta jaddada kudirinta na kakkabe dukkan ‘yan ta’adda da kuma dawo da dorewar zaman lafiya da kwanciyar hankali a Arewa Maso Gabas, tana mai cewa wannan nasara ta nuna kwarewa da jajircewar jami’an tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Bayan Titin Sam Njoma da ke cikin garin Bauchi, shin akwai wani t**i da wutar layinsa ke amfani da hasken rana (solar) k...
13/12/2025

Bayan Titin Sam Njoma da ke cikin garin Bauchi, shin akwai wani t**i da wutar layinsa ke amfani da hasken rana (solar) ko kuma duka man diesel suke sha akan kimanin Naira Dubu daya akan kowacce lita?

NOA, NBC Move to Nationalise Cartoons to Promote Nigerian CultureBy Ude Ogbonnaya Israel The National Orientation Agency...
13/12/2025

NOA, NBC Move to Nationalise Cartoons to Promote Nigerian Culture

By Ude Ogbonnaya Israel The National Orientation Agency has inaugurated a joint committee with the National Broadcasting Commission to drive the nationalisation of cartoons in Nigeria, a policy aimed at reshaping children’s media consumption and strengthening cultural identity. The seven-member committee was inaugurated by NOA Director-General, Mallam Lanre Issa-Onilu, who described the initiative as a strategic move to preserve Nigerian culture, promote shared values, and reorient young people through locally relevant animated content....

By Ude Ogbonnaya Israel The National Orientation Agency has inaugurated a joint committee with the National Broadcasting Commission to drive the nationalisation of cartoons in Nigeria, a policy aimed at reshaping children’s media consumption and strengthening cultural identity. The seven-member co...

Daya daga cikin aikin hanya da yayi nisa a daya daga cikin sabbin unguwannin cikin garin Bauchi. Zabi daya a ciki idan k...
13/12/2025

Daya daga cikin aikin hanya da yayi nisa a daya daga cikin sabbin unguwannin cikin garin Bauchi. Zabi daya a ciki idan ka gane wajen:

A. Madina Quarters
B. Magaji Quaters
C. Gwallagan Mayaki
D. Yelwa zuwa Lushi
E. Babu ko daya

Governor Bala Insists on Transparent Recruitment, Engages Stakeholders on 10,000 JobsBy Mubarak Aliyu Kobi Bauchi State ...
13/12/2025

Governor Bala Insists on Transparent Recruitment, Engages Stakeholders on 10,000 Jobs

By Mubarak Aliyu Kobi Bauchi State Governor, Bala Abdulkadir Mohammed, has taken a firm stand against secret hiring as the government prepares to roll out the first phase of its 10,000 civil service recruitment. In a closed-door session with key political and administrative stakeholders, the governor said the meeting was designed to protect the process from favoritism and political interference. He revealed that the Head of Service had identified 214 job categories with 5,669 vacancies ready to be filled across various ministries and agencies....

By Mubarak Aliyu Kobi Bauchi State Governor, Bala Abdulkadir Mohammed, has taken a firm stand against secret hiring as the government prepares to roll out the first phase of its 10,000 civil service recruitment. In a closed-door session with key political and administrative stakeholders, the governo...

Malam Bashir Muhammed  yana cikiyar dansa mai suna Ibrahim Bashir Wanda ya fita daga gida a garin Azare da ke karamar hu...
13/12/2025

Malam Bashir Muhammed yana cikiyar dansa mai suna Ibrahim Bashir Wanda ya fita daga gida a garin Azare da ke karamar hukumar Katagum a jihar Bauchi tun ranar Jumu'a 5 ga watan Disamba na shekarar 2025.

A don haka ne yake rokon duk wanda Allah yasa ya ganshi ko ya samu labarinsa ya taimaka ya kira 07038751833 08068432929.

Allah yasa a dace, amen summa amen.

Address

NO. 22 MAMBILA Avenue, OFF SUNDAY AWONIYI STREET, NEW GRA
Bauchi
740271

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Albarka Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Albarka Radio:

Share

Category