Malikiya TV

Malikiya TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Malikiya TV, News & Media Website, Bauchi.

29/07/2025

Ƙasurgumin ɓarawon da ake zargi da sace Naira miliyan 5, tare da wayar hannu da kwamfuta, Kabiru Bala, ya amsa laifin da ake tuhumarsa dashi yayin tambayoyin binciken da CSP Ahmed Mohammed Wakil ya mai

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta k**a Kabiru Bala, ɗan shekara 31 da haihuwa, bisa zargin satar kaya da fasa ƙauri a...
29/07/2025

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta k**a Kabiru Bala, ɗan shekara 31 da haihuwa, bisa zargin satar kaya da fasa ƙauri a sassa daban-daban na jihar.

A rahoton da Kakakin Rundunar yan sanda a Jihar Bauchi CSP Ahmed Mohammed Wakil ya fitar ya bayyana cewa, An k**a Kabiru ne bayan wani likita daga Gombe, Dr. Auwal Abdullahi, ya shigar da ƙara cewa an fasa masa mota tare da sace masa ₦5,000,000, laptop da wayar Tecno Spark 17.

Kabiru ya amsa laifin, inda ya bayyana cewa ya shafe kusan shekara bakwai yana aikata laifuka, ciki har da satar wayoyin lantarki a wurare da dama. Ya ce yana sayar da kilo ɗaya na waya akan ₦10,000, inda ya sayar da kilo shida a karshen sati da ya gabata.

Ya kuma tabbatar da cewa ya taba shiga gidan yari sau takwas, kuma yana da abokan laifi da har yanzu ake nemansu.

An gano kayan da aka sace daga hannunsa, yayin da Kwamishinan ‘Yan Sanda, CP Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin gurfanar da shi da zarar bincike ya kammala.

Hukumar EFCC Ta K**a Mutane 32 da Ake Zargi da Zamba ta Intanet a BauchiJami’an Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta ...
29/07/2025

Hukumar EFCC Ta K**a Mutane 32 da Ake Zargi da Zamba ta Intanet a Bauchi

Jami’an Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (EFCC) reshen shiyyar Gombe sun k**a wasu mutum 32 da ake zargi da aikata zamba ta intanet a Jihar Bauchi.

An k**a wadanda ake zargin ne a ranar Juma’ar da ta gabata yayin wasu ayyukan hadin gwiwa da aka gudanar a unguwannin Sabon Kaura da Gwalameji, cikin garin Bauchi.

EFCC ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook, inda ta ce an k**a su ne bisa sahihan bayanan sirri da s**a nuna alaka tsakaninsu da nau’o’in damfara ta yanar gizo.

Kayan da aka kwato daga hannunsu sun hada da wayoyin hannu 9 na Samsung, iPhone 15, waya 1 Infinix, wayoyi 3 na Redmi, iPad guda 2, kwamfutoci 8, mota Peugeot 406, babura 4 kirar Neonx Auto, janareta Maxi E50KWH, na’urorin wasan PS4 guda 2, PS5 guda 1 da kuma bindiga.

EFCC ta ce za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.

Rahotannin da gwamnatin Jihar Katsina sun bayyana cewa mutum 100 daga cikin jami’an tsaron al’umma da  Gwamnatin Katsina...
29/07/2025

Rahotannin da gwamnatin Jihar Katsina sun bayyana cewa mutum 100 daga cikin jami’an tsaron al’umma da Gwamnatin Katsina ta samar ne s**a mutu a yayin aikin karaɗe ’yan bindiga da s**a addabi al’ummomin jihar.

Wannan ƙari ne a kan sojoji da kuma aƙalla jami’an ’yan sanda 30 da s**a rasu a yayin aikin tabbatar da tsaron rayuwaka da dukiyoyin al’umma, a cewar ma’aikatar tsaron jihar.

Kwamishinan tsaron jihar, Nasir Mua’zu ya sanar da haka ne a martaninsa kan wasu rahotanni da ke yawo a kafofin sada zumunta, waɗanda ya ce ana amfani da su domin tayar da hankalin jama’a.

Mu’azu ya ce Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Raɗɗa yana yin iya bakin koƙarinsa wajen shawo kan matsalar ’yan ta’adda kuma ana samun nasara a kansu.

Kwamishinan ya ce lokacin da Gwamna Raɗɗa ya karbi shugabancin Jihar Katsina, ƙananan hukumomi aƙalla 24 ne ke fama da matsalar ’yan bindiga, amma kuma sak**akon haɗin kai da jami’an tsaro da kuma ƙirƙiro ƙungiyar ’yan sa-kai ta jihar, an yi nasarar murƙushe su a ƙananan hukumomi 11.

Mu’azu ya ce, matsalar ta kuma yi sauƙi a wasu ƙananan hukumomi tara, in banda Faskari da Ƙankara da Safana da kuma Matazu, da ke ci gaba da dama da hare-hare.

Ya bayyana cewa hakan ba ya nufin cewa gwamnati ta gaza, domin jami’an tsaro na iya bakin ƙoƙarinsu wajen tabbatar da tsaron lafiya da duniyoyin al’umma a wuraren.

A cewarsa, duk da hatsarin da gwamnan ya yi kwanakin baya, bai daina tattaunawa da shugabannin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a harkar tsaro ba da ke jihar, domin shawo kan matsalar.

Don haka ya buƙaci haɗin kai daga kowanne ɓangare, musamman ganin yadda jami’an tsaron ke sadaukar da rayukansu wajen kare lafiya.

Wasu barayin daji sun sake kai hari a dajin Madam da ke yankin Duguri, cikin Karamar Hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi, i...
29/07/2025

Wasu barayin daji sun sake kai hari a dajin Madam da ke yankin Duguri, cikin Karamar Hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi, inda s**a kashe akalla mutane biyar a ranar Asabar da ta gabata.

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin wata tattaunawa ta zaman lafiya da aka gudanar a Nahuta, cikin Karamar Hukumar Darazo, domin warware rikicin da ya barke tsakanin manoma da makiyaya, wanda ya janyo raunata mutane da dama.

Gwamnan ya nuna matuƙar damuwarsa kan harin, yana mai bayyana cewa masu farauta, waɗanda a da suke taimakawa wajen kare dazuka daga barayi, yanzu sun fara rikicewa da manoma a wasu sassan jihar.

Ya ce gwamnatinsa na ci gaba da aiki tare da hukumomin tsaro da kungiyoyin sa-kai wajen dawo da dabbobin da aka sace da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankunan karkara.

Gwamna Bala ya alakanta ƙarar rikice-rikice da yawaitar shigowar mutane daga jihohi makwabta zuwa Bauchi, da kuma yawan jama’a da ke ƙaruwa da gaggawa, wanda hakan ke ƙara matsin lamba kan ƙasa da albarkatu

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC) ta bayyana damuwarta kan yadda wasu ƴan ƙasar ke sayar da bayanansu, ciki har da...
29/07/2025

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC) ta bayyana damuwarta kan yadda wasu ƴan ƙasar ke sayar da bayanansu, ciki har da lambar shaidar ɗan kasa (NIN), domin samun kuɗi.

Wannan na zuwa ne bayan sanarwar da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta fitar cewa wasu mutasa na biyan mutane naira 1500 zuwa 2000 don karɓar bayanansu sannan su sayar da su ga wasu kamfanonin hada-hadar kuɗi a kan naira 5000.

A wata sanarwa da shugaban sashen hulɗa da jama’a na hukumar, Dr. Kayode Adegoke ya fitar, sanarwar ta ce ba za ta ɗauki alhakin duk wani bayani da mutum ya bayar da kansa ko ta wani ba, musamman idan hakan ya kasance domin samun kuɗi ko riba.

NIMC ta bayyana cewa wannan lamari yana da matuƙar haɗari ga tsaron ƙasa da kuma tsaron rayuwar masu NIN ɗin wanda dalilin hakan ne hukumart gargaɗi ƴan Najeriya da kada su dinga bayar da bayanansu ga kowanne mutum da ba ma'akacin hukumar ba.

Hukumar ta NIMC ta sha jan kunnen al’umma a baya cewa kada su rika bayyana lambar NIN dinsu ga kowanne mutum sai da ga ma'aikacin NIMC ko kuma waɗanda hukumar ta amince da su

- BBC

29/07/2025

Kafintan da ake zargi da satar talabijin a gidan yaje aiki ya bayyana yadda lamarin ya faru, a wata tattaunawar bincike da ya yi da Kakakin Rundunar ‘Yan Sanda na Jihar Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta k**a wani matashi mai sana'ar kafinta mai suna Auwal Mohammed, ɗan shekara 22, bisa...
29/07/2025

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta k**a wani matashi mai sana'ar kafinta mai suna Auwal Mohammed, ɗan shekara 22, bisa zargin satar talabijin guda huɗu kirar 43-inch, a Bauchi.

Kakakin rundunar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar.

Wakil Ya bayyana cewa Auwal ya aikata laifin ne yayin da yake aikin shi na kafinta a wani gida da ba a bayyana sunan mai gidan ba, inda ya gano talabijin ɗin a ɗaya daga cikin dakunan gidan.

Bisa ga cewar rundunar, Auwal ya ɓoye talabijin ɗin a wani wuri a cikin gidan na tsawon makonni biyu, kafin daga bisani ya kwashe su zuwa gidan wani maƙwabcinsa domin ɓoyewa, tare da karɓar Naira dubu 50 a matsayin jinginar kaya.

Binciken ‘yan sanda ya nuna cewa daga baya ya sayar da ɗaya daga cikin talabijin ɗin ga wani da ake zargin dillalin kayan sata ne, a farashin Naira dubu 40.

Rundunar ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike tare da kokarin k**a sauran da ake zargi da hannu a cikin lamarin, da kuma dawo da sauran kayan da aka sace. Za a gurfanar da Auwal Mohammed a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

28/07/2025

Rawar gargajiya

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi musu yankan rago, daga cikin mutum 56 da s**a yi garkuwa da su sak**akon...
28/07/2025

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi musu yankan rago, daga cikin mutum 56 da s**a yi garkuwa da su sak**akon gaza biyan kuɗin fansa da ƴanbindigar suke nema.

A Rahotannin da BBC Hausa ta wallafa a sahfimta ya bayyana cewa, Kimanin watanni huɗu ne dai ƴan fashin daji s**a far wa ƙauyane Banga da ke ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda a jihar ta Zamfara inda s**a yi garkuwa da mutum 56
Bayanan da s**a zo mana shi ne ƴanbindigar sun nemi kuɗin fansa na naira miliyan 50 kuma an ba su amma duk haka s**a zaɓi su kashe mutum 38. Su s**an san dalilin kashe su. Mutane ne da ba su da tunani da ba su da hankali.

Sun manta ƴanuwansu ne suke kashewa kuma za mu haɗu a gaban Allah.Shugaban ƙaramar hukumar ya kuma ƙara da cewa kawo yanzu mutum 16 da s**a dawo da su ranar Asabar na asibiti inda ake kula da lafiyarsu, inda gawar su kuma mutum 38 da aka kashe na wurin ƴanbindigar "k**ar yadda s**a saba ai ba sa bayar da ita."

Dangane kuma da abin da ya shafi jami'an tsaro a yankin, Manniru Haidara Ƙaura ya ce duk da a wasu wuraren yana jin labarin irin ƙoƙarin da jami'an tsaro ke yi amma a yankinsa labarin ya sha banban.

"Alal haƙiƙanin gaskiya jami'an tsaro ba sa ba mu irin tallafin da ya k**ata mu samu daga ɓagarensu ba ma samu....illa dai askarawa na jihar Zamfara su ne kawai suke taimakon mu."

Jami'an tsaron Najeriya dai musamman sojoji sun sha musanta zarge-zargen da ake yi musu na rashin ka ɗauki a wuraren hare-hare, inda suke cewa jama'a ne ba sa sanar da su da wuri sannan a mafi yawancin lokuta mutane ba su san irin koƙarin da suke yi ba.

28/07/2025

Bauchi State First lady Aisha Bala Muhammad Distributes Rice, Carton of Bottle water, Cash to over 500 women in Bauchi.

28/07/2025

Kaddamar da Shirin Bada Maganin Azithromycin Ga Yara 'Yan Wata 1 Zuwa 59 (SARMAAN II)

Kaddamar da shirin bada maganin Azithromycin ga yara ‘yan wata 1 zuwa 59 a Jihar Bauchi, a wani ƙoƙari na inganta lafiyar yara ƙanana a faɗin jihar. Wannan muhimmin mataki na daga cikin shirye-shiryen da gwamnatin jihar ke ɗauka don rage mace-macen yara da kuma kare su daga cututtuka masu barazana ga rayuwa.

Bikin kaddamarwar ya samu jagorancin Uwargidar Gwamnan Jihar Bauchi, Hajiya (Dr) Aisha Bala Mohammed, wacce kuma ita ce shugabar gidauniyar Al-Muhibba Foundation.

Shirin, wanda aka fi sani da SARMAAN II Project, na gudana ne a karkashin haɗin gwiwar Hukumar Lafiya a Matakin Farko ta Jihar Bauchi (BSPHCB) da mitosath, tare da tallafi daga Gates Foundation, Malaria Consortium, da SCIDaR (Solina Centre for International Development and Research). Hakanan, shirin yana samun goyon bayan Ma’aikatar Lafiya da Walwalar Jama’a ta Tarayya.

SARMAAN II na daga cikin muhimman shirye-shirye da aka kaddamar domin bayar da maganin Azithromycin kyauta ga yara, wanda hakan ke taimakawa wajen kare su daga cututtuka irin su na numfashi, gudawa, da sauran cututtuka masu barazana ga lafiyar yara.

Address

Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malikiya TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share