02/08/2026
Gwamna Abba Gida Gida ya yi ta'aziyyar rasuwar mawaki Kosan Waka
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana alhini kan rasuwar fitaccen mawaƙin siyasa, Muhammadu Buhari, wanda aka fi sani da Kosan Waka, wanda ya rasu a ranar Lahadi yana da shekaru 47 a duniya.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi.
A cewar iyalan mamacin, Kosan Waka zai kasance a makwancinsa na ƙarshe a ƙauyen Tsanni da ke Ƙaramar Hukumar Batagarawa a Jihar Katsina da misalin ƙarfe 5:00 na yammacin ranar Lahadi.
Gwamna Yusuf ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga iyalan marigayin, musamman mahaifiyarsa, tare da abokansa, masoyansa da daukacin al'ummar Jihar Kano.
Ya bayyana marigayi Kosan Waka a matsayin ɗan asalin Jihar Katsina mai kishin ƙasa da ya yi fice a Kano, inda ya ce waƙoƙinsa sun wuce siyasa, tare da taka muhimmiyar rawa wajen inganta haɗin kai, al'adu da wayar da kan jama'a.
Gwamnan ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya yalwata masa kabari, Ya shigar da shi Aljannatul Firdaus, tare da bai wa iyalansa haƙurin jure wannan babban rashi.
Marigayi Kosan Waka na daga cikin fitattun mawakan siyasa na Kano, inda hazakarsa, ƙirƙirarsa da salon waƙarsa s**a ba shi karɓuwa a sassa daban-daban na Najeriya.
Sanarwar ta ce gudummawar da ya bayar wajen bunƙasa sadarwar siyasa da kuma nishaɗin Hausa za ta ci gaba da kasancewa abin tunawa.
Gwamna Yusuf ya ce gwamnatin Kano tare da masana'antar nishaɗi da miliyoyin masoyan marigayin a faɗin ƙasar nan sun yi jimamin wannan babban rashi, tare da addu'ar Allah Ya ba shi hutu na har abada.
Daily Nigerian Hausa.