Karamci TV

Karamci TV scattering news and information about social life activities and political issues.

Ruwan Zam Zam din Alhazan jihar Bauchi yan jirgi ns hudu ya iso Bauchi kafin ta shin zuwa kasar Saudiya domin sauke fara...
10/05/2026

Ruwan Zam Zam din Alhazan jihar Bauchi yan jirgi ns hudu ya iso Bauchi kafin ta shin zuwa kasar Saudiya domin sauke farali
-BRC BAUCHI

Innalillahi wa Inna ilaihi raji'unAn samu labarin rasuwar wata mahajjaciya ‘yar Niger mai suna Hadiza Oumar Sy yayin gud...
10/05/2026

Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un
An samu labarin rasuwar wata mahajjaciya ‘yar Niger mai suna Hadiza Oumar Sy yayin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026.

Rahotanni sun bayyana cewa marigayiyar ta isa ƙasar Saudi Arabia ne ranar 5 ga watan Mayu 2026, kuma tana kan hanyarta ta zuwa Medina lokacin da rashin lafiya ya same ta.

An garzaya da ita asibiti domin ba ta kulawa, amma daga bisani Allah Ya karɓi rayuwarta.

Za a gudanar da sallar jana’izarta a Al-Masjid an-Nabawi kafin a binne ta a makabartar Jannat al-Baqi.

TIRKASHI-:Hukumar Hisbah ta karamar hukumar Ikara a Jihar Kaduna karkashin jagorancin Kwamandanta Malam Lawal Shuaibu, t...
10/05/2026

TIRKASHI-:
Hukumar Hisbah ta karamar hukumar Ikara a Jihar Kaduna karkashin jagorancin Kwamandanta Malam Lawal Shuaibu, ta k**a wani boka da ake zargi da yaudarar mata yana karbe musu kudadensu.

Arewa Updates ta rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar jami’in hulda da jama’a na hukumar a Ikara, Abu Ammar ya fitar a ranar Juma’a 8 ga Mayu 2026.

Sanarwar ta ce, an samu kayayyakin tsafi a wajen bokan wadanda yake amfani da su wajen yaudarar mata da zummar biya musu bukatunsu.

Ya ce, bayan ziyarar gani da ido, hukumar ta kori bokan tare da shawartar al’umma da su rika kai rahoton duk wani abu mai k**a da haka ga hukumomi domin kare al’umma daga fadawa cikin irin wannan tarko.

Daga Arewa Updates wacce ta rubuta muku wannan labari da taimakon fasahar AI.

Hoton Rabiu Musa Kwankwaso na yau.
09/05/2026

Hoton Rabiu Musa Kwankwaso na yau.

Ni ba Muslimi bane, amma a ganina Annabi Muhammad shine mutumin da yafi kowa.-cewar Chicharito
09/05/2026

Ni ba Muslimi bane, amma a ganina Annabi Muhammad shine mutumin da yafi kowa.
-cewar Chicharito

DA DUMI DUMI:-Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta ayyana tsohuwar Ministar Harkokin Jinƙai, Sadiya Umar Faro...
09/05/2026

DA DUMI DUMI:-
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta ayyana tsohuwar Ministar Harkokin Jinƙai, Sadiya Umar Farouq, a matsayin wadda ake nema ruwa a jallo bisa zargin karkatar da kuɗaɗen gwamnati da kuma amfani da ofis ba daidai ba.

A cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta, EFCC ta roƙi duk wanda ke da bayanin inda take da ya tuntuɓi ofisoshin hukumar ta lambobin da aka bayar.

Hukumar ta bayyana cewa Sadiya Umar Farouq mai shekaru 52 ’yar asalin Jihar Zamfara ce, kuma adireshinta na ƙarshe da aka sani shi ne EN008, Okpo River, kusa da titin Agulu a Maitama, Abuja.

Sadiya Umar Farouq ta riƙe muƙamin minista daga shekarar 2019 zuwa 2023 a gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.

EFCC na binciken ma’aikatar da ta jagoranta kan zargin badakalar kuɗi har Naira biliyan 37.

A ranar 16 ga Afrilu, 2026, babbar kotun tarayya ta Apo da ke Abuja ta bayar da sammacin k**a ta, tare da Bashir Nura Alkali, babban sakatare na dindindin a ma’aikatar.

Alƙalin kotun, Jude Onwuegbuzie, ya bayar da umarnin ne bayan waɗanda ake tuhuma sun kasa bayyana a gaban kotu domin fara shari’arsu.

Sadiya Umar Farouq da Bashir Alkali tare da wani Sani Mohammed na fuskantar tuhume-tuhume guda 21 da s**a haɗa da cin amanar aiki da amfani da ofis ba bisa ƙa’ida ba.

EFCC ta ce waɗanda ake tuhumar sun karkatar da kimanin dala miliyan 1.3 da kuma Naira miliyan 746.6.

A cewar hukumar, wani ɓangare na kuɗaɗen da aka mayar wa ma’aikatar daga shirin tallafin jama’a ne aka karkatar domin amfanin kai.

TIRKASHI-:Aure wahalarsa tafi daɗinsa yawa. Daɗin ma da kake hange daga waje duk wahala ce .Cewar Yahya Shawai Me zakuce...
09/05/2026

TIRKASHI-:
Aure wahalarsa tafi daɗinsa yawa. Daɗin ma da kake hange daga waje duk wahala ce .

Cewar Yahya Shawai

Me zakuce?

DA DUMI-DUMI:Tsohon dan takarar Gwamnan Bauchi na APC a 2023, Air Marshal Sadiq Baba Abubakar ya fice daga jam'iyyar ADC...
09/05/2026

DA DUMI-DUMI:Tsohon dan takarar Gwamnan Bauchi na APC a 2023, Air Marshal Sadiq Baba Abubakar ya fice daga jam'iyyar ADC zuwa ADP

Tsohon dan takarar gwamnan Jihar Bauchi a zaben shekarar 2023 karkashin jam’iyyar APC, Air Marshal Sadiq Baba Abubakar mai ritaya, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), inda ya koma jam’iyyar Action Democratic Party (ADP).

Rahotanni sun bayyana cewa Air Marshal Sadiq Baba Abubakar ya dauki wannan mataki ne sak**akon rikicin cikin gida da jam’iyyar ADC ke fama da shi a matakai daban-daban.

Tsohon hafsan rundunar sojin saman na Najeriya ya bayyana cewa rikice-rikicen cikin gida da rashin daidaito a tafiyar jam’iyyar ne s**a sanya ya yanke shawarar barin ADC domin ci gaba da harkokinsa na siyasa a karkashin ADP.

Sauyin jam’iyyar nasa na zuwa ne a lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasar shekarar 2027, lamarin da ke kara jan hankali a siyasar Jihar Bauchi da kasa baki daya.

Naji Masoyana Suna Cewa Za Su Siyamin Form Ɗin Takara, To Ni Dai Karku Kaini Ku Baro, Ku Barni A Ɗan Film Ɗina, Domin Si...
09/05/2026

Naji Masoyana Suna Cewa Za Su Siyamin Form Ɗin Takara, To Ni Dai Karku Kaini Ku Baro, Ku Barni A Ɗan Film Ɗina, Domin Siyasa Sai Yan Siyasa - Cewar Adam A Zango

Me zakuce?

Tun Daga Lokacin Da Na Bada Sanarwar Bada Tukwicin Naira Milyan Ɗaya Gʻa Ŵànðà Ya Ÿi Bàŧàn̈çì Ga Àn̈n̈abì, Aka Kulle Min...
08/05/2026

Tun Daga Lokacin Da Na Bada Sanarwar Bada Tukwicin Naira Milyan Ɗaya Gʻa Ŵànðà Ya Ÿi Bàŧàn̈çì Ga Àn̈n̈abì, Aka Kulle Min Asusun Ajiyata Ta Banki Guda Biyu, Sannan Jami'an Tsaro Suna Bibiyar Gidajen Ƴan Uwana Don Su K**a Nì, Cewar Sheik Sani Isah Kano

Ina da kwarewar ciyo wa APC kujerar  Gwamnan jihar Bauchi idan na samu tikitin takara a karo na biyu - Tsohon Gwamna M. ...
08/05/2026

Ina da kwarewar ciyo wa APC kujerar Gwamnan jihar Bauchi idan na samu tikitin takara a karo na biyu - Tsohon Gwamna M. A Abubakar

Address

Bakaro Street
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karamci TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category