09/01/2026
Gwamnatin Jihar Bauchi ta sake buɗe shafin daukar ma’aikata domin bai wa waɗanda s**a riga s**a nemi aiki damar duba matsayinsu da kuma ci gaba da matakan da s**a rage.
Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar Bauchi, Barrister Mohammed Sani Umar, ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da manema labarai a Bauchi.
Barrister Mohammed Sani Umar ya ce sake buɗe shafin na nufin bai wa duk wanda ya riga ya yi rijista damar shiga ya duba ko ya cancanta ko a’a.
“Yanzu duk wanda ya riga ya yi rijista yana da account dinsa a shafin daukar aiki na Bauchi, zai iya shiga ya duba ko ya cancanta. Idan ya cNcN, yana da damar ya yi printing na slip dinsa, sannan ya tafi karamar hukumar da ya yi applying,” in ji shi.
Ya bayyana cewa wannan mataki ya biyo bayan umarnin Gwamnan Jihar Bauchi wanda ya jaddada cewa kowacce mazaba a fadin jihar dole ne a dauki ma’aikata daga cikinta, domin tabbatar da adalci da wakilci.
Barrister Mohammed Sani Umar ya kara da cewa bayan an tantance mutum a portal, mataki na gaba shi ne na karamar hukuma, inda jami’an da ke can za su tabbatar da mazabar mutum tare da tattara sunaye domin mika su ga gwamnati don amincewa.
“Su ne s**a san gundumar mutum, su ne za su iya bada shaidar cewa wannan mutum daga wannan gunduma yake. Bayan haka za su tattara jerin sunaye, mu amince da su, sannan mu tura su zuwa hukumomin da s**a dace kamar hukumar kula da ma'aikata wato Civil Service Commission da hukumar kula da malamai wato Teachers Service Commission,” in ji shi.
Ya ce daukar ma’aikatan na bin matakai ne bisa ga matakin albashi (grade level), inda ya ce:
“Wanda yake kasa da Level 06, ma’aikatu ne za su daukeshi. Amma daga Level 07 zuwa sama, hukumomin kula da ma'aikata wato Service Commissions ne za su shigo cikin aikin.”
Shugaban Ma’aikatan ya kuma bayyana cewa babu wani mutum da zai zo ofishi domin karɓar takardar aiki kai tsaye, domin komai ana yi ne ta hanyar shafin.
“Ko an dawo an samu aiki, babu wanda zai ce ka zo ofis ka karɓi takardarka. Za ka koma por