LBC Hausa

LBC Hausa LBC Hausa amintacciya kuma sahihiyar kafar samar da labarai da rahotanni da hirarraki masu ilimantarwa. A tuntubemu ta WhatsApp: +234 8025223987

Ghana na shirin fara sayar wa Nijeriya wutar lantarkiGhana ta bayyana shirin fara samar da wutar lantarki da za ta rika ...
27/08/2026

Ghana na shirin fara sayar wa Nijeriya wutar lantarki

Ghana ta bayyana shirin fara samar da wutar lantarki da za ta rika sayar wa Nijeriya, inda Nijeriya za ta samar da iskar gas, Ghana kuma ta yi amfani da iskar wajen samar da wutar lantarki.

Ministan mak**ashi na Ghana, John Abdulai Jinapor, ya ce tsarin zai kasance k**ar “musayar kayayyaki”, inda Ghana za ta mayar wa Nijeriya wani kaso na wutar da ta samar daga iskar gas ɗin.

Kafar DW Africa ta ruwaito cewa za a yi amfani da bututun iskar gas na Afirka ta Yamma wajen gudanar da shirin. Bututun ya samo asali ne daga Nijeriya, ya ratsa Benin da Togo kafin ya isa Ghana.

Nijeriya na da kusan tiriliyan 210.5 na cubic feet na iskar gas, yayin da Ghana ke samar da wutar lantarki ga ƙasashen Benin, Togo, Burkina Faso da Ivory Coast.

An kwantar da wata mai shayarwa, Zara Muhammad, a asibiti bayan da ake zargin kishiyar mahaifiyarta ta zuba mata ruwan z...
27/08/2026

An kwantar da wata mai shayarwa, Zara Muhammad, a asibiti bayan da ake zargin kishiyar mahaifiyarta ta zuba mata ruwan zafi a yankin Kofa da ke Maiduguri, jihar Borno.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne bayan wata gardama ta cacar baki ta barke tsakanin matan biyu.

Wata makwabciyarsu ta ce mazauna yankin sun ji kukan Zara, inda s**a garzaya gidan s**a same ta cikin yanayi na ƙuna a jikinta.

Mazauna yankin sun kuma yi zargin cewa Zara na fuskantar wahala da cin zarafi tun bayan da ta samu juna biyu, sak**akon watsi da ita da mahaifin jaririnta ya yi.

Zara Muhammad ta ce rikicin ya fara ne bayan da ƴarta ta yi ƙoƙarin shiga ɗakin kishiyar mahaifiyarta, lamarin da ya haifar da gardama wadda daga bisani ta kai ga kai mata hari da ruwan zafi.

Bayan shiga tsakani da Kwamishiniyar Harkokin Mata ta jihar Borno, Hajiya Zuweira Gambo, ta yi, tawagar agaji ta kai Zara asibiti domin samun kulawar lafiya.

An k**a kishiyar mahaifiyar Zara tare da tsare ta a hannun jami’an tsaro.

Hotuna daga ɗakin taro na BRC Radio Bauchi, inda ake gudanar da taron wata-wata na Quality Control, domin duba ayyukan t...
27/08/2026

Hotuna daga ɗakin taro na BRC Radio Bauchi, inda ake gudanar da taron wata-wata na Quality Control, domin duba ayyukan tashar tare da ƙara inganta inganci da ƙwarewar gudanar da shirye-shirye da labarai.

Shugaban BRC Radio Bauchi, Alhaji Umar Muhammad Shira, ya buƙaci ma’aikatan Sashen Labarai da Sashen Shirye-shirye da su ƙara zage damtse wajen gudanar da ayyukansu, tare da tabbatar da bin ƙa’idojin aiki da jadawalin shirye-shirye.

Alhaji Umar Muhammad Shira ya kuma bayyana cewa BRC 1 (AM) zai dawo aiki nan ba da jimawa ba, inda ya ce a halin yanzu ana kan aikin sanya kayan aikin na’urorin da ake buƙata. Ya roƙi ma’aikatan BRC da su bai wa injiniyoyi cikakken haɗin kai domin ganin an kammala aikin cikin nasara.

Babban bako a taron, kuma tsohon Shugaban BRC Radio Bauchi, Alhaji Hassan Adamu Shira, ya gargadi ma’aikatan da su riƙa zuwa shirye-shiryen da aka saka a cikin jadawalin aikinsu, tare da nuna muhimmancin ɗaukar nauyin da aka ɗora musu da muhimmanci.

Taron Wanda ya Sami halartar babban sakataren ma'aikatar yada labarai Alhaji Ibrahim Gambaki, ya yaba wa shugaban gidan BRC Radio Bauchi Alhaji Umar Muhammad Shira bisa nuna kwarewa da hazaka tare da Kira wa Ma'aikatan BRC da su sake maida hankali akan ayyukan su na yau da kullum.

BRC Radio Bauchi — Inganci, Kwarewa da Gaskiya wajen isar da saƙo ga alummar jihar Bauchi dama kasa baki daya.

Wani rahoto na SBM Intelligence ya bayyana cewa tsakanin Yuli 2025 da Yuni 2026, an sace mutane 7,825 a Najeriya cikin h...
27/08/2026

Wani rahoto na SBM Intelligence ya bayyana cewa tsakanin Yuli 2025 da Yuni 2026, an sace mutane 7,825 a Najeriya cikin hare-haren garkuwa da mutane guda 1,713.
Rahoton ya ce an samu hare-haren garkuwa 1,411, yayin da wasu 302 s**a shafi ayyukan jami’an tsaro da masu garkuwa da mutane.
A wannan lokaci, akalla mutane 1,142 sun rasa rayukansu, ciki har da fararen hula 895, masu garkuwa 179, da jami’an tsaro 68.
Zamfara ce kan gaba
Jihar Zamfara ce ta fi kowace jiha yawan hare-haren garkuwa da kuma mutanen da aka sace. An samu:
Hare-haren garkuwa 236
Mutanen da aka sace 1,921
Sai Katsina da hare-hare 187, amma adadin wadanda aka sace ya tsaya kan 559.
Sokoto ta biyo baya da hare-hare 179, inda aka sace mutane 1,157, yayin da Kaduna ta samu hare-hare 134, tare da mutane 814 da aka sace.
Arewa ta fi daukar nauyin matsalar
Rahoton ya nuna cewa Arewa ta dauki mafi girman kaso na wadanda aka sace, inda mutane 7,334, wato kusan 93.7%, aka sace a yankunan Arewa.
A Kudancin Najeriya kuwa, mutane 491, wato 6.3%, aka sace.
An nemi fansar ₦22.8bn
A cikin wannan shekara, masu garkuwa da mutanen sun bukaci a biya su kusan ₦22.856 biliyan a matsayin kudin fansa, amma daga ciki an biya kusan ₦7.779 biliyan.
Wannan ya nuna cewa an samu nasarar karbar kusan 34% na kudin fansar da aka nema.
Idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, adadin wadanda aka sace ya karu da kusan 66%, yayin da mace-macen s**a karu da 50%. Haka kuma, kudin fansar da aka biya ya ninka fiye da sau uku.
Rahoton ya gargadi cewa garkuwa da mutane domin neman kudin fansa na ci gaba da zama wata mummunar sana’a mai haddasa asarar rayuka ga kusan dukkan bangarorin da abin ya shafa.

TIRƘASHI: Dubban Mutane Sun Hadu A Spain Domin Bikin Tumatir Na La TomatinaDubban mutane daga sassa daban-daban na duniy...
27/08/2026

TIRƘASHI: Dubban Mutane Sun Hadu A Spain Domin Bikin Tumatir Na La Tomatina

Dubban mutane daga sassa daban-daban na duniya sun taru a garin Buñol na ƙasar Spain, domin gudanar da bikin shekara-shekara na La Tomatina, inda mahalarta s**a mayar da titunan garin tamkar koramar tumatir.

An kiyasta cewa kusan mutane 20,000 ne s**a halarci bikin, inda aka yi amfani da sama da tan 120 na tumatir cikin kusan awa guda.

Bikin dai wata al’ada ce da ta samo asali daga wani faɗan bazata tsakanin matasan garin a shekarar 1945.

Abuja — Yayin da muhawara kan makomar tallafin man fetur ke ci gaba da ɗaukar zafi a Najeriya, wasu ’yan ƙasa sun bayyan...
27/08/2026

Abuja — Yayin da muhawara kan makomar tallafin man fetur ke ci gaba da ɗaukar zafi a Najeriya, wasu ’yan ƙasa sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan ko ya k**ata a dawo da tallafin ko kuma a bar shi ya zama tarihi.
Wani mai sharhi kan lamarin ya yi tambaya kan dalilin da zai sa ɗan kasuwa ya kashe makudan kuɗi wajen gina matatar mai, wadda za ta ɗauki shekaru kafin ta fara dawo da jarinta, alhali akwai damar shigo da man fetur daga ƙasashen waje tare da samun tallafin gwamnati domin sayar da shi cikin rahusa.
Ya kuma yi zargin cewa ’yan siyasa da abokansu na iya kasancewa cikin waɗanda s**a amfana da tsarin tallafin, yana mai cewa Najeriya na buƙatar ƙarin matatun mai masu aiki yadda ya k**ata da inganci, maimakon komawa tsarin tallafin mai.

Sai dai Aransiola Abiodun ya yi kira da a bar batun tallafin mai a baya. A cewarsa, kuɗaɗen da aka samu sak**akon cire tallafin ya k**ata a mayar da su wajen gina ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, tsaro da noma, maimakon wasu tsirarun masu rike da muk**an siyasa su yi amfani da su domin amfanin kansu.

Shi ma Augustine Amos ya goyi bayan matakin Shugaba Bola Tinubu na cire tallafin, yana mai cewa matakin ya kasance mai tsauri amma ya buɗe hanyar gyaran tattalin arzikin ƙasar. Ya ce komawa kan tsarin tallafin zai zama babban koma-baya.
Muhawarar ta zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da muhawara kan sak**akon cire tallafin mai. Masu goyon bayan manufar na cewa ta rage nauyin da tallafin ke ɗora wa gwamnati tare da ƙarfafa zuba jari a harkar matatun mai na cikin gida. Masu adawa kuma na cewa tsadar rayuwa ta ƙaru sosai, yayin da har yanzu ba a ga sauye-sauyen da s**a dace a wasu muhimman ayyukan gwamnati ba.
A takaice, muhawarar ta ta'allaka ne kan tambaya guda: *Shin kuɗaɗen da aka samu daga cire tallafin mai sun isa ga talakawan Najeriya ta hanyar ayyukan ci gaba, ko kuwa har yanzu ana buƙatar sake duba tsarin?

27/08/2026

Ambaliyan Ruwa

27/08/2026

Ziyarar Ta’aziyya

Sanata Shehu Buba Umar Dantakarar Gwamna na Jam’iyyar PRP, ya kai ziyarar ta’aziyya gidan Alh. Bello Kirfi (Baba Waziri) da ke cikin garin Bauchi, domin jajanta masa bisa rasuwar matarsa.

Sanatan ya bayyana alhininsa tare da addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayiyar, Ya kuma ba iyalanta da sauran ‘yan uwa haƙurin jure wannan babban rashi.

27/08/2026

JARIDUN NIGERIA NA YAU Ahamis
Albarka Radio Globe FM Bauchi Eagle Radio Bauchi Labari Daga Bauchi

Shahararriyar ‘yar jarida kuma mai tasiri a kafafen sada zumunta, Hafsa Musa Abdullahi, wadda aka fi sani da Moofy, ta y...
27/08/2026

Shahararriyar ‘yar jarida kuma mai tasiri a kafafen sada zumunta, Hafsa Musa Abdullahi, wadda aka fi sani da Moofy, ta yi watsi da ra’ayin cewa akwai matan da namiji ba zai iya kai wa matsayin su ba. Ta ce abin da ya fi muhimmanci a gare ta shi ne tsafta da k**ala, ba dukiya ba.
A wani bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta, Moofy ta yi magana kan mazan da ke cika aika mata saƙon soyayya a DM, suna cewa: “Ina son ki, amma kin fi karfina.”
Ta tambayi ma’anar hakan, tana cewa: “Idan na fi ƙarfinka, me ya sa ka aiko min da saƙo? Babu macen da ta fi ƙarfin kowane namiji — babu ko ɗaya.”
Moofy ta ce ta yi imani da Allah, kuma ba ta yarda cewa mace ta fi namiji daraja ba. A cewarta, aure yana bukatar fahimtar juna.
Ta ce: “Idan kana son mace, ka je gare ta ka ce mata ina sonki kuma ina son in aure ki. Idan mun fahimci juna, sai mu yi aure. Shi ke nan.”
Sai dai ta gargadi duk wani namijin da zai nemi aurenta cewa ba za ta lamunci ya zo mata cikin rashin tsafta ba ko yana wari saboda rashin wanka.
Ta bayyana cewa duk lokacin da wani namiji ya tura mata saƙon neman aure, abin farko da take yi shi ne duba bayanansa da hotunansa domin ganin yadda yake sanya kaya da kuma tsaftarsa.
Ta ce: “Ku manta da ko kayan suna da tsada ko arha — shin mutum yana da tsafta? Akwai wasu maza da za ka kalli hotonsu guda ɗaya kawai ka ce, ‘Ah, wannan mutumin mai tsafta ne. Wannan fa namiji ne na gaske.’”
Moofy ta ce wani lokaci tana fara farin ciki idan ta ga wani ya turo mata saƙon neman aure, tana tunanin watakila ta samu mijin aure, amma daga baya sai ta ji takaici.
Ta ce: “Kamar, kai! Da gaske kake? Kana son ka aure ni amma kana kallon kanka a haka, kana cikin rashin k**ala?”
Mai tasirin ta ce ba ta damu da yawan kuɗin namiji ba, sai dai ta damu da yadda yake gabatar da kansa da kuma ko zai iya kula da ita.
Ta ce: “Ka tabbatar kana da kyau, ɗan’uwa! Ka tabbatar kana da kyau! Ba na damu da kuɗinka sosai ba. Amma ka tabbatar kana da tsafta. Shin za ka iya kula da Moofy?”
Ta kuma ce za ta iya auren talaka, amma gidan da zai kai ta ya k**ata ya kasance ya fi gidan mahaifinta kyau.
Ta ce: “Na fahimci idan kana sona amma ba ka da dukiya. Amma kana da gidan da za ka kai Moofy wanda ya fi gidan mahaifinta? Dole ne ka tabbatar gidan da za ka kai ni ya fi wanda nake zaune a gidan mahaifina yanzu kyau kuma yana da kayan more rayuwa. Ka tabbatar kana da kyau, kana da ƙamshi mai daɗi, kuma kana da kyakkyawan gida.”
Moofy ta ƙarfafa maza da su nemi matan da suke so cikin mutunci, har da mashahuran mata.
Ta ce: “Idan ka ga macen da kake so, ka shiga DM ɗinta cikin mutunci. Idan ta zage ka, ka kare kanka. A cikin DM, babu wanda ya fi wani matsayi.”
Ta ƙara da cewa ita ba ta zagin mutane a DM, amma idan aka raina ta ko aka ci mutuncinta, za ta mayar da martani.
A cewarta, idan namiji ya bayyana mata soyayyarsa cikin gaskiya, za ta iya cewa cikin ladabi: “Yi haƙuri, ba kai ne irin mutumin da nake so ba; tuni ina da wanda nake ƙauna.” Ta ce wannan ya isa, ba tare da wata hayaniya ba.

Address

LushI Yelwa Behind General Hassan Usman Katsina Unity College Bauchi
Bauchi
740001

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when LBC Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share