Malikiya TV

Malikiya TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Malikiya TV, News & Media Website, NO 9 GOMBE Road OLD GRA BAUCHI, Bauchi.

Sanarwa gareku Al’ummar Najeriya!Wanda yaga zai iya, ya zo ya gwada bajintar shi
21/09/2025

Sanarwa gareku Al’ummar Najeriya!

Wanda yaga zai iya, ya zo ya gwada bajintar shi

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya taya Uwargidansa, Sanata Oluremi Tinubu, murnar zagayowar ranar haihuwarta ta sheka...
21/09/2025

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya taya Uwargidansa, Sanata Oluremi Tinubu, murnar zagayowar ranar haihuwarta ta shekaru 65 a yau, inda ya bayyana ta a matsayin ginshiƙi a rayuwarsa da kuma abin koyi ga al’ummar Najeriya.

A cikin sakon taya murnar da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Shugaban Ƙasar ya bayyana Oluremi a matsayin abokiyar rayuwa da yake matuƙar kauna, mai ƙarfin zuciya da kwanciyar hankali, wadda ta tsaya tsayin daka a gefensa tun daga ƙalubalen siyasa har zuwa nauyin shugabanci.

Acewarshi “Ba kawai matar rayuwata ba ce. Ita ce aminiyata ce, mai ba ni shawara, mai juriya da tausayi, mai tawali’u kuma fitilar da ke haskaka hanyata,

Shugaban Ƙasar ya kuma jaddada irin rawar da Uwargidan nashi ta taka wajen tallafawa jama’a ta hanyar ayyukan jinƙai da sadaukarwa, yana mai cewa duk wani shiru da ta yi wajen ɗaukar nauyi a gida ya kasance hidima ga ƙasa baki ɗaya.

“Najeriya na bin ki bashi fiye da yadda mutane za su taɓa sani. A cikin duk wata sadaukarwa da kika yi a ɓoye, da duk wata wahala da kika ɗauka ba tare da kuka ba, kin bauta wa ƙasarmu daga gida k**ar yadda na yi daga kan mimbari.

Tinubu ya kuma yi addu’ar Allah ya ƙara wa matarsa lafiya, farin ciki da cikar buri, yana mai bayyana ta a matsayin uwa mai kwarjini ga al’ummar Najeriya da kuma madogara ga rayuwarsa ta sirri.

Jami’ar European American University ta karyata wani bikin murnar kammala karatu da aka ce an gudanar da shi a NICON Lux...
21/09/2025

Jami’ar European American University ta karyata wani bikin murnar kammala karatu da aka ce an gudanar da shi a NICON Luxury Hotel, Abuja, inda aka yi ikirarin ba wa wasu fitattun mutane shaidar girmamawa na PhD ciki har da mawaki Dauda Kahutu Rarara.

A wata sanarwa da shugaban jami’ar, John Kersey, ya fitar, ya bayyana cewa ba su amince da wannan taro ba, kuma an shirya shi ne ta hanyar yaudara, ba tare da sanin jami’ar ko yardarta ba.

“Mutanen da s**a shirya wannan biki sun yi amfani da sunan jami’ar ne wajen yaudarar jama’a da kuma karɓar kuɗi ba tare da wata hurumi daga gare mu ba,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa jami’ar ba ta taba ba da shaidar PhD ko girmamawa ga Dauda Kahutu Rarara, Alhaji Ahmed Saleh jnr., Mustapha Abdullahi Bujawa da Tarela Boroh ba. Haka zalika, duk masu digiri daga jami’ar suna cikin jerin Register of Graduates a shafin intanet na jami’ar, kuma waɗannan ba su cikin sahihan daliban da aka girmama.

Haka kuma, jami’ar ta bayyana cewa Musari Audu Isyaku, wanda aka ce shi ne wakilin Arewa maso Yamma, ba shi da wani izini daga gare ta. Hakazalika, Idris Aliyu, wanda aka ce ya wakilci shugaban jami’ar a wajen bikin, ba shi da wani matsayi a hukumar jami’ar, kuma ba shi da ikon wakiltar shugabanta. An tabbatar cewa a shekarar 2024 aka ba shi mukamin Fellowship da matsayin farfesa a fannin Financial Management, amma yanzu haka an soke mukamin saboda hannunsa cikin wannan zamba.

Jami’ar ta kuma tunatar da cewa a watan Afrilu na wannan shekara ta fitar da sanarwa game da tsohuwar shugabar jami’ar, Dr. Mrs. Josephine Egbuta, wadda aka kora daga mukaminta saboda laifuka, tana mai cewa yanzu haka ba ta da ikon wakiltar jami’ar. Shugaban jami’ar na yanzu shi ne Professor Luca Scotto di Tella de’ Douglas di Castel di Ripa.

Sanarwar ta ƙara da cewa jami’ar ba ta da alaka da Dominica ko Panama k**ar yadda aka wallafa, inda ta jaddada cewa yanzu haka tana aiki ne a matsayin gidauniyar ilimi mai zaman kanta a Faransa, tare da riƙe Royal Charter daga Bunyoro-Kitara Kingdom a Uganda.

Jami’ar ta ce za ta shigar da ƙara a gaban hukumomin Najeriya domin dakile irin wannan yaudara ta buga takardun jami’a na ƙarya, tare da tabbatar da cewa wadanda ke da hannu za su fuskanci hukunci na doka.

NOA Ta Bukaci NIPR Ta Jagoranci Gangamin wayar dakai Kan Muhimmancin Shidar Tantance Ɗan ƘasaDaga Aminu Gambo AdamuDarak...
20/09/2025

NOA Ta Bukaci NIPR Ta Jagoranci Gangamin wayar dakai Kan Muhimmancin Shidar Tantance Ɗan Ƙasa

Daga Aminu Gambo Adamu

Daraktan Janar na Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA), Malam Lanre Isa Onilu, ya bukaci Ƙungiyar Masana Hulɗa da Jama’a ta Najeriya (NIPR) da ta jagoranci babban taron wayar dakai na ƙarfafa muhimmancin samun takardar shaidar dan ƙasa da kuma inganta ƙimar al’umma a Najeriya.

Malam Onilu ya yi wannan kira ne a yayin taron wata-wata na reshen Ƙungiyar NIPR na Babban Birnin Tarayya Abuja, da aka gudanar a birnin.

Ya ce masana hulɗa da jama’a na da muhimmiyar rawa wajen gina ƙasa, domin sauya ta daga kasancewar ƙasa kawai ta taswira zuwa zama al’umma ɗaya mai haɗin kai, bisa martaba da takardar shaidar ƙasa ta bai daya.

Daraktan Janar ya bayyana cewa NOA tare da haɗin gwiwar NIPR na aiki tukuru wajen fayyace da yaɗa asalin ɗan Najeriya, yana mai jaddada cewa ba za a iya tallata kowace alama yadda ya k**ata ba sai an fara bayyana muhimman siffofi da halayenta na asali.

Ya kuma bayyana cewa Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya kuduri aniyar kaddamar da aikin Nigerian Identity Project, wanda zai kasance bisa tushen National Values Charter. A cewarsa, wannan tsari zai jagoranci kamfen na ƙirƙirar asalin ’yan ƙasa ɗaya da zai wakilci ƙimomi da burukan dukkan ’yan Najeriya.

Malam Onilu ya ce masana hulɗa da jama’a za su taka muhimmiyar rawa wajen nasarar shirin, yana mai bayyana shi a matsayin babban aikin ƙasa.

A nasa jawabin, Shugaban NIPR na ƙasa, Dr. Ike Neliaku, ya bayyana shirye-shiryen ƙungiyar wajen haɗa hannu da NOA domin yaɗa sabbin ƙimomin al’umma. Ya ƙara da cewa, baya ga haɗin gwiwa da gwamnati, NIPR na aiwatar da shirye-shirye daga bangaren masu zaman kansu ta hanyar shirin Rebirth Nigeria.

WATA SABUWA: Wani Matashi Mai Suna Kabiru Ɗan Auta Dake Kofar Kibo Zariya ya Cinnawa Takardun Degree Dinsa Wuta, Sabo da...
20/09/2025

WATA SABUWA: Wani Matashi Mai Suna Kabiru Ɗan Auta Dake Kofar Kibo Zariya ya Cinnawa Takardun Degree Dinsa Wuta, Sabo da Acewar sa Yau Shekarar Sa 3 Da Gama Degree Bai Samu Aiki Ba, Amma Sai Ga Mawaki Rarara Wai Yagama Degree Harda Shaidar Girmamawa,Yace Gara Ya Kona Takardun Yakoma Kasuwanci don baiga amfanin su ba

DDL Hausa

Wani bincike da likitoci s**a gudanar ya gano cewa cin naman aladen da bai dahu sosai ba na iya tsuro da wasu fararen ts...
20/09/2025

Wani bincike da likitoci s**a gudanar ya gano cewa cin naman aladen da bai dahu sosai ba na iya tsuro da wasu fararen tsutsotsi a cikin ƙwaƙwalwar mutum.

Bincike wanda aka gudanar kan wani mutumi mai shekara 52 da ke fama da matsanancin ciwon kai na ɓangare ɗaya da ake kira da 'Migraine' ya gano cewa a tsutsotin da ke tare cikin ƙwaƙwalwarsa su ne s**a janyo masa matsanancin ciwon kan da yake fama da shi.

A cikin rahoton da likitocin s**a bayar, sun bayyana cewa ana kyautata zaton cewa cin naman aladen da bai dahu sosai ba da rashin wanke hannu a kodayaushe na iya kasancewa sanadin fitowar tsutsotsin k**ar yadda kafar BBC Hausa ta rawaito.

Aminiya

Al’ummar Jihar Bauchi ga Saƙo
20/09/2025

Al’ummar Jihar Bauchi ga Saƙo

20/09/2025

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!

Wata ta haifi jariri ta jefar dashi.

20/09/2025

TIRKASHI: Jirgin ƙasan Kaduna zuwa ya tsinke ya gudu ya bar Tarago cike da fasinja.

20/09/2025

Hukumar Lafiya Ta Jiha Da Majalisar Jiha Sun Kai Ziyara Ga Sarkin Dass, Tare Da Duba Ayyukan Kwangilan Cibiyoyin Kiwon Lafiya

Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Jihar Bauchi tare da hadin guiwar Kwamitocin Lafiya da Na Asusun Jama’a na Majalisar Dokokin Jihar Bauchi sun kai ziyarar ban girma ga Sarkin Dass a fadarsa, tareda ziyartar wasu cibiyoyin lafiya a ƙaramar hukumar domin sa ido kan yadda ake aiwatar da ayyukan kwangila da gwamnatin jihar ta bayar a fannin lafiya.

Manufar ziyarar ita ce tabbatar da ingantaccen aiwatar da ayyuka da kuma duba matsalolin da cibiyoyin lafiya ke fuskanta, domin kawo mafita ga al’umma.

Gwamnatin Bauchi Za Ta Inganta Tsaro a Fannin Yawon Buɗe Ido Kafin Babban Taron Bunkasa Tattalin ArzikiDaga Aminu Gambo....
20/09/2025

Gwamnatin Bauchi Za Ta Inganta Tsaro a Fannin Yawon Buɗe Ido Kafin Babban Taron Bunkasa Tattalin Arziki

Daga Aminu Gambo.

Gwamnatin Jihar Bauchi ta ce tana ɗaukar matakai na musamman domin inganta tsarin tsaro a fannin yawon buɗe ido kafin babban taron Tattalin Arzikin Jihar da ke tafe.

Shugaban Hukumar Bunƙasa Yawon Buɗe Ido ta Jihar Bauchi (BSTDC), Dakta Muhammad Nasiru Yusuf, shi ya bayyana hakan a lokacin da ya karɓan bakuncin mambobin ƙungiyar masu otel na Najeriya a ofishinsa.

Ya ce tsaro muhimmin ginshiƙi ne ga duk wani ci gaba, don haka akwai buƙatar tabbatar da tsaro mai inganci yayin taron da kuma bayan taron.

Dakta Nasiru Yusuf, wanda shi ne Babban Kwamishinan Adana Muhalli na BSTDC, ya tabbatar da cewa hukumar na aiki tukuru wajen kare rayuka da dukiyoyi baƙi da kuma dawo da martabar yawon buɗe ido a idon duniya.

Ya ƙara da cewa hukumar za ta tabbatar da daidaiton harkokin otel domin kiyaye mutuncin jihar.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Masu Otel ta Najeriya reshen Bauchi, Mista Tracy Folarin, ya ce taron da s**a gudanar da hukumar na nufin gano wuraren haɗin gwiwa da tallafi tare da fahimtar manyan fannonin yawon buɗe ido da baƙunci.

Mista Folarin ya ce ƙungiyar ta amince da bin ƙa’idojin ɗabi’un baƙunci, tare da roƙon gwamnatin jihar da ta haɗa su a cikin taron Tattalin Arziki mai zuwa domin bayar da gudummawa wajen bunƙasa yawon buɗe ido a jihar.

CIKIN HOTUNA: ƳAN ACHABA SUN YI ZANGA ZANGA A BAUCHI KAN K**A BABURADaruruwan masu aikin achaba sun mamaye ofishin Hukum...
20/09/2025

CIKIN HOTUNA: ƳAN ACHABA SUN YI ZANGA ZANGA A BAUCHI KAN K**A BABURA

Daruruwan masu aikin achaba sun mamaye ofishin Hukumar kula da zirga zirgar hanya (VIO) a Bauchi, inda s**a koka kan abin da s**a kira rashin adalci wajen k**a yan uwansu musu babura saboda rashin plate number, body number, da kuma lasisin tuki.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa bayan taruwar ƴan achaban a ofishin domin bayyana damuwarsu, sai rikici ya ɓarke, lamarin da ya sa jami’an ‘yan sanda s**a yi gaggawar shiga tsakani domin kwantar da tarzomar da ke neman ɓarkewa a gurin.

Daga bisani, ƴan achaban sun bazu cikin manyan titunan garin Bauchi suna gudanar da zanga zanga a unguwanni daban daban, domin jan hankalin hukumomi kan buƙatunsu na ganin an bi musu hakkin su.

Hotunan da muka samo sun nuna tarin ƴan achaba da s**a cika wurare daban-daban na cikin garin Bauchi, abin da ya jawo hankalin jama’a da kuma ƙara sa ma’aikatan tsaro yin shiri sosai don hana barkewar tashin hankali.

Address

NO 9 GOMBE Road OLD GRA BAUCHI
Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malikiya TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share