02/06/2026
DA DUMI-DUMI ll Kenya: An Gudanar da Ƙazamar Zanga-Zanga Kan Shirin Amurka na Gina Cibiyar Killace Masu Ebola.
A ƙasar Kenya, an gudanar da zãngã-zãngã a yankin Nanyuki da ke tsakiyar ƙasar, kan shirin Amurka na kafa cibiyar killace masu yiwuwar kamuwa da cutar Ebola.
Cibiyar da ake shirin kafawa a yankin Laikipia na cikin wani sansanin soji, inda za a rika kula da mutanen da ake zargin sun yi mu’amala da cutar.
Wannan mataki ya haifar da fargaba a tsakanin mazauna yankin, inda suke nuna damuwa cewa hakan na iya shafar lafiyar jama’a da kuma tsaro a yankin.
Masu zanga-zangar sun rika rera taken neman a dakatar da aikin gaba ɗaya, tare da kira ga hukumomi su yi cikakken bayani kan shirin.
A halin yanzu, rahotanni na cewa ana ci gaba da tattaunawa tsakanin hukumomin Kenya da Amurka kan yadda za a tafiyar da shirin cikin tsari da tsaro.
Hotuna: Al Jazeera English
Credit: Funtuwa Online Tv