Malikiya TV

Malikiya TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Malikiya TV, News & Media Website, NO 9 GOMBE Road OLD GRA BAUCHI, Bauchi.

20/10/2025

Mu kula da lafiyar mu

BBC ta Ruwaito Cewa akwai jita-jita da dama da ke yawo tsakanin maza kan batun fitar maniyyi yayin barci, abin da wasu k...
19/10/2025

BBC ta Ruwaito Cewa akwai jita-jita da dama da ke yawo tsakanin maza kan batun fitar maniyyi yayin barci, abin da wasu ke ɗauka a matsayin alamar rashin haihuwa ko ƙarancin ƙwayar maniyyi.

Sai dai masana kimiyya da likitoci sun bayyana cewa wannan lamari na “fitar maniyyi yayin mafarki” ko nocturnal emission, al’ada ce ta halitta wadda ke nuna lafiyar jiki, ba rashin lafiya ba.

A cewar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), fitar maniyyi yayin barci abu ne da ke faruwa da yawancin maza, musamman tun daga lokacin da s**a balaga, saboda ƙaruwa da aiki na ƙwayoyin halittar namiji (s***m cells).

Wannan yanayi, wani ɓangare ne na tsarin jiki wajen fitar da maniyyi idan bai samu hanyar fitarwa ta hanyar jima’i ba.

Binciken da Jami’ar Shu Yin ta Hong Kong ta gudanar mai taken “Mafarkin Jima’i” ya nuna cewa kashi 80 cikin 100 na mutanen da s**a shiga binciken sun fuskanci fitar maniyyi yayin barci, inda aka gano cewa maza da yawa suna yin irin waɗannan mafarke mafarken akalla sau tara a shekara.

Masu binciken sun ce, ko da yake jima’i wani muhimmin ɓangare ne na rayuwar ɗan’adam, amma ba kasafai ake mafarki da shi ba.

Masanin ilimin jima’i, Dakta K**araj, ya bayyana cewa jikin namiji na samar da maniyyi a kai a kai. “Idan ba a fitar da shi ta hanyar jima’i ba, jiki na iya fitar dashi a lokacin barci wannan tsari ne na halitta, k**ar yadda mata ke haila.

Haka zalika, wani masanin lafiya, Dakta Bhupati Jan, ya ce fitar maniyyi a barci ba wata matsala ba ce. Inda ya kwatanta shi da tankar ruwa: “Idan ta cika, sai ruwa ya fara fita haka jikin mutum ke yi idan maniyyi ya taru sosai.”

A wani binciken da Kwalejin Kiwon Lafiya ta Tongji da ke ƙasar China ta gudanar, an kwatanta maniyyi daga maza masu fama da rashin haihuwa da na maza masu lafiya. An gano cewa kashi 72 cikin 100 na matsalolin rashin haihuwa na da alaƙa da “rashin ƙarfin maza” ba wai fitar maniyyi a barci ba.

Binciken ya kuma nuna cewa maniyyin da ake fitarwa yayin barci na iya kasancewa mai inganci har ma fiye da na wasu hanyoyi.

Masana sun bayyana cewa maza masu fama da matsalar ƙarfin maza ma suna iya yin mafarkin jima’i kuma suna fitar da lafiyayyen maniyyi yayin barci.

Har wa yau masana sun yi karin bayani cewa babu wata hujja ta kimiyya da ke nuna cewa fitar maniyyi yayin barci na janyo rashin haihuwa.

Jikin mutum, a cewar Dakta K**araj, “na ci gaba da samar da sabuwar maniyyi bayan kowace fitarwa.”

Me ke haifar da mafarkin jima’i?

A cewar Dakta Bhupati Jan, mafarkin jima’i na iya faruwa ne sak**akon tunanin sha’awa ko burin mutum, amma hakan ba yana nufin yana ɗauke da wata cuta ba.
“Babu wata shaida da ta nuna cewa yin mafarkin jima’i yana rage ƙarfin maza ko yawan maniyyi,” in ji shi.

A ƙarshe, Dakta K**araj ya jaddada cewa, “Kawowa ba tare da jima’i ba, alama ce ta lafiyar jiki, ba cuta ba.”

18/10/2025

Alhamdulillah!
An kammala taro cikin koshin lafiya

Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa Hukumar Tsaron Soji ta Najeriya ta k**a wani Birgediya Janar tare da...
18/10/2025

Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa Hukumar Tsaron Soji ta Najeriya ta k**a wani Birgediya Janar tare da wasu jami’an soja bisa zargin shirya juyin mulki domin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Wannan mataki na zuwa ne bayan samun bayanai kan wata makarkashiyar da ake zargin wasu manyan jami’an tsaro da hannu a ciki, wadda nufinta shi ne kifar da gwamnatin dimokuraɗiyyar da ke kan mulki a halin yanzu.

Jaridar Sahara ta ruwaito cewa jami’an da ake zargi suna tsare a hannun Hukumar Tsaron Soji, inda ake ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.

A cewar wata majiya daga cikin rundunar, an bayyana cewa babban binciken kwa-kwaf din zai ɗauki tsawon kwanaki goma, sannan a ƙara wasu kwanaki biyu domin share sauran ragowar matakan da s**a rage.

Har yanzu hukumomin tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan zargin ba, yayin da ake sa ran karin haske zai fito nan gaba kadan.

18/10/2025

Waɗannan sune dalilin tsayawar internet a Duniya 🤔

18/10/2025
18/10/2025

Ga cikakken hirar yadda lamarin ya faru,
Bayan ‘Yan sanda sun k**a matashin da ake zargin ya kashe ɗan achaba don ya samu kuɗin auren mace ta uku 😱💔

Rundunar ‘Yan Sandan Bauchi Ta K**a Wani Matashi Bisa Zargin Kashe Ɗan Achaɓa Domin Samun Kuɗin Auren Mace Ta UkuDubun w...
18/10/2025

Rundunar ‘Yan Sandan Bauchi Ta K**a Wani Matashi Bisa Zargin Kashe Ɗan Achaɓa Domin Samun Kuɗin Auren Mace Ta Uku

Dubun wani matashi mai suna Mamuda Zakari Yau, mai shekaru 30 da haihuwa, ta cika a hannun ‘yan sanda bisa zargin kashe wani ɗan Achaɓa, Basiru Mohammed, mai shekaru 25, tare da sace masa mashin domin samun kuɗin da zaiyi amfani da su wajen auren mace ta uku, a Jihar Bauchi.

Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, shi ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Juma’a, inda ya ce lamarin ya faru ne a ranar 16 ga Oktoba, 2025, a unguwar Dakta Sulaiman Adamu Quarters, da ke bayan tsohon filin jirgin sama dake Bauchi.

A cewar CSP Wakil, wanda ake zargin ya yi amfani da wuƙan yanka lemo wajen cakka wa marigayin Basiru Mohammed yayin da yake ƙoƙarin sace masa mashin ƙirar Bajaj Boxer.

Rahoton ya ce marigayin ya yi ta ihun neman taimako kafin ya fāɗi ƙasa sak**akon raunukan da ya samu, abin da ya sa jama’a s**a bi wanda ake zargin yayin da yake ƙoƙarin gudu.
Da ya ga ana binsa, Mamuda ya yar da mashin ɗin da ya sace sannan ya tsere daga wurin.

18/10/2025

Tarbar Maraba wa Sarkin Kano

18/10/2025
Kimanin Yara Sama da miliyan Uku ne Ake sa ran Za'ayiwa Rigakafin Cutar Kyanda da Bakon Dauro a BauchiHukumar Kula da La...
17/10/2025

Kimanin Yara Sama da miliyan Uku ne Ake sa ran Za'ayiwa Rigakafin Cutar Kyanda da Bakon Dauro a Bauchi

Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Jihar Bauchi, tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Lafiya da walwala ta jihar, sun kaddamar da gangamin rigakafin cututtukan masassarar kyanda da bakon dauro a faɗin jihar.

Taron kaddamarwar wanda uwar gidan Gwamnan Jihar Bauchi Hajiya Aisha Bala Abdulkadir Mohammed wanda Asma'u Auwal Jatau ta wakilceta ta bayyana cewa ana sa ran kimanin yara sama da miliyan uku ne za'ayi musu a dukkan ƙananan hukumomi ashirin dake jihar Bauchi.

Ta kuma bayyana cewa za a gudanar da babban rigakafin ne na tsawon kwanaki goma, tare da ƙari wasu kwanaki biyu domin tabbatar da cewa dukkan yara da ake sa ran sun samu rigakafin.

Shugaban Hukumar Dr. Rilwanu Mohammed ya jaddada cewa wannan rigakafin na daga cikin shirye shiryen gwamnati na tabbatar da cewa kowane yaro yasami kariya daga cututtukan masu hadari da ke yaduwa cikin sauƙi a tsakanin yara.

17/10/2025

Zaka iya ci idan aka yimaka tayi?

Address

NO 9 GOMBE Road OLD GRA BAUCHI
Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malikiya TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share