Karamci TV

Karamci TV scattering news and information about social life activities and political issues.

Ga Saƙo A Kaiwa Gwamnan Neja, Ku Gaya Masa Cewa Ita Sunnah Kuturwar Uwa Ce, Don Haka Bai Isa Ya Hana Yaɗa Da'awar Sunnah...
19/07/2026

Ga Saƙo A Kaiwa Gwamnan Neja, Ku Gaya Masa Cewa Ita Sunnah Kuturwar Uwa Ce, Don Haka Bai Isa Ya Hana Yaɗa Da'awar Sunnah A Nijeriya Ba, Kuma Ya Sani Rigima Tsakanin Ƴan Ɗarika Da Sunnah Ba Zai Taɓa Ƙarewa Ba.

Me zakuce?

TOFAH 🤔Tuwo Ne Ba Na So, Shi Ya Sa Ba Na Son Auren Talaka, Inja Khadija Autar MawaƙaMe zakuce?
17/07/2026

TOFAH 🤔
Tuwo Ne Ba Na So, Shi Ya Sa Ba Na Son Auren Talaka, Inja Khadija Autar Mawaƙa

Me zakuce?

Wata Kaza Ta Tsinci Kanta A Komar Jami'an Bijilanti Bayan K**a Ta Da Laifin Tone Amfanin Gonar Wani Manomi A KanoWata ka...
16/07/2026

Wata Kaza Ta Tsinci Kanta A Komar Jami'an Bijilanti Bayan K**a Ta Da Laifin Tone Amfanin Gonar Wani Manomi A Kano

Wata kaza ta faɗa komar jami'an bijilanti a garin Ɗorawar Sallau dake ƙaramar hukumar Garun Mallam a jihar Kano bayan k**a ta da laifin shiga gonar wani manomi ta tone masa amfanin gona.

Kazar wadda darajar ta bai wuce naira dubu huɗu ba, ana zarginta da yin ɓarnar amfanin gona na dubban kuɗaɗe, inda bayan an hango tana yin ɓarnar aka yi tara-tara aka k**a ta.

Daga ƙarshe dai mamallakin kazar, Abdullahi Yalo Ɗan K**asho sun sulhunta da mai gonar, wato Sallau Mai Iri, inda kuma aka ja masa kunne da ya dinga saka ido a kan kazar tasa.

Al'ummar garin na Ɗorawar Sallau suna fama da dabbobin dake ɓarnatar musu da amfanin gona, inda ko a kwanakin baya ma an cika hannu da wani zoma bayan ya yi ɓarna a wata gona.

Me zakuce?

TIRKASHI-:Ina hidimar Sama da  Naira Miliyan 400 duk wata - Mawaki DavidoFitaccen mawakin Afrobeats, David Adeleke wanda...
15/07/2026

TIRKASHI-:
Ina hidimar Sama da Naira Miliyan 400 duk wata - Mawaki Davido

Fitaccen mawakin Afrobeats, David Adeleke wanda aka fi sani da Davido, ya bayyana cewa kula da rayuwarsa a matsayinsa na daya daga cikin manyan mawakan Afirka na bukatar makudan kudade, inda ya ce yana kashe tsakanin Naira miliyan 300 zuwa 400 a kowane wata.

Mawakin ya ce kudin da yake kashewa ba wai na jin dadinsa kadai ba ne, domin ya hada da kula da matsayinsa na shahararren mawaki. Ya kuma bayyana cewa wannan adadi bai kunshi kudin kula da matarsa, Chioma Adeleke, da sauran mutanen gidansa ba.

Karamci TV

Ya K**ata Shugabannin Jam'iyyar APC Da Gwamnoninta Su Kira Rara Su Ja Masa Kunne, Saboda Surutan Da Yake Yi Suna Ƙarawa ...
15/07/2026

Ya K**ata Shugabannin Jam'iyyar APC Da Gwamnoninta Su Kira Rara Su Ja Masa Kunne, Saboda Surutan Da Yake Yi Suna Ƙarawa Jam'iyyar Baƙin Jini A Wurin Jama'ar Ƙasa, Inji Jarumin Finafinan Hausa, Umar Ibrahim Rimi

Karamci TV

Kungiyar Matasan Nasara Sun Fice Daga APC Zuwa PRP, Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga Sanata Shehu Buba UmarKungiyar Matasan ...
14/07/2026

Kungiyar Matasan Nasara Sun Fice Daga APC Zuwa PRP, Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga Sanata Shehu Buba Umar

Kungiyar Matasan Nasara ta sanar da ficewarta daga jam'iyyar All Progressives Congress (APC) zuwa jam'iyyar Peoples Redemption Party (PRP), inda ta bayyana cewa ta yanke wannan shawara ne bayan tuntubar mambobinta da kuma nazarin halin siyasar jihar Bauchi.

A yayin wani taro da kungiyar ta gudanar, shugabanninta sun bayyana cewa daga wannan lokaci za su ci gaba da gudanar da harkokinsu na siyasa a karkashin jam'iyyar PRP.

Har ila yau, kungiyar ta bayyana cikakken goyon bayanta ga Sanata Shehu Buba Umar, tana mai bayyana shi a matsayin zabinta na neman kujerar Gwamnan Jihar Bauchi a babban zaben shekarar 2027.

Kungiyar ta yi kira ga magoya bayanta da sauran al'ummar jihar Bauchi da su hada kai domin tallafawa jam'iyyar PRP da kuma burin Sanata Shehu Buba Umar, tana mai cewa tana fatan samun sauyi mai inganci da ci gaba ga jihar.

Karamci TV

Cikekken Dan jihar Bauchi ne   kadai zai iya gane nan wajen 👇🏼
14/07/2026

Cikekken Dan jihar Bauchi ne kadai zai iya gane nan wajen 👇🏼

Yau tsohon Shugaban kasar Nigeria Muhammadu Buhari yake cika shekara guda da rasuwa .Ubangiji ya gafarta Masa 🤲🏼
13/07/2026

Yau tsohon Shugaban kasar Nigeria Muhammadu Buhari yake cika shekara guda da rasuwa .

Ubangiji ya gafarta Masa 🤲🏼

Wallahi bana so ake kirana da likitan zuciya, nima fama nake da tawa zuciyar ~ inji Sheikh Ahmad Tijjani GurumtumMe zaku...
09/07/2026

Wallahi bana so ake kirana da likitan zuciya, nima fama nake da tawa zuciyar ~ inji Sheikh Ahmad Tijjani Gurumtum

Me zakuce?

Address

Bakaro Street
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karamci TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category