Albarka Radio

Albarka Radio Albarka Radio 97.5 FM is a Nigerian English and Hausa Radio Station based in and broadcasting from Bauchi, Bauchi State, Nigeria.
(5)

Catch us Live on TuneIn, Radio Garden or visit live.albarkaradio.com to Listen to us Live Online. Albarka Radio 97.5 FM Bauchi is a Nigerian English and Hausa radio station based in Bauchi, Bauchi State. It was founded and owned by Arrowhead Global Communication services Limited. Renowned for its humorous approach to broadcasting, the station broadcast a mixture of news, features, sport, entertain

ments, talk shows, topical issues and interviews. and also promote businesses through advertisement. Mission
As an independent broadcast station, Albarka radio shall reflect and promote all sides of issues and opinions and build a tradition of trust and credibility with our audience. Vision
To be a reference point in quality radio broadcasting in Nigeria using the professional ethics of balance and fairness to motivate the listeners.

Gwamna Abba Gida Gida ya yi ta'aziyyar rasuwar mawaki Kosan WakaGwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana alhini ...
02/08/2026

Gwamna Abba Gida Gida ya yi ta'aziyyar rasuwar mawaki Kosan Waka

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana alhini kan rasuwar fitaccen mawaƙin siyasa, Muhammadu Buhari, wanda aka fi sani da Kosan Waka, wanda ya rasu a ranar Lahadi yana da shekaru 47 a duniya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi.

A cewar iyalan mamacin, Kosan Waka zai kasance a makwancinsa na ƙarshe a ƙauyen Tsanni da ke Ƙaramar Hukumar Batagarawa a Jihar Katsina da misalin ƙarfe 5:00 na yammacin ranar Lahadi.

Gwamna Yusuf ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga iyalan marigayin, musamman mahaifiyarsa, tare da abokansa, masoyansa da daukacin al'ummar Jihar Kano.

Ya bayyana marigayi Kosan Waka a matsayin ɗan asalin Jihar Katsina mai kishin ƙasa da ya yi fice a Kano, inda ya ce waƙoƙinsa sun wuce siyasa, tare da taka muhimmiyar rawa wajen inganta haɗin kai, al'adu da wayar da kan jama'a.

Gwamnan ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya yalwata masa kabari, Ya shigar da shi Aljannatul Firdaus, tare da bai wa iyalansa haƙurin jure wannan babban rashi.

Marigayi Kosan Waka na daga cikin fitattun mawakan siyasa na Kano, inda hazakarsa, ƙirƙirarsa da salon waƙarsa s**a ba shi karɓuwa a sassa daban-daban na Najeriya.

Sanarwar ta ce gudummawar da ya bayar wajen bunƙasa sadarwar siyasa da kuma nishaɗin Hausa za ta ci gaba da kasancewa abin tunawa.

Gwamna Yusuf ya ce gwamnatin Kano tare da masana'antar nishaɗi da miliyoyin masoyan marigayin a faɗin ƙasar nan sun yi jimamin wannan babban rashi, tare da addu'ar Allah Ya ba shi hutu na har abada.

Daily Nigerian Hausa.

02/08/2026

Daya daga cikin magoya bayan tsohon gwamnan jihar Bauchi, kuma dan takarar gwamnan jihar Bauchi a karkashin jam'iyyar APC, Muhammad Abdullahi Abubakar wato Adamu Inuwa Ibrahim wanda aka fi sani da AD, ya karyata jawabin da dan takarar gwamnan jihar Bauchi a karkashin jam'iyyar PRP Sanata Shehu Buba Umar cewa shi ne ya taimaki M A Abubakar a lokacin zaɓen shekarar 2015, har ya kai shi wajen tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya bashi kuɗin yakin neman zaɓe.

Kari akan haka, Adamu AD ya hakikance cewa tun kafin Shehu Buba ya san Atiku Abubakar, Muhammad Abdullahi Abubakar ya sanshi, sannan kuma tun kafin Muhammad Abdullahi Abubakar ya zama gwamnan jihar Bauchi yana da rufin asiri.

SponsoredKungiyar BWSO Ta Karrama Ƙungiyar Arc Usman Ya'u Darazo Volunteers Don Faɗaɗa Rajistar MambobiBala Wunti Suppor...
02/08/2026

Sponsored

Kungiyar BWSO Ta Karrama Ƙungiyar Arc Usman Ya'u Darazo Volunteers Don Faɗaɗa Rajistar Mambobi

Bala Wunti Support Organisation (BWSO) ta karrama ƙungiyar Arc Usman Ya'u Darazo Volunteers da lambar yabo bisa gagarumin gudunmawar da ta bayar wajen yi wa sama da mutum 2,000 rajista a matsayin mambobin BWSO a ƙaramar hukumar Darazo.

Shugaban BWSO, Malam Mukhtar Ahmed Jarmajo, wanda Babban Kodineto Chibiyar, Malam Sha'abdin Bello Zalanga ya wakilta, ya miƙa shaidar yabon tare da tabbatar da ci gaba da aiki kafaɗa da kafaɗa da ƙungiyar a ziyarar da ya kai ofishin ta da ke Darazo.

A matsayin wani ɓangare na ƙarfafa wannan haɗin gwiwa, BWSO za ta samar da hasken wutar lantarki mai amfani da hasken rana na solar da kuma intanet a ofishin Ƙungiyar Arc Usman Ya'u Darazo Volunteers domin inganta yanayin gudanar da ayyukansu.

Da yake jawabi, Shugaban Ƙungiyar Arc Usman Ya'u Darazo Volunteers, Anas Garba, ya jaddada aniyar ƙungiyarsu na ci gaba da wayar da kan jama'a da yi musu rajista a matsayin mambobin BWSO a birane da ƙauyukan Darazo, domin ƙarin al'umma su amfana da ayyukan chigaba da ayyukan jin ƙai da BWSO ke aiwatarwa a fadin Jihar Bauchi.

Kamal Ibrahim,
Public Relations Officer,
Bala Wunti Support Organisation (BWSO), 31/07/2026

Hotuna: Gwamnatin jihar Kwara ta kammala tituna masu tsawon kilo mita 234.99Gwamna AbdulRahman Ya Ce Gina Hanyoyi Na Haɗ...
02/08/2026

Hotuna: Gwamnatin jihar Kwara ta kammala tituna masu tsawon kilo mita 234.99

Gwamna AbdulRahman Ya Ce Gina Hanyoyi Na Haɗa Jama'a Da Damar Ci Gaba

Gwamnatin Jihar Kwara ta ce tana ci gaba da aiwatar da manyan ayyukan gine-ginen hanyoyi da nufin inganta sufuri, rage cunkoson ababen hawa da kuma buɗe ƙarin damar tattalin arziki ga al'ummomin jihar.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ƙarƙashin shirin Rahman Legacy Series, gwamnatin ta bayyana cewa manyan ayyuka irin su gadar sama ta General Tunde Idiagbon Flyover, da Dr. Ibrahim Sulu-Gambari (Unity) Flyover, tare da sake gina manyan hanyoyi a sassa daban-daban na jihar, sun taimaka wajen sauƙaƙa zirga-zirga da haɗa al'ummomi da damammakin ci gaba.

Sanarwar ta ƙara da cewa an kammala gina hanyoyi masu tsawon kilomita 357.19, yayin da ake ci gaba da aikin wasu hanyoyi masu tsawon kilomita 234.99. Haka kuma, an aiwatar da fiye da ayyukan hanyoyi 160 na interlocking a faɗin jihar.

A cewar gwamnatin, waɗannan ayyukan sun sa ababen more rayuwa s**a zama muhimmin ginshiƙi na bunƙasa tattalin arziki da ci gaban al'umma a Jihar Kwara.

Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa manufar gwamnatin ba wai gina hanyoyi don sauƙaƙa zirga-zirga kaɗai ba ce, illa dai haɗa jama'a da damammakin rayuwa da ci gaba.

Daily Nigerian Hausa.

Join us every Sunday from 5 30pm to 6pm
02/08/2026

Join us every Sunday from 5 30pm to 6pm

HOTUNA: Yadda rukunin farko na sojojin Najeriya s**a tafi ƙasar Guinea-Bissau domin shiga tawagar wanzar da zaman lafiya...
02/08/2026

HOTUNA: Yadda rukunin farko na sojojin Najeriya s**a tafi ƙasar Guinea-Bissau domin shiga tawagar wanzar da zaman lafiya ta ECOWAS a ƙasar.

📷: Aminiya.

Jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya karɓi tarin ƴan APC da s**a koma jamʼiyyar NDC a Jihar Kan...
02/08/2026

Jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya karɓi tarin ƴan APC da s**a koma jamʼiyyar NDC a Jihar Kano.

Wannan na cikin sanarwar da mai taimaka wa Kwankwaso kan harkokin yaɗa labarai, Hon. Saifullahi Hassan, ya fitar.

Sanarwar ta ce waɗanda s**a sauya sheƙar sun fito ne daga Ƙaramar Hukumar Madobi, inda aka karɓe su a gidan Kwankwaso da ke kan titin Miller a Kano.

Sanarwar ta ƙara da cewa tawagar ta bayyana goyon bayanta ga tafiyar NDC Kwankwasiyya tare da alƙawarin ci gaba da aiki domin cimma manufofinta.

Me za ku ce?

- Arewa Updates.

02/08/2026

LABARAN DUNIYA (02-08-2026).

Karanta Labarai: Muhammad Adamu

Edita: Auwal Ibrahim Gital.

02/08/2026

BIKIN YAYE ƊALIBAN SASHIN HADDAR ALKUR'ANI NA MUSAMMAN WATO SHU'UBATU DARUL QUR'AN WASSUNAHA ƘARƘASHIN MADARASATU HAFSAH LITTAHFIZ WAT TARBIYYATIL ISLAMIYYA WANDA DR. USMAN IBRAHIM USMAN GIADE YA ASSASA

Address

NO. 22 MAMBILA AVENUE, OFF SUNDAY AWONIYI STREET, NEW GRA
Bauchi
740271

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Albarka Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Albarka Radio:

Shortcuts

Share

Category