24/08/2026
Gwamnati Zata Cigaba da Aikin Hako Danyen Mai A Kolmani – RMFAC
Gwamnatin Najeriya ta sha alwashin komawa aikin haƙar man fetur a Kolmani dake Alkaleri a jihar Bauchi, wanda aka yi watsi dashi a baya,
Shugaban hukumar rarraba arziƙin ƙasa Muhammad Bello ya bayyana haka lokaci da ya jagoranci tawagar, inda ya bayyana muhimmancin aiki ga jihar Bauchi da kuma yankin arewa maso gabas baki ɗaya.
Bello ya ce sun je domin ganewa idanunsu halin da ake ciki.